Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MIJIN Buzuwa Complete Complete Hausa Novel by Nil

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   101 / 144

300K to 303K   out of 431K words

mata yar yanzu.
Ya gama na sauke ajiyan zuciya dama yanayin sa ya nuna ba dadin rai ya dawo don yadda na ganshi a cikin rashin walwala a fuskan shi.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Bamu yi nisa ga barci ba tazo tana dukan kofa hankali tashe na farka naji muryan shi yana fadin kwanta abinki tayi abinda zatayi din.
Da safe ko da na sauko lokacin tara na safe ya gwauta a falo na samay ta zaune ta harde a cikin masifa da bala,i take ban muna arba ta soke kanta a kasa.
Na shige ban mata magana ba sai da naje nayi wanka na shirya na fito na nufi part din ta cikin rashin dadara nayi sallama na shiga.
Tana zaune ta jingina bayan ta a gado kafanta a harde tana waya kamar bata son aji maganan sai gani nayi sallama har kuryan dakin inda take.
Wayan ta kashe da sauri ta dago tana kallo na nace maman ihisan sannun ku da zuwa kun dawo lafiya ya mai jikin kuma ?
Tace lafiya kan muka dawo tunda kin ga miji har kin iya shigewa wurin shi kin san kuma bake ce dashi ba mai jiki kuma gata nan idan za a karasa ta ne da zai fi.
Murmushi nayi nace wanan kuma Allah ne kadai yakai can Allah ya bata lafiya yasa kafara ne gare ta .
Dama nazo in gaida ku da hanya ne in kuma dubs mamana Tani da jiki Allah ya sauwa ka na juya ina jin tana fadin muna funcin banza da wofi idan ma karasata kika zo yi ai gaki gata da yafi min wanan wahalan da kuka samu ciki.
Na kada kaina ina murmushi na wuce nace kodai ba komai na sauke nauyin da Allah yace ka sauke tsakanin ka da abokin zama.
Dakina na dawo na shige na kwanta barci nayi sosai ban falka ba sai wuraren karfe dayan rana na tashi don lokacin sallah da yayi.
Ban fito falo ba sai da nayi sallah na fito na samu mama laraba a falon yaran sun fita laraba ke fada min shigowan shi biyu part din nawa ya samu ina barci.
Zama nayi ina tambayan ta yaran tace yanzu baban su Yusuf yazo suka bishi tace kina barci ba an tayar da fitinan kujerun falo da aka raba ba gidan nan Yusuf yana zuwa yace a mayar dasu yadda suke a gyara .
Tace na fita in gyara wurin mu ne sai gata ta fito a cikin masifa kai wanan yarinyar bata da mutunci wai ni zatacewa maza in gyara kujerun a yadda suke a da can.
Tsoro da ya kamani yadda naga ta fito min dole na juya na shigo nan na barta tana ruwan bala,i a falon nasan tasa an warga zasu ne sai dazun da Yusuf ya shigo ne yake tambaya wanda ya hadesu tace itace tasa a yi hakan.
Yace yan uwanta su gyara a yadda suke anan gurin namu suka zauna yanzun haka badon sun tafi sallah ba tun dazu nan yake karban mutanen shi ai yau mutanen ki sun samu fita falo suna yadda suke so.
Nace ashe yau daddy ya samu sake, sai kinji ke nan dama abinda yake so ke nan a rayuwan shi dan ni har tausayi suke ban duk a takure suke dama.
Ai kina ma kokari tunda kina dan fita dasu acan in dai ba gurin kakan su ta turasu ba ko cen ko yaushe suna gida kumshe.
Shine ya shigo part din yake fadin kin tashi ke nan nace eh yace idan kin huta kije dakina kaya na nan saman gado ki dauko.
Tsaraban ki ne nace mun gode na bashi amsa yana fita na mike zuwa dakin a nan na suma kayan indian sari ne zube a saman gadon da kayan yara a cikin buhun nan na saka su na mayar na dawo na kira mama tazo ta dauka muka nufi part dina da kayan .
Nan dai muka baje ina duba daya bayan daya kayan suna da matukar kyau sosai da gani suna da tsada sosai sai set na dan kune da sarka masu kyau suma har guda uku.
Na gode sosai don kayan sun min kyau sosai gashi lokaci ya kure sosai duk da ina da kayan da suka fisu a dakin ke.
