gode yayan mu ina mikewa.
Hajiya tayi murmshi tace kema dai yayan naki ke nan zama nidai na shige ina masu dariya a can muka zauna ina fada masu yadda mukayi zainab naji ta dungumay ni nace kamata yayi ki shigo mu zagaya dake ina ganin zaifi.
Ban dauki lokaci ba ya gama ganawa da mahaufiyar shi yace in fito mu tafi nayi masu sallama tare da zuwa dakin mommy na yima su anty Amina sallama suma muka tafi.
Duk wani shiri da zanyi nayisa a cikin daren nan mama laraba zata biyo motane zuwa abuja sai da safe na samu anty fati bayan nagama shirya nake cewa anty a gafarce mu idan munyi ba daidai mu zamu tafi ke nan tace yau ne tafiyan nace eh haka yace ai tace dukan ku kenan zaku tafi nace eh Affan najin haka ya mike da sauri yana fadin anty mu fa nace zan dawo in dauke ku ai yanzu zan tafi yin wani abu a can ne in dawo.
Karfe tara kamar yadda nace wa maryam muna cikin garin Abuja har na huta na gyara part dina ba kowa a gidan sai mu kadai.
Don shima muna isowa ya nufi office ya barmu ba kowa a gidan sai mu kadai abinci na girka da zanci don rashin karyawa da banyi ba can.
Ina zaune a falo sai ga Samira ta shigo tana tambaya na abinci nace ta jira ya dahu tana zaune sai ga uwar ta turo kofa tana fadin may samira tazo yi guri na yarinyar tace Ami yunwa nake ji ke kuma baki girka ba nazo gurin anty taban.
Idan ban girka ba ke ba zaki iyaba da zaki zo nan a tsafe min ke nace cikin wani murya mai kaushi ke ya ishe ki ya isa haka idan bakin ki ya kara kirana da matsafiya zaki gane kuren ki a gidan nan.
Da dasuke cin ban tsafe su sai yau ne zan tsafe maki su da sherin ki wanan kalman ya isa hakana daga bakin ki daga taimako zaki dinga aibanta ni haka ke wata irin mace ce da baki da lissafi.
Ke kina ganin budar idon ki a kaina zai razani ko may ko umurni kike ban karya na fada ke ba yar matsafa bane ko may duk tsafin da kuke dake da iyayyen ki a kune yake ai.
Nace kin dauka kowa irin kine jikan mayu masu yawo da maita suna sayarwa kuna yat ga ganye kuna kuma tallan kan ku.
Nafa san komai harda zuwa gidan dakike gun tsohon mijin ki da kika bari a gida sai shekara shekara zagayo shi.
Ni din ta fada a rude nace ke mun san komai fa da na dauka abin naki na wasa ne zaki gane ki dawo hanya amma yanzu nagane baki san ana maki ragowa ba.
Yunwa da kika saba zama cikin sa yasa ko girkin abinci bazaki iyawa yaran ki suci ba sai yawo bin boka da malamai saboda bakin yunwa har dangin kaf kika kwaso zuwa gidan mijin ki don baku gaji kunya ba.
Ina ma akasan shi balle a jishi uwa da uba duk a gidan suki zaune an fada maki ana bara ana karuwa kin dauka ban san yanyala uwar ki ce data haife ki tsohon dake bakin get kuma da kuke kira da Ruwa shine mahaifin ki.
Ban aune ba sai ganin ta nayi a gaba na wai zata doke ni ban san ina da wanan azaman ba a yadda nake jin jikina da nauyi sai ji kake kau kau kau na zuba mata maru biyu masu kyau ta yunkura Allah yaban sa, an ta nan na mata dukan banza a dakin.
Na turata waje ashe har yanzu samira na dakin muryan ta naji tana fadin idan kun gama ki bani abincin anty.
Kitchen na shiga nasamu abinci har ya tsane yana son kuna na zuba mata tafita a falo ta tsaya taci abinta inda uwar na daki tana fama da bugun waya wa miji da su madam.
Samad kazo gida yanzu daga magana matarka ta daga hannun ta mare ni yace what tace kazo tun kan ayi barna a gidan nan don ba yarda zanyi ba.
