MIJIN BUZUWA complete Hausa Novels.txt

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   135 / 144

402K to 405K   out of 431K words

nuna ga yan uwa da abokanta wai ni sister din marigayitace kishiyar ta kuma yar uwar su.
Mun fito wurin waliman ne mun saurari nasiha da akayi inda aka fara hada hadan buki bayan waliman mai kidan kwarya suka dauko ta kida inda mata ke ta rawa da sauran su mudai muna gefe daya a zaune.
Sai abubuwan karamawa ake shigo muna dashi ina magana da Altine maryam ta ya futo ni tare da fadin kinga buzuwan ki gidan nan gaba daya muke kallon inda suke zaune.
Ita da wasu mata da gani masu ji da kansu ne a garin nan suka dasa hiran ta sai naji na tsawala a gurin don kasancewan Nafisa itama a gidan bukin.
Maryam ce ta fahinci hakan tace ita sai ta tambaya taji alakansu da ita nace haba dai akan may zaki tambaya.
Ashe zancen na a ran maryam sai ji nayi tana tambayan hajiyan ta juya tace wacan kike nufi tace eh wallahi ban san ta ba sai dai ina ganin gayan wata yar uwar maigidan nan ne sabuwa.
Maryam tace itace kishiyar khadija ai tace ita wanan din haba ashe a gidan ku na taba ganin ta ina ta tunanen a ina na santa tunda na ganta dazun tun shekaran jiya tana gidan nan yaude ne suka jima haka ai.
Bayan fitan hajiyan ne maryam tace yanzu ai munji dahir can mukaji ana sanarwa daga na hannun daman hajiya wai ana bukatar khadija matar AA perm sec ta fito fili nata ne.
Wani iri naji a gurin maryam tace da gaiya hajiya ta sa a fadi hakan don ki fito Nafisa ta ganki wuri yayi tsit ana sauraren fitowana a filin ga masu kwaraya sai kirari suke min.
Hajiya da kanta tazo taja hannun zuwa filin take na balle jakka ba dai wani rawa nakeyi ba na azo a gani amma sai wuri ta dauki ihu Allah ya taimake ni nazo da kudi a jakka na ina zubawa ana zuba min.
Koda na fito filin rawan ba Nafisa a inda suke daga ita har kawayen nata sun bar gurin mun dan dauki lokaci a gidan kafin ai muna iso gurin maigidan mu gaisa.
Yana ta zuba min godiya tare da fadin ki saki jiki kin zama yar gida kin bamu abinda ba kowa zai iya bamu ba a dalilin ki.
A raina nace badon ka nayi ba ai da zaka taimakawa yaya Adam ya daga zai fi min wanan godiyan da kake min a yanzu duk da yanzu AA na ma ya Adam din kokari sosai sun fita cikin gangin talauci ana danawa dasu sosai.
Biyar daida mu ka dawo gidan motar Nafisa da take amfani dashi muka gani a haraba don ta sayar da wancan na farko daya bata yanzu wani ya kara bata sai dai ko kusa bai kai nawa kudi da daukan idon jamma,a ba.
Muna shiga falon su Altine dauke da kaya niki niki itace zaune falon da mutanen ta kai ba dan kwali sai hayaniyan su ke tashi gidan.
Jin motsin mu shigowa ya dawo da hankalin su a gare mu har mun dan wuce ta tace yau ni naga inda ake cusa kai babu kwarjini a garin nan.
Nace ashe ke makin san gayyan na anya kika je babu gaiyata don kin gani da idon ki kai abin takaici wai mutun yaje bukin da babu gaiyata don rashin sanin ciwon kai.
Wallahi karya kike wai har ke za a kira da matar Samad a fili a cikin matan shi wa kike nace ai da aka kira keda kike wata tsiya a gurin shi sai ki fito tsakiyan filin.
Wata ce ke tare ta da fadin kaiya Nafisa wanan ai ba zancen fasawa bane don rai ya baci ai ita ma tasan ba zata hada kanta da ke ba.
Ke kuma wacece a cikin kayan miya na tambayi matar nace koda yake ba abin mamaki bane an gama cin kasuwa da madam yanzu kuma ku aka jaji bo muna.
Haka dai zaku kare wurin akaita sheri har da bukin da babu gaiyata kai girma dai ya fadi idan an sanshi maryam sai yau ta saka baki a zancen mu tace da an san dashi ne ai.
