Allah zan baki hakkuri kan danki kada kice haka don samun haske a gare shi ko yaushe udan kince haka mama kamar kin yafe shi ke nan a cikin diyan ki baki daya.
Tace khadija idan bance hakan ba may zance shi kadai ne da namiji da Allah ya hore min yanzun baki ganin Suraj kanin sa ne na baya amma baya wuce magana da shawara da mahaifiyar shi.
Mama don Allah kiyi hakkuri insha Allahu shima zai dawo kamar yadda kike so har ma ya dara duk wani a gidan .
Murmushi naji tayi tana fadin kai kina son ki kare mijin ki ne a gurina khadija bayan kema a yanzun kina shirin zama uwa ga wasu kin kuma san sherin kishiya yadda yake.
Yaya ba zan saka damuwa a kan haka ba kin san ko ba ai magana a fili ba dole ne ayi shi a boye yau bakiji urin bacin ran da nake ciki ba dana samu wanan labarin.
Nace mama kiyi hakkuri bai kyauta ba kan gaskiya don ko bai kira kowa ba ya kamata ya kiraki tun farko ya sheda maki halin da ake ciki ku sani adduan ku ai shine jagora a gare mu.
Tace ke kika san wanan amma babagida sam narasa gane inda ya dosa da irin wanan rayuwar tashi baiko tunanen shima ya fara tara iyali a bangaren shi yanzu.
Ni dai hakkuri na bata don banda shi ba abinda zan iya cewa nasan kuma duk maganan ta gaskiya take fadi.
Don babu uwar da zata so ta haifi da yace bai shawaran komai da ita komay kuwa ya zama a duniya.
Laraba ke fadin hajiya ranta ya baci ne hakan akan maigidan ku kuma nace abin ne sai hakkuri mama don kyautawa bai kyauta ba gaskiya.
Ni ina ganin bai kyauta min ba ashe ga idan bai kyauta ba din da tushe Allah dai ya sa ya gane gaskiya ya daina hakan don mama tana da gaskiya wallahi .
Ai yanzu kin samu abu yayi sauki ke nan idan da sabo ai yakamata itama hajiyan ta saba ni nake ganin kamar dai haka rayuwan shi take ba mai son yawan magana ba ne shi .
Shiru nayi ina tunane kafin in mike tsaye tare da fadin Affan kuzo mu dan zaga kafin a kira sallah ko.
Muka fice daga part din muna fita falo buzayen nan suna zaune ga butar shayi sun dora a tsakiyar falon yana tafasa sai abin ya ban mamaki a raina har na kasa daurewa nayi masu magana.
Wanan wani irin dabi a ce haka kuke wa mutane wanan ai ya zama ganganci a gare ku koda baku san zafin kayan dake cikin falon nan ba ai kuma kun san zafin amfani dashi tunda kun fi kowa marar abinda ke cikin falon don kullun kune a cikin sa zaune.
Dije munyi wanin abinda bai dace bane kike fadar haka inji yanyala tana dagowa daga kwance nace yanzu don Allah haka ya dace ku saka wanan abin anan haka ?
Ko da masu gidan basa nan ai ku kuna nan ko kuma kuna amfani da kayan wuta a gurin tace yo ai in wanan ne ko masu gidan da suke nan muna amfani da abin mu.
Don haka dabiar mu yake buzu baya yayi sai da shayi kowa ya sani nace idan ma bakuyi sai da shayi sai kuyi a cikin kitchen don ban lamunci kuyi shi a nan ba din.
Idan kuma kunce ba haka ba yau sai a raba falon in san bangare na da naku yanzu a cikin wanan watan da muke mai albarka a wanan lokacin ne mace zata fito tana shan abu da rana kiri kiri haka.
Tace yo Dije sai dai idan wani zancen na daban kike nema a kan mu ko Alhajin dake da gidan ya gamu ya kyale mu a hakan.
Nace yau ni ba zan kyale ba don ban taba ganin kuna haka ba cikin yare naji samiha tana magana wanda na fahinci tsageranci take son yi.
Zuwa nayi with full confidence na dauke abin wutan a gaban su zuwa kitchen din gida wanda tsami da dauda ya cika shi na kai na aje na fito.