Ta kasheta kira madam tana fadin a turo mata yan uwanta yanzu gidan don babu lafiya wanan bakar banufan ta na son kashe ni.
A zabure madam da tasa yan uwanta a taso azo gidan sai dai sunzo bakin get masu gadi sun tare su waya madam ta buga mata tace gata fitowa.
Shafin hannu na kwance a kumcin ta magana tayiwa yan sandan kofar gidan suka ba shiga doka ne daga maigidan nan ta shiga dura masu ashar har bakin layin dayan yan sanda ya raka su da bindigan shi.
Abin sai ya taru ya zama mata biyu ga na cikin gida ga kuma namiji ya hana kowa nata shiga gidan .
Ciki ta koma a haukace tana tatara kayan ta wai ita ba zata zauna a kashe ta ba a gidan sai yasan yadda zai yi yau a gidan.
Nikan ina zaune bayan na dan cakula abinci don yunwar da nake ji ya bace min na daina jin shi kuma yanzu ina sauraren zuwan maigidan inji irin hukunci da zai dauka saboda irin haukan da take tana sababi.
Zuwan su laraba da Yanyala da kayan mu ne yasani fitowa waje tun lokacin sai dai na samu suna rikici a bakin get masu gadi sun hana yanyala shiga gidan.
Nace ma security din ya barta tashiga mama da harshe turanci muke magana dashi yace oga yace kada subar wani froriner ya shigo mai gida.
Ga Nafisa a tsaye sai surfa ma zagi take yi masu akan may zasu hana yanyala shiga gida zasu bar Laraba fa shigo.
Nace a cikin hausa ku bari wanan ta shiga don uwar matar oga ne ita ma daga kd take tafe sai yace ok ma tare da sarawa ya bude mata get din.
Tunda na fadi haka nacewa driver ha shiga muna da kayan mu cikin gida na barta a wurin tana masifa.
Saida ya fito ya shiga masu da kayan su ciki suma mun zauna da mama a falo muna fira abincin dana aje mata na dauko mata tana ci muna hira.
Sai four ya shigo gidan kai tsaye dakin shi ya nufa ya watsa ruwa dayake ranan muka dawo ban sawa raina wani yin girki ba duk danice zan karba.
Sai na kyaleta ita tayi don gudun jan wani fitina sai dai mun girka a part din mu don gudun ta taso a gaba.
Part din Nafisa ya fara shiga yanyala ce zaune a falon ta ya gaida ita da dawowa ya nufi cikin dakin inda ya samu yar tana kuka ga uwar a zaune bata kula mata ba.
Wurin yarinyar ya nufa ya dauke ta yana fadin sadiya ya akayine mai ke damun ta ne kin kyale ta tana kuka haka.
Idon ta da ya kade yai ja tace samad yau ina son ka raba muna gida da wanan yarinyar idan ba zaka dauki mataki ga abinda tai mun ba.
Haka kawai zatai min wanan aikin haka na kiraka kuma bakazo baka dauki wani mataki ba a kai sai yanzu ka ga daman shigowa gidan.
Kallon mamaki yake mata yace oh dama so kike da na dawo in shigo gida in rama maki dukan ko may ?
Ke may kike da har ta mare ki baki rama ba sai ni kike son inzo in tare maki fada komay yanzun haka ko ban tambaya ba nasan kece kika fara wanan fitinan.
Kamar kada taji haka daga bakin shi tace shike nan dama na sani ta wanke tabaka kashanye ta kaika gurin matsafan iyayyen ta an tsafe ka.
Ka sani yau ban zama a gidan nan da wanan gajar matar taka mai karfin doki ta illantani a banza tunda ita fadan mahaukata takeyi.
Yace kije duk inda zaki tafi kofa a bude take maki idan ke ba zaki tsaya ki rama ba sai ni ke son in zo in rama maki ko ?
Yana fadin haka ya aje yarinyar zai fita tace kazo ka dauki yar ka nagaji da wahala banza hakana yace ki barta ta mutu dama ba son ta kike yi ba ai.
Ya fita dakin sai samira ne ta shiga ta dauko yarinyar ta kawowa yanyala ita itako har kofa tabishi tana fitina bai juyo gare ta ba yaci gaba da tafiya .