Tsiyan abin ba a san kunya ba da girma ai da ba, a zubar da mutumci ba ku dai kan kunyi hasara wallahi abin kunya masu buki suce basu san wanda ya gaiyato ku ba.
Ke har kina da bakin magana kullun kina yawo gidan kawa kuna fita yawon iskan cin ku da kuka saba wanan sai dai a fada maku ai.
Don mun san komai har gidan bokaye kuke zuwa suna amfani daku don kawai su biya maku bukata da bai yuyuwa.
Wanan maganan ya ci masu rai sosai take gida ya kaure da fitina security ya shigo yace su zo su fice a gidan Nafisa tace ba wanda ya isa ya kore mata mutanen ta.
Waya ya daga ya kira AA a fusace yace kada su bar mace ko daya a gidan nan kafin yazo nan suka tasa su a gaba sai da suka bar gidan cikin kunya sai faman zage zage sukeyi.
Wai an wulakanta su maryam bata dade ba ta tafi sai bayan sallah magariba ya shigo gidan rai bace falo ya kira mu ya tara mu yana tambaya.
Ta koro mai karya da gaskiya ta fada mai ya juyo gare ni jin tun da ta fara bayani banyi magana ba yace naji nata ke ya akayi fada min naki.
Nan na kora mai duk abinda ya faru ya juya wurin ta a hasale yace banta sanin ke sakarai bace haka sai yau.
Wai ma uban wa kika tambaya da zaki fita Nafisa na fada maki ba zan dauki wanan shashanci ba na yawon banza a gidana.
Nafisa wai ke wata irin mace ce da baki da tunane har kije gurin bukin da ba a gaiyace ki ba kina zubar da kimar ki ana maki gori akan shi.
Ke baki san komai ba a rayuwan ki sai shashanci da tambadewa kina bin tsofin zawarawa kuna zubar da mutuncin ku a gari.
Kana nufin goyan bayanta zakayi ne ko may yace kina rufe min baki ki barni da abinda nake jina raina ko sai ranki ya baci wurin nan.
Mace bata iya ba kanta tarbiya ba ta yaya zata ba yaranta ta tarbiya tace yanzu ne kasan banda tarbiya ko may ?
Na dade da sanin haka ya fada a hasale zatai magana ya daka mata wani uban tsawa wanda yasa har ni ma na kadu a wurin.
Mikewa tayi zata bar wurin yace dawo mara mutunci kawai wace bata san ciwon kanta ba bari kuji duk da ke kadai ce a cikin su ke da wanan halin duk ranan da irin haka ya sake faruwa da dayan ku sai na ba maishi mamaki a gidan nan.
Ku bace min da gani ya fadi daga karshe kowan mu ta mike zuwa part din ta yana gurin yana ta fada a cikin hasala har muka shige.
Nasan tasan bata da gaskiya ne ko may ta gani tayi shiru don bata zaci abin zai juye haka da ita ba idan da dane ba zaiyi wani fada na azo a gani ba.
Sai bayan sati biyu ne yake fada min wai yana ganin bukin Zainab ya tashi nayi mamakin jin haka don ni gida naso inyi hutun da muka samu sai ga zancen bukin zainab kuma ya taso.
Jin da sauran lokaci yasa na yi amfani da damana na shirya zuwa gida in duba su shiri sosai nayi inda na so su Altine ma suje gida da laraba su duba gida kafin buki sai dai ba zai yuyu ba haka muka fara shirin tafiya tunda nayi sa,a ya barni.
Sati mai kewayowa muka ziyarci gida da yarana sadiya kawai muka zo da ita bamu zo da Ihisan ba don suna makaranta har lokacin.
Munji dasin zuwa gida don muna da lokaci har sati daya ya bani inyi a gida haka ya bani daman ziyartan tan uwa da abokan arziki da aka dade ba a hadu ba.
Tafiyan mu da kwana biyu ne ya dawo gidan ta shigo tana fada mai wai ta dafa mai abinci yayi mamaki amma sai ya dauka don bani gari ne take son burge shi da hakan ita ma.
Tana zaune a gefe bayan ta zuba mai duk da abincin bai cika mai ido ba haka ya daure zai ci ya jawo plate din zuwa gaban shi bayan ya wanke hannun shi da ruwa.