Zaman dai babu dadi sam don duk da mutanen da ke shigowa gaida su da dawowa bai hana Nafisa yin halin ta ba a bainan jamma,a duk dai a kan cikin dake jikina ne.
Shi da kan shi a wani safiya da ta tayar da fitina yace dani kada in kara kulata idan ta isa ta zuba da cikin a gani tace wai yana fada akan cikin da ba shine yayi min ba don tasan ba yadda za ayi ya iya min ciki din.
Yace saboda kin san sherin da kikayi yasa kike fadin haka to na dade da gane hakan sherin ki baiyi tasiri akan mu ba.
Fadan hauka ta fara yi dashi wai ita zaiwa kazafi yace kazafin may tunda yanzu ta fada kowa yaji bayan sun gama ta shiga daki sai gata ta kwaso kayan sallah dana sayawa yaran ta nufo dakina dashi yaran na biye da ita suna kuka.
Kukan yaran ne ya fito dashi yana tambayan su may ke faruwa nan samira ke fada mai abinda uwar ke niyar yi part din ya nufa ya samu an bude kofan ke nan tana shirin shiga ya dakatar da ita yana fadin.
Ba yaran nan kayan su idan ba so kike ranki yau ya baci a gidan nan ba tace akan kayan raina zai baci yace kwarai kuwa.
Ganin da gaske yake ga ihisan tana fisge kayan ta a hannun uwar ta rugumay su a jikin ta ta koma bayan uban ta tsaya.
Diya nane ko naka yace yar ki da nawa tace to kayi iko da yarka kabar min nawa yace haka kika ce tace eh na fada yace yau ko idan kin hana ta amfani da wanan kayan sai dai samira ta bar min gida.
Eh lalai Samad an wanke an baka kasha ka tsuma to bari kuji wallahi ko damay take tsafi sai na nuna mata tsafin ki karya ne kada kiga kin salwantar min da wanan da na haifa ki dauka na kyale ki ne kin ci bulus.
Yanzu ma kin saka miji ya yi min gori akan wanan kuma yadda kika saka yai min ki dauka kinci bashi ne a guri na idan na tashi nawa na fiki iya sheri.
Duk wanan hayaniyar muna jin su don kofan har lokacin a bude yake bamu rufe ba tace yau har kana ikirarin Samira ta barma gidan ka saboda na hanata saka rigan tsafi a jikin ta ko ?
Tsafi kece mai yi ai tunda har kika iya zuwa wurin boka a india don rashin imani irin naki kina dauka kowa haka yake kamarki komay to ke da bukan kunyi kadan ku juya ni yadda kuke so.
Kinji na fada maki kaya ne idan har samira kika hanata amfani da wanan kayan ni kuma ki tabbatar da tabar min gidana ta gama har abada.
Sai dai ta koma gidan ubanta can ta zauna ni hadin kai nake so a gidana ba watsewar kai ba yadda kika kasa wata tazo tanayi ya zamay maki kuma abin bakin ciki da sheri tunda ke baki iya hakan.
Nan ya fice ya barta tana jidali tare da ihuce ihuce can naji hayaniyar su da yan uwan ta ana ta koke koke ashe baiyi nisa sai gashi ya shigo gidan rai bace yace duk su fito daga su bar maigida.
Nan ya tsaya lalai ranan ba zata zauna mai a gidan shi ba daga ita har yan uwar nata duk yadda ta bada hakkuri yaki amincewa da hakan karshe ya fice tare da ba yan sandan bakin get baki akan su tabbatar da kafin biyar na yamma.
Ranan kan sun gamu da halin shi ashe Yusuf ne ya yi mai tas yace badon Allah ya kawo shi ranan ba da yaya zai samu anyi ni kadai sai laraba suka wuri su shida a kaina .
AA kan san kuna daukan alhakin wanan yarinyar duk da bata magana akan haka kyale ku fa tayi ta barka ga Allah idan kun cuce ta.
Kuma sai Allah ya kama ka da laifi akan hakan don kaine ka tauye ta ba wani ba nan dai ya kawo musalan irin tauye nin da zaman su ke yi a gidan.
Ashe shine turje matan da yayi dayazo ya samu tana fada dasu wai don sun karbi kayan sallah a hannu na shine dalilin fadan ta dasu tayi masu yankar kauna.