Hiran daddy mukeyi muna dariya sai gashi ya shigo part dina daga unda nake zaune nayi mai sannu da zuwa ya amsa .
Labara na gaidashi yace laraba ku iso lafiya ta hanya tace da godiya Alhaji ya naku hanya da aiki kuma yace Alhamdullahi.
Daga haka bai kara magana ba ya fita nima kuma ban bi bayan shi ba don yadda na ganshi bai walwala yasa ban bishi ba don nasan yasan da batun fadan namu.
Sauraren shi nakeyi inji mai zace min akan zancen sai naga bai min magana ba ya fita har dare bai nemay ni ba nima ban je inda yake ba don ban kara jin duriyan shi ba ma.
Washe gari da safe da ya shigo har lokacin yana cikin tamke fuska gaisawa mukayi ya juya ya fita zuwa maryam yasa na manta da zancen a raina.
Har kwana uku banji yai min magana ba kuma babu wani sakin fuska a gare ni ga gidan ya koma muna tsit kamar ba gidan nashi ba.
Wani lokaci ashe mutum yana da rana ko shigowan da nake ina ganin su a falon ashe wani abune ga Laraba a yan kwanakin tana gyaran gidan sosai yai kyau da wani haske kamar dai ba gidan ba.
Zaman doya da manjan da yake damu ya ishi nafisa da kanta ta nemi shiri don taga haukan bazai fisheta ba dashi.
Na idar da sallah na fito falo na zauna wayana dake gefe yai kara na duba shine a layin na dauka da sallama ciki ciki yace ba tare da ya karba sallaman ba.
Bazaki kawo min abinci bane ko may nace dashi ban san ka shigo bane ya kashe wayan sai da na dan dauki lokaci namike na shiga kitchen na hada abincin shi na fita.
Bai gurin cin abincin bayan na jera ne na shiga dakin yana zaune nace na hada abincin gani tafe yace ba tare daya dago kan shi ba gare ni.
Komawa nayi saman kujeran dininng din ina jiran fitowan shi sai can ya fito har ya zauna bai yi magana ba na zuba na juya zan wuce yace ina zaki na dawo na zauna.
Abincin ya fara ci ba tare da ya kula dani a wurin ba sai da ya kusa karewa yace may ya hadaki da nafisa har yakai kuka hada jikin ku a wanan yanayin da kike ?
Shiru nayi ban bashi amsa ba ya dago yace ba tambayan ki nake nake yi bane nace ban san amsar da zan baka ba yanzu don ban san may ta fada ma ba kake fushi dani.
A hasale ya aje cibin yace ashe kin san ina fushi dake ke nan ko dana dauka kina da hankali ashe ban sani ba duk kanwar jace halin ku daya ga baki dayan ku.
Kina a wanan irin yanayin har zaki tsaya irin wanan fada kuna tijara wa junan ku nace dama nasan laifina zaka gani kan wanan maganan.
Fadan ku bai damay ni ba sai cikin dake jikin ki idan ke baki san zafin kan ki ba nina sani don idan har wani abu ya samay ki ni zaku daukowa magana.
Baki da hankali ne ko halin Nafisa ne ya zama maki bako kuma nace har part dina fa tabi ni zata dake ni bayan zagin da take min kuma.
Ta dake ki mana idan tayi hauka ne ta dake ki din idan rashin hankalin ta ya kai can tunda ita bata dake ki ba aike kin dake ta din.
Najirane inji kin ce wani gurin naki yana maki ciwo na shirya abin da zan maki kan haka sai Allah ya taimake ki banji kin min korafin komai ba.
Ranan dai naga bacin ranshi sosai a gare ni don yai min fadan da bai taba yi ba a gidan har sai da nayi kuka a wurin.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Laraba mace mai kwazo da sanin ya kamata ga kawar da kai ga abin mutum ga aiki a tsakani da Allah idan nace wani halinta wanda bai mun ba nayi karya illa da farko dana fara ja baya da ita.
Don yawan complain din Fati da takan mun don idan ta dauko zancen Fati shiru nakanyi in nuna mata banson zance.
Amma yanzu da muka dauki dan lokaci tare da ita saina fahinci wasu abubuwa a gamay da halinta, na farko dai tana korafinn akan zaman su da Fati.