Allah Allah take taga ya fara ci yana saka hannu kamar ance ya dubi zoben nan daya saka wanda na tsinto mashi a kasan gadon shi.
Wani sirirn hayaki yaga yana fita daga jikin zoben sai da gaban shi ya fadi sai ya dake ya kara kai hannu zai dibi abincin karo na biyu.
Abinda ya faru da farko ya kara faruwa dashi zoben yana fitar da hayaki yace wanan tsohon yayi gaskiya.
Plate din ya tura mata gabanta yace bisimillah ki fara ci don naga kamar baki ci ba ke ta kakaro murmushin yake tace nikan ai dam nake yanzu naka ne kawai ya rage.
Ido ya tsura mata tare da mikewa ya zagayo inda take ya duka ya dibi abincin tana zaune tana kallon shi.
Zuwa lokavin tayi mutuwan zaune ya dibi ya kai mata a bakin ta kai ta girgiza mashi take ya daure fuska yace ko kici ko in saba maki yanzu wurin nan.
Hakkuri ta fara bashi akan ba zata ci ba yace Nafisa kashe ni kike son yi ko may da kika zuba min mugun abu cikin abinci na ?
Ta fara kamay kamay ita bata zuba mashi komay ba watau ita bai yarda da ita ba ke nan ko ?
Nan suka fara rikici a tsakanin su yace kina tunanen yanzu zaki iya shamta nane ki yaudare ni kar nake kallon ku a gidan nan.
Duk wace ke sheri na sani kyale ki kawai nake yi nan dai ta hau borin kunya inda take shiga banan take fita ba yace kici idan kin san baki zuba wani mugun abu a ciki ba .
Karshe dai ya kore ta dakin yace kada ta kara zo mai daki idan bashi ya nemay ta ba tunda ke jahila ce baki dogara ga Allah ba.
Ranan dai kunya ma ya hanata ko wani dogon motsi a gidan wayan sabuwa ta nema tana fada mata abinda ya faru.
Tace ke yaya akayi ya gane amma wanan mijin naku na yarda da madam ke fadin wahalan banza muke akansu gaskiyane asiri baya kamasu tunda har ya gane wanan shirin namu.
Nandai na sha zagi a wurin su sun dade suna kulawa da warwarewa a tsakanin su shiko yana can rai bace ya rasa matakin da zai daukar mata ya huce.
Kasheni Nafisa take son yi ko may may na rage su dashi a gidab nan da take neman rayuwana tabbas Yusuf dasu hajiya sunyi gaskiya.
Yau ba don na kasance da khadija a rayuwana ba da Allah kadai yasan irin cuta min da Nafisa zataci gaba dayi ba tare dana sani ba gidan nan.
Barci rabi da rabi ya yi shi ranan tun safe ya fice gidan tare da taurara mataki akan Nafisa ba tare data sani ba.
Yusuf yana ganin shi ya fito da safe haka yake tambayan shi ko lafiya kasa fada mai yayi a lokacin don bai san may zaice mai ba.
Sai zuwa yamma ne da Yusuf yaga damuwa yayi mai yawa ya tasa shi a gaba take fada ma Yusuf din abinda ya faru.
Yusuf yace kaga zoben tsohon nan ke nan ya wani yamuste fuska yace Deedar ta tsinto min shi a kasan gadona nasan kuma hakan sherin Nafisa ne ba kowa ba.
Yanzu wani mataki ka daukan mata don ya kamata ka daukan mata mataki yanzu tunda bata da niyar bari.
Na riga na dauki mataki ko sai ta raina kanta a gidan nan don ba saki a tsarina wancen ma danayi bakaji irin fadan da Abba yai min ba ranan.
Don haka a cikin ruwan sanyi zangasa ta sai ta raina kanta gidan nan Allah yasa ta bari indai Nafisa ne ina ganin da shi idon ta ya bude dama yusuf yace.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/21/21, 7:42 AM - Fatima Amarya: Satin mu daya a gida muka dawo sai dai tunda na dawo naga sauyin gidan ya juya a yanzu gaba daya na rasa fahintar komai daga mutanen gidan.
Ban kara gaskata hakan ba sai da ta shigo wurina da safe yana fadin kulun ku dinga saka min abincin dare a part din nan.
Saurin dago kai nayi don jin abinda ya fadi kasa hakuri nayi sai da nayi magana nace wanan kasan ba zai yuyu ba tunda ga matar ka a gidan.