Na dawo falon na zauna ina jin suna zuba yare akaina wanda nasan zagi na sukeyi ban kula su ba sai sai samiha ce tace wanan dai jan magana kike son yi a gare mu.
Kin san kuma ba kyale ki zamuyi ba tunda kafin ki shigo gidan nan kin samay mu da yar uwan mu a nan ne don haka ganin bata nan zaki zo ki kafa muna naki ikon a kan mu.
Nace yar uwar taku gidan ta ne nan ko may yadda take a gidan nan haka nake auro ta akayi auroni akayi don haka ba fina tayi ba ga maigidan.
Duk abinda kuke bawai tsoron ku nake ji ba kyale ku nake yi don kawai a zauna lafiya idan kuma wata tace zata fada min maganan banza yanzu zaku gane kalana a gidan nan.
Wasa wasa maganan ke girma gare mu na ko haukace masu a gurin har yakai mama laraba fitowa a part din mu ta tsoma baki akan su bari don samiha ta dauko dahuwar tasu ta dawo dashi falon wai taga abinda zanyi.
Cikin ikon Allah muna haka sai ga Yusuf kamar wanda aka kira ya shigo gidan duba mu ya samu ana wanan fitinan .
Rai bace ya daka masu tsawa yace baku da hankali ne mace da ciki haka zaku tarar mata wanan samun wurin yayi yawa haka gare ku.
Ya zama dole yau a raba falon nan kowa cen ku ta rike bangare ta har maigidan ya dawo yasan yadda zaiyi daku a gidan nan ku ishi wanan yarinyar tana hakkuri da halin ku dana yar uwar ku amma duk baku ganin hakan.
Bai bar gidan ba sai da ya kira wasu da ban sani ba yace suzo gidan har wajen karfe hudu ana magana daya a gidan dole aka raba set din kujerun biyu aka bar hanya a tsakiya yace ba zai kore su ba yanzu don maigidan yai tafiya amma su kwana da shirin idan ya dawo dole ne asan abinyi kan su tunda ba don Allah ya kawo shi ba da bai san abinda zasu yi min ba.
Yai masu iyaka da mu da komai na fanni na yace idan yaji wani abu ya taso kuma zai dauki mataki sosai a kan su don sai ya sa an daure su.
Karshe dai sukace don yaga yar uwar su bata nan ne ya wullakan ta su yace idan da tana nan ma abinda zai masu daya fi wanan don da basu kwana a gidan bai mai zuwa shida sai gashi da yan sanda mutum biyu yace su zauna a get din gidan su kula da komai na gidan.
Wanan abin ya kara tayar da hankalin su sosai madam suka nema suka fada mata halin da ake ciki shawara ta basu akan sai sunyi hankali don Yusuf din nan kamar ya shanye maigidan ne.
Don haka suyi hakkuri su bimu yadda muke so har yar uwar su ta dawo gidan yanzu ba komai ya daga masu hankali ba sai yan sanda dake gadi a kofan gidan da bindigogin su shine tashin hankalin su.
Ya kuma kira maigidan yace yai wa nafisa ma gana idan yan uwan ta suka taba ni sai ya masu wulakanci sosai tare da mashi bayanin komai dake faruwa.
Ranshi ne ya baci ya samu nafisa di yai mata tas dama kuma gashi suna rikici a tsakanin su da zuwan ta ta tsiri yawo har lokacin zuwa ba yarinya nono yayi bata a masaukin su.
Kiran su tayi ta tambaya yadda akayi suka fada mata ashe dama ta basu go ahead idan nai masu wani gani gani su doke ni har sai cikin jikina ya zube idan kuma sunyi ban kulasu ba din su san yadda zasu tsoratani a gidan.
Sai gashi kafin suyi din ni na fara magana da har yakai akai min iyaka dasu komai zai faru da mutum idan ba mai kyau ba sai ubagiji ya kare shi ta wani hanya.
Sudai gurin su yanzu shine yadda zan rasa cikin da ya baiyyana a jikina yanzu shine babban bakin cikin duk wani na tare da Nafisa din.
Suna kallo na da yara muna shige da ficen mu a gidan babu yadda zasuyi shima yusuf bai faye zuwa ba don yace yana gudun sherin su.
Sai dai yazo ya tsaya a waje ya turo a kai mai abimcin buda baki ya tafi dashi idan ya gama da safe ya bayar da kayan a shigo min dashi ciki.