Sai na biyu tana son ja na da maganan da ya shafi cikin family house din su AA sai daga baya na fahinci abida yasa take hakan.
Yau na fito da niyar zuwa gidan su maryam mu gaida anty hauwa dani da mama laraba zamu fita budan part din mu naci kararo da su Samiha sun dawo gidan.
Madam ta gargadoso don bazata iya ba sun isheta a gida shine mafarin ladabin shegun da Nafisa take ma AA akan yayi hakkuri idan anyi sunan yarta tayi arbain zata gida ta wuce dasu.
Ya amince mata da su dawo su zauna a gidan kafin lokacin data ce din dan hakan akace tsakanin mata da miji sai Allah don haka ta san kan abinta bata samu matsala wurin jawo hankalin shi ba.
A raina na hade mamakin ganin su zaune a falon har falon ya fara komawa yadda yake da da tarkace da shara komai akaci anan za a aje falon.
Ko kallon gefen su bamuyi ba muka fice daga gidan driver yana waje yana jiran mu ya kaimu unguwa.
Sai da motar ta fara tafiya laraba tace abin mamaki bai karewa a duniya mutanen nan dawowa sukayi kuma gidan nan again.
Murmushi na dan sake tare da fadin sun dawo mana mama tunda gasu nan har mazan su a gidan tace ikon Allah sai dai kuma ina ganin shigan dare sukai ma gidan don kafin mu kwanta ban gansu gidan nan ba danazo kwaso kayan da security sukaci abinci.
Dama haka suke kamar bakin sheri basu sauka gari da rana sai a cikin dare a wayi garin dasu ba mai cewa ya san saukan buzu a gari sai dai ka wayi gari ka gane shi.
Nace mama kin san su basu yarda da kan su ba balle wani don haka komai nasu a cikin munafunci sukeyin sa .
Munje gidan anty hauwa a can muka wuni gidan mun sha hira sai yamma lis muka dawo gida ba mu girka komai ba don mun ciko ciki a can gidan da muka fito.
Kamar gidan buki haka naga gidan ya koma min ga hasken kwayakwayan wuta ya haska falon sai hiran su ke tashi wasu kuma na waka har da tafin hannayen su.
Wani iri naji tankar a kaina suke wanan hayaniyar duk da naji kewan rashin su amma yanzu sai na tsunci kaina ina bakin ciki sake ganin su a gidan da nayi zamu zauna dasu kuma.
Bamu karasa shiga part din ba naji sun sake wani irin dariya har da guda irin shigen na matan larabawa.
Tirkashi nace raina ya baci sosai don nasan dani suke haka na daure ido rufe na bude part din muka shiga muryan laraba naji tana fadin oho wanan masifafun sin dawo ke nan kuma.
Ban iya bata amsa ba kai tsaye bed room na shiga na rage kayan dake jikina zuwa dogon riga na daura dankwalin shi a kaina na dawo falon na samu laraba.
Nace mama ko a dan dafa maki wani abu ne ki dora akai kada ki kwana da yunwa tace kai yan nan wanan koshi da nayi haka sai dai gobe idan Allah ya kai mu dai ko ?
Nace bari dai mu dora da dan ruwan tea a kai don kwanan nan mama sai dare yayi wani masifan yunwa yake damuna sosai.
Sai da tayi dariya tace yar nan banda abinki yunwa ai yana maki da sauki na gani mace mai ciki da ake so taci ta koshi amma ke har yanzu cakulan abinci naga kinayi.
Haba mama aiko yanzu ina ci da yawa fa a kwanakin nan har mamnakin kaina nake yi irin wana cin tace a hakan shine ci kada fa ki haifo min miji ko kishiya a ramay nace mama kishiyar dai don ku ji dadin kishi dakyau irin na gidan nan.
Laraba tace kedai bari yar nan ai har na sallamay sallah ina mamakin wana abin ke dai da gani kin san ba banza bane wanan abin haka.
Ace wai yadda aka rabu baram baram din nan wai Alhaji ya iya dawo da mutanen nan gidan nan haka kai da gani kasan ba abin kai sake bane wanan wanan.
Kai mama kai sake kuwa ya dawo da ita kin san bai iya