Bani kadai bace matarka kasani sai dai idan wani fitina kake son ka dauko min kuma ga yin hakan yace idan ba zakiyi abindana sakaki ba sai ki bari.
Zan fita waje na dinga ci a can nace idan hakan yayi maki nace indon abincin da zakaci ne ba sai ka fita kaci waje ba.
Yace shi zai fita fuskan shi babu walwala a cikin shi da alama ma bai karya ba zai fita gidan lokacin bishi nayi da kallo ina nazarin shi a raina.
Ajiyan zuciya na sauke tare da fadi a fili Allah ya kyauta koma may nene don banda amsa komai a yanzu.
Naki tasowa da wuri ne don kada in karbi girki a ranan yasa sai biyar muka taso na dare dayake motar mai lafiya ce Alkasim ne driver ya iso da wuri bayan gudun dayai ta shararawa damu a hanya mun iso ana sallah magariba.
Haka yasa ban damu da wani girki ba a ranan duk da nasan idan na tashi yi koda tsiya yadda takeyi zanyi nima.
Wanka nayi na shirya na fito falo wurin su laraba dake faman cire tsaraban da muka dawo dashi tana adana shi inda ya dace.
Zama nayi a cikin rashin walwala a tare dani sadiya da ke kwance nake kallo yadda yarinyar ke dada girma yanzu shi kuma kan dake da matsala yana kara girma sosai.
Naji tausayin ta sosai a raina ga ta dai yarinya ce duk da ba tada alhakin kowa a kanta amma Ubangiji ya jerabe ta da wanan lalurar a rayuwan ta.
Altine ce ta fito daga dakin du tana dauke da mami a hannun ta wuri ta samu ta zauna a gefe na tana fadin kamar in koma minnan nan naku nake ji.
Ban taba zuwa jahan ba a baya sunan girin kaidai nake ji ashe gaein babba ne haka ban sani ba gaku da abunci kala kala a garin.
Duk da naga kunfi maida hankali ga doya itace abincin mutanen garin sosai duk gidan da mukaje shine za a sarafa muna a wani launi.
Nace haba dai inda dai muka je kikaga hakan ai yanzu wasu saboda wayewan kai basu faye son doyan ba sai dai abincin zamani .
Bayan mun dan taba hira ne na mike na fita daga part din nawa gidan nake zagayawa inda tun a falon naga yadda ya koma tankar babu mata a cikin shi.
Din ina ganin ko kara ba a taba a gidan baya dada shara da kazantar da akayi ko ina na gidan kai na girgiza, tare da kwala wa Altine kira tana fitowa nace tazo ta gane min wanan wulakancin.
Nan Altine ta shiga zuga ni har naji raina yana tafasa sosai kira ba kwala ma samiha dake kwance a dakin su taki amsawa.
Part din na fada nace samiha da yanyala su fito tare da su Altine su gyara gidan nan tas ku wasu irin kazamai ne haka kamar ba mata ba zakuyi rayuwa haka a cikin kazanta.
Ku ke nan baku iya gyaran wuri sai dai ku bata kuna jira azo a gyara maku don haka ku fito ku taru ku gyara gidan nan yanzu.
Daga bayana naji muryan Nafisa tana fadin ba zasu gyara ba ke wacece da zaki shigo har nan ki basu umurni wai suzo suyi maki aiki.
Aiki aina kowa ne don su suka bata amma na saka su Altine da laraba a taru a gyara tace wanan ke ya dama don mu ba matsalan mu bane.
Waya na daga na kira AA ya dauka bayan ya dan dade yana ringing yana dauka nace mai cikin ladabi dama na kiraka ne don kaiwa matar ka magana gidan yayi mugun datti ko da muka dawo.
Mun samay shi ba a gyara ba tun tafiyan mu shine yanzu na saka samiha da yanyala dasu Altine su gyara amma ga Nafisa tace wai ba zasu gyara ba.
Yace bata wayan ko ki saka wayan a hand free yadda zata tajini na saka ban yarda na bata wayan ba yace Nafisa kina jina idan mutanen nan bazasu aiki ba kamar yadda aka sakasu suyi su bar min gidana kafin in dawo.
Yana gama magana na juya na fita na barta a wurin da takaici na ba abinda take kallo sai sauyin da take gani a gareni.
Sai mamakin yadda na juye

135 / 144

Chapters