Dole ta kwashi angayan ta maza da mata suka wuce gidan madam madam tana gani su tace yo ni Nafisa ina zan kaiku duka haka.
Wanan dawainiyar ai sai mijin ki shi daya dauka abinda nake fada maki ke nan kin kasa ganewa gashi gobe jajibirin sallah.
Don may ba zaki hakkuri dakomai ke cikin ranki ba abinshi a sannu har hankali ya kwanta da sannu gani Allah ta samu ta karbi matan da ita ga yar tana ta tsala ihu tana neman nono.
Haushi ne ya kamata tace yar banza mai cin tsiya da shegen taurin rai ta mutu taki mutuwa tana lake dani.
Madam tace nafisa baki da hakkuri ne ga yar nan ko bukin suna ba ai mata ba kin debi rabon ki dako ta wanan yar idan kin kwantar da hankali ai sai ki cuta ma khadija.
Cikine fa a jikin ta take dauke dashi da kinyi dabara nuna mata bakomai a zuciyar ki ki tsiri tura yar wurin ta da itama haka zata haifo cikin ta tankar wanan yar na hannun ki.
Kin manta ace mace mai ciki wanda take arba dashi duk safiya kamar shi sak take haihu dakin daure kina iza mata yar ai da itama sai ta haifi sherin ta taji inda dadi.
Amma ina kin kasa hakkuri don zafin kishin da baki iya boyewa kin kaiga yadda ba a son akai yo ko ciyar daku yau kawai ai aiki ne gun mutum.
Wurin kwana kan zan iya baku sai dai ki nema muna abinda zamuci dagani harku a gidan nan yau gobe ki samu ki lalaba mijin ki ki koma dakin ki yafi sauki.
Tayi mamakin jin kalaman madam din sai dai ba yadda ta iya tunda duk yan uwanta da saka shigo ta gujesu yanzu tunda tana ganin ta fisu yanzu.
Don haka abin kunya ne ta nemay su akan su taimaka mata ta kwamace ta zauna hakanan wurin madam din in yasoda safe zata nemi mijin ta su shirya dashi.
A gidan kuma ban san har sun fice daga gidan ba sai da laraba ta fita har sau biyu bata ga ko dayan su ba ta dawo tana fada min.
Fita nayi na duba sai banji dadin hakan ba da yai masu ko don yar nan mara lafiya da take dauke da ita nasan ko yayane dole tana jin zafin kasancewar yar ga hakan.
Maryam na fara nema ina fada mata dariya ta kwashe dashi tana fadin dama a ce ina gidan da zasu tafi in dauke su in watsa shegiya a duniya.
Tace ke tsaya kin yi amfani da wanan abin sai nace nayi wasu banyi wasu ba sunan aje tace kai ke wai wata iri ce khady wanan matar fa ke taso aiwa haka rashe ya juye da mojiya sherin da ta dauko ya koma kanta.
Ke bari dai yau komai dare gani nan zuwa gidan wallahi gaba zan sakaki sai kinyi amfani dasu dariya nake mata nace maryam baki da tausayi wallahi.
Mata da danyen jegon ta zaki ce kinji dadin tafiyan ta ki kwanta haka da kan ki fa idan kece bazaki ji dadin hakan ba ai.
Tace amma ke ai da cikin taso kibar gidan ki koma gidan ku ki kayan goyo da ciki tana jin dadi don nasan wallahi idan itace ba zata tausaya maki ba ko kadan.
Nace wanan kuma ita ta sani nidai da zuciya daya nake zaune da ita a gidan nan tace ita kuma da zuciya biyu take zaune dake ba.
Karfe bakwai da wani abu ta iso gidan tun daga kofa take fadin wai Alhamdullahi Allah mun gode ma yau gidan nan kamar bashi ba wallahi.
Laraba ta dinga mata dariya tace don Allah mama ki tayani gani dajin wanan matar ko itama ba mamaki buzuwan nan ta shanye tane dai bamu sani ba wai fa mama tausayin wanan matar take harda kirana ta fada min maganan takaici.
Nidai ina zaune ina tasbihi ina kallonta ina murmushi na shafa nace ke dai baki da tausayi wallahi ni banga abun farin ciki ba a nan.