Tafiyan su da kwana uku na fita muka tafi yin sayaya kamar yadda ya umurce ni da motar shi muka fita tare da maryam harda ihisan da yanzu ta lake min da ba uwar ta a gida.
Sayaya mukayi sosai komai kamar yadda yace don Yusuf ne zai kai ma mutanen kaduna nasu idan zai tafi weekend.
Can kuna nafisa ne da ta dawo a fusace tana fada dashi don may zai bar min makulin motar shi inyi amfani dashi.
Yace ke da na saya maki mota kin fita ne ko may a wurina kada kiga ban sai mata mota ba har ki dauka wani abu ne ya hana bari nayi har ta gama karatun ta kada ya dauke mata hankali.
Kuma har yau ita bata san da manufana akan haka ba bata kuma taba nuna min bacin ranta kan rashin sai mata mota da banyi ba kamar yadda ke kika nuna min a baya.
Don haka itama matatace tana da iko da abina kamar yadda kike da iko dashi kuma ki fada ma yan uwan ki da suke bugo maki waya don gulma in ba suyi hankali ba abin akan su zai koma don nagaji wallahi ba akan ki bane faraun kishiya don ke ma wata ki ka shigo kika sama a gidan.
Kada ki dauki kamar wani daki ko wanda bai san abinda yakeyi ba nan dai sukai barsm baram da ita a dakin hotel din da suka sauka din.
Washe gari akai ma yarinyar aiki har lokavin kuma bai kirani ba sai dai da yayi tunanen ai banda layin shi koda yaso ya kamani da laifi tanan ne ya sa shi kiran layin nawa.
Muna zaune dukkan mu a falon da na dawo na samu samiha akwance tana barci tayi ale ale da ita na buga kujera ta tashi gani na ta da marairaice tace kanta ke ciwo tazo nan kada a damay ta a can.
Ban mata magana ba illar alama da nayi mata da ta bar gurin ta wuce muka zauna sai ga kiran shi ya shigo min.
Ba kuwar nomba dana gani na kasar waje ne yasa na gane shine a layin har kiran ya katse ban daga waya ba na share shi.
Ya kara kira kusan zai katse na daga da sallama wani iri yaji dajin muryan ya amsa yana fadin watau ke idan ba,a kiraki ba bazaki nemi mutane kiji saukan su ba ko ?
Nace cikin dakewa tunda naji shiru nasan tafiya yai dadi ne don ance shiru alaman lafiyace ya mai jikin da fatan an yi nasara ga tafiyan.
Yace jiki da sauki yanzu aka fito da ita gurin theater an dinke cikin dake bude din kan ne dai sukace bazasu taba ba yanzu saboda tayi kankanta da aikin shi sai idan Allah ya raya ta ta tasa nan gaba zasu taba ta.
Nace Allah ya bata lafiya yace amin ya wajen su mama da yaran nace duk lafiya muke sai yayi shiru.
Kawar da shirun nayi da fadin ka kira mama ka fada mata halin da ake ciki ko don su sani ?
Yace ban samu kiran ta ba har yanzu nace amma dai kasan baka kyata ba iyayye fa ba abin wasa bane mussanman uwa da Aljannan ka ke karkashin ta.
Yace may ya kawo wanan maganan Deedar nace gani nayi baka kyauta bane dai yace ai sun san na fada masu an haifa min ya mai lalura ko ?
Wa yazo dubata daga cikin su nace amma kuma kai kasan halin matar ka ai suzo kuma tace gulman ganin yar ya kawo su kamar yadda tai masu a baya.
Shiru yayi yace na fahinci dai kunyi waya da hajiyan mu ke nan ko nace ni ba muyi waya ba sanin halin ka dai nayi ba zakai tunanen ka kirata ka fada mata halin da ake ciki ba ka kuma san a karkashin wani take ga ta da abokan zama.
Naji zan kira yanzu idan mun gama waya sai na kara kira nace agaida su muna masu fatan alheri duk da nasan ba fada mata din zaiyi ba nadai fada ne kawai.