Laraba tace ni ai tun dazun ina zaune imani ya kashe ni wallahi wanan da ba a nan nake zaune sai in ce yar nan itama takai ta isa.
Amma sanin ko waye ita yasa na kara tsoron alamarin ubangiji yanzu duk balain da matar na ta dauko a kasan yan tsafin nan yau sai gashi abin ya juye da ita a gidan nan.
Shiyasa aka ce mutum wanda ya dogara da Allah baya taba kunya a duniyan nan don Allah yana tare dashi a ko wani lokaci.
Matan nan saboda bakin fitinan irin nata tun ranan da suka dawo take sama da jidali a gidan nan har rana mai kamar tayau bakin ta bai huta ba kan wanan boyar Allah.
Maryam tace ai yanzu ta kai ga yadda take so don da tsamani take mijin ba zai iya mata komai ba tana ganin ta gama dashi .
Bata san Allah ba ai mashi haka ba sai ya girgiza bawan sa ta inda bai zata ba Allah dai yasa ta tafi ke nan yar iska daga ita har angayan nata kowa ya huta.
Tara maryam tabar gida har lokacin kuma bsi dawo ba sai goma ya shigo part din mu ya nufo ya gaida mama da shan ruwa na fita na bishi da ga bayan don dama nakai mai komai na jera acan .
Koda na shiga na samu yana sallah sai dai baiyi wanka ba a lokacin na shiga na hada mai ruwa na fito ya rarage sallah yana zaune fanin na fito ya mike yana rage kayan jikin shi ya shiga ban dakin har ya fito ina zaune da waya na a hannu ina dubawa muna charting da binta.
Nan ya barni zaune ya nufi dinning na mike nasamay shi a girin abincin na fara zuba mai kafin in zauna yace kina ganin yau zan iya cinye wanan abincin haka mai yawa ?
Nace haka fa na saba zuba ma sai dai yau idan baka jin ci abincin ne kawai in rage ma yace barshi mu gani tunda kin zuba ko.
Idona koma gefe na zubs mai tare da harde hanaye na wuri daya na zuba mai ido yana ta cin abincin shi hankali a kwance.
Can ya dago kai yace min lafiya kikai shiru haka nace hakkuri nake baka bisa ga abinda ya faru yau a gidan nan don wallahi ban yi zaton zaku dawo bane yanzu kuyi sallah a gida yasa na hada dasu nasai masu kayan cikin kudin ds ka bar muna ai amfani dashi din..
Ai ba laifi bane don kin yi hakan yace ba tare da ya dago kan shi gare ni ba ya kalle ni nima shiru nayi na dan lokaci sai kuma na sake fadin.
Don Allah kayi hakkuri su dawo gida hakana ko don yaran ka dake wurin su din sai naga kamar hakan da kayi bai dace ba gaskiya.
Don , , , , hannu ya daga min tare da fadin ya isa haka don Allah koma may ye ya riga da ya faru ai ban son wanan maganan again.
Yaci gaba da cin abinvin sa sai can yace gobe kaduna zamu a can zamuyi sallah in Allah ya yarda.
Yana fadin haka ya dauki cup ruwa ya kora ya jawo tiesui yana goge bakin shi dashi ya mike binshi nayi da kallo har ya shige ciki.
Sai lokacin daya shige nake mamaki watau dai halin shine hakan na tafiya babu sanarwa sai yazo yaiwa mutum girshi Allah yasa ina da dan shiri na sai kuma goben zamu shiga in karo abinda nake so.
Mikewa nayi na shiga dakin na samay shi zaune yana waya gado na hau na lafe kamar yar mage ya dade yana wayan kafin ya gama.
Yace shirin sati daya zakiyi don ina son indan huta idan munje can na sati daya idan haka ya samu a gare ni.
Allah ya kaimu nace tare da fadin sai a shirya su Affan ke nan su koma gaba daya don hutun su ya kare one week after sallah zasu koma school.
Akwai wani abinda zaki kara sai masu ne ya tambaya yana hawowa gadon nace sai dai sayayyan school da nake son yimasu da dan abinda ba a rasa din ba dai.
Ok yace yana jan bargo tare da fadin kada muje can kuma kice zaki kawo min kabali da badi din da kika saba fada min idan munje don hutu nake son muje

101 / 144

Chapters