Yace zasuji ya kashe wayan nima na bi wayan da kallo na sauke ajiyan zuciya tare da gode ma Allah dana taushi zuciya nayi mai magana yadda zai fahinta.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Idan kin san darajan Allah kuma kina tsoron haduwa dashi kada ki karanta idan baki biya ba kyale mai cin amana taci ita kadai don ramin kowan daban ne kada ta halaka kan ta ta halaka ki yar uwa.
Ina falo zaune wayana yai kara na dauka hajiya mace a layin bayan mun gaisa ne take fadin kunyi waya ne da mijin ki don ya kirani yau.
Nace a, a mama ya kwana biyu bai kiramu ba nan tace haba khadija nasan kece zaki mai magana ya kirani ai.
Don yanzu ya kira yana min dadin baki na zage shi tas tunda shi har yanzu bai san ciwon kanshi ba.
Nace mama ayi hakkuri don Allah in Allah ya yarda zamu gyara haka ba zai sake faruwa ba tace idan ma ya ga haka shine daidai yaje yai tayi ai duniyace ita ta ishi kowa.
Nan dai na dinga bata hakkuri ta bar zancen tare da min kuma godiya a karshe tana fadin nagode khadija duk da kin boye bakece kika mai magana ba amma ni nasan ke din ce don wanan ba dabara shi bane.
Nace wallahi mama ban san cewa yana irin wanan dabi,ar ba da tuntuni na nuna mai kuskuren hakan da yake yi tace fushin shi na banza wa yake son yazo a wullakanta dama dai mommy ku ce mai wanan kokarin ita kuma Alhaji yayi mata iya ka da al,amarin Nafisa din tun wancan zuwa da sukayi don haka ne bata kula ba ma wanan karon.
Idan dai sun dawo zanyi kokari in zo da kaina in duba su in gani koni ma din zatai min rashin mutuncin nata data saba ne.
Nace wane ita mama dako ni ranan na isheta ai da takai karshen rashin mutunci gidan nan hakan dana fada ne yasa ta sake murmushi har ina iya jin ta mukai sallama na kashe wayan.
Sai shirin sallah muke ta faman yi da yanzu baifi sati daya ba idan Allah ya kai mu duk wani shiri da zanyi a bangare na nayi shi .
Yau muna zaune muka kira Anty Fati a waya bayan mun gaisa ne na ba yaran waya su gaisa da ita take tambayan su yaushe zasu dawo ne ?
Daddy yace da ita mama ni anan zan tsaya wurin anty tana kaimu yawo tana sai muna abin dadi ina ci kuma tana muna karatu a gida.
Daddy kaida kanka kace baka dawowa gurin maman ka yace eh mama ni anan zan zauna muna zuwa masallaci da Abban mu.
Dariya muka sawa yaron ta gama gaisawa da Affan ya miko min wayan nace ina nan kawo maki daddy ki mun maso muzo nan muyi maki sallah ne sai kuma ga zancen tafiyan mai gidan india.
Tace haka dai nake ji dana shiga wurin hajiya ashe kuma haka abin yazowa Nafisa wanan karon nace wlh anty ikon Allah yafi da nan ai.
Tace ta dai gani ga rabon ta dama idan mutum yace aikin sa yiwa mutane sheri ne da bin bokaye tafar ganin sherin ta na fita mata ai.
Tayi nisa Allah dai ya taro ta don ko wanan abin daya samay ta baisa jikin ta yai la,asar ba ta tuba ta daina wanin abin sai ma ai abinda ya karu gare ta ita.
Khadija ai ina ganin kokarin ki da kika iya zama a tsakiyan wanan nan mutanen don ta riga da ta gama da maigidan shiyasa kika gani gaba daya ma lamarin shi ya fice min a raina yanzu.
Nace hakkuri zakiyi ai don goben ki anty ki bar duba da tuna abinda sukai maki a baya ki dube gaban ki ki gyara goben ki.
Don ita dama gurin ta ke nan abar mata shi ita kadai ta yi yadda take so dashi tace bazan tsaya bata lokaci na akan su ba ni gaskiya nace anty nima na iya hakan balle ke don Allah dai ki gyara tsakanin ki da mijin ki da yan uwan shi tace nagode sai na kara kiran ku mukai sallama ta kashe wayan.
Laraba dake gefe tace wani abin ne baya mantuwa ga mutum ai amma in kana duban wanan sai kaima ka bata goben ka a banza.
Gwama da kike iya fada mata gaskiya ake lamarin