MIJIN BUZUWA complete Hausa Novels.txt

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   33 / 144

96K to 99K   out of 431K words

kaima ka sani.
Please ka fitar masu dashi mu tafi don ina da abinda nafito yi yanzu ba wanan ne a gabana ba zaiyi magana yace fito masu dashi nace please.
Ai da ka barshi zuwa kawai mukayi in gaida mommy da su anty Fauziya da suka zo ya sake fafin don Allah ciro mata mu tafi ya sake maimaitawa.
Fita Yusuf yayi daga motar ya bude bayan motar yana fitar da kayan da aka saka a bayan motar sai da nayi mamakin ganin yawan kayan da aka debo muna mu kadai.
Haka na dake fuska daure na fita daga motan ban koyi masu godiya ba na fice fuuu a motar Yusuf ne ya tsayar dani yana fadin haba yar mama ki sasauta wanan fushin naki ku fahinci juna da mutumin ki.
Dan Allah yaya Yusuf ka daina hadani da wanan mutumin don ba ajina bane shi mutumin da yake under control din mace macen ma yar haure ba jinsin nahiyar mu ba.
To waima may kake son in kula shi aka in kula shi ya bata min lokaci ya hana mutanen arziki zuwa gurina ko may ?
Subbahanalahi ina wanan maganan ya fito haka a bakin ki baki taba tunanen Abdulsamad son ki yake bane ko may ?
Da sauri nace so so fa kace na girgiza kaina nace a,a dama kace kawai yana amfani dani ne wurin cin ma wani manufa nashi da zan yada da hakan amma ba wanan kalamin naka na so ba.
Sam na sake girgiza kaina karo na biyu tare da fadin wanan wani sallon yaudarane kuma ka dauko yanzu.
Yace to ko ki yarda ko kada ki yarda ni yau na fada maki son ki Abdulsamad keyi har cikin ranshi wallahi bai dai iya fitowa fili na ya fada maki ko ya nuna maki hakan.
Wani irin kallo nayi mashi tare da girgiza kaina na juya na fara tafiya ina jin wani bacin rai a zuciya har na shige ba tare da na dauki komai nasu ba da suka aje muna.
Kwanciya nayi ina tunane a raina maryam da wata suna shigo da kayan daki har suka gama ta debar masu ta basu daga ciki.
Ta dawo ta zauna tana ta faman cicire kayan guda guda tace kai khadija akwai wanda ya samu abinda muka samu kuwa a wurin nan jifa wanan uban kayan da aka loda muna wai duk namu ne mu kadai ina zamu da wanan kayan haka ?
Sai lokacin na dago kaina ina duban kayan data tara a gaban ta na maida kaina saman filo na kwanta magana Yusuf ne ke ta min yawo a zuciyana har wanan lokaci.
Maryam ne naji tace wallahi khadija na yarda da Yusuf daya ce son ki Abdulsamad keyi har cikin ranshi ba karya ya fadi ba don ni na dade da sanin haka tun tuni.
Ina jinta saidai ban yi mata magana ba har ta gama fadin abinda zata nace ke idan nace zan bata lokaci ga wanan mutumin ba zaki min fada ba maryam.
May ke cikin gidan irin su Abdulsamad banda tarin rikici da tashin hankali kulun ni kwadayi bai kai idona ya rufe ga abin hannun shi ba wallahi.
Salama nike nemawa rayuwana ko yaushe ba zan tsaya in yaudari kaina ga abin da nasan yafi karfi na tun yanzu akan matar shine fa ya daina kulani ke ma kin san da hakan.
Tace da sauri Kin san uzurin shine da zaki yanke mai wanan hukucin haka khadaji idan yana son ki ko Allah ya kaddara akwai aure a tsakanin ku matar shi ta isa ta hana ne ko tayi kamar Allah ne.
Sai dai in kece zaki bata kafan da zata hana din ta dauki kanta inda Allah bai kai ta ba kinatsu khadija ki san may son ki da zuciya daya.
Ni na fahinci A,A irin mazan nan ne da furta kalman so ke wahala a bakin su sai dai suyi ta nuna ma mace alama amma basu iya furta mata da baki.
Nace shine kike son in tsaya wahal da kaina gare shi ko may ni koda ya furta bai mun ba don ba zan so shi ba ma ban ra,ayin mijin tace a rayuwa na.
Ban yarda ba wallahi ke ma kina son shi kishine dai ke damun ki ke ma kina ganin kamar ya mutu akan matar shi ya daina kulaki don ta.
Haka zuciyar ki ta fada maki ashe nace mata bata ko fada maki daidai ba ke nan idan tace maki nima ina son shi.
Tace idan baki son shi may yasa yanzu kika rage mashi tsiwa irin da don da dane da yanzu kunyi fada a motan nan yafi a kirga.
Nace amma kin san wulakanci bai da kyau ko saboda haka ne na kyale shi badon komai ba yanzu dai ai kanku ake ji ku karaci gulman ku ku dawo hanya dai.
Indai har kin san kina son shi ya kamata ku daina wanan shirmay tun wuri tun bazuwa bata kara kwace maki shi ba kuma.
Ta kwace shi mana shi ya shafa bani ba nace mata cikin kunan rai tace dukkan ku dai ya shafa khadija bashi daya ba kin dai san so yanzu koda kike kirarin baki taba so ba a rayuwan ki.
Washegari a wurina su Binta da zainab suka wuni don ba shiga school Friday ne yau sai sunday zasu koma kd.
Don haka da yamma muka shiga gari dasu yawo sunyi mamakin sanin garin da nayi don sanin da sukayi min ba mai rigima bace ni.
Munsha yawo sosai rana sai dare muka dawo hostel dasu bamu dade da dawowa ba wayan Binta yai kara ta dauko da sauri tana dubawa take fadin nashiga uku yayane fa ke kirana zainab.
Zainab tace dauka mana kiji may yake kiran mu nasan dai sunga dare yayi ne bamu dawo ba suke neman mu ta dauka tana fadin hello yaya A,A yace kuna ina ne har wanan lokacin hankali mutane ya tashi.
Tace gamu nan wurin khadija tun dazu ita ce zata rako mu mu dawo yanzu yace tana da motane tace a a yaya karatu fa take yi ina zata samu mota kuma ?
Yace ganinan zuwa in dauke ku yanzu ku jirani in zo yace ya kashe wayan kallon ta mukayi nace yanzu ba zai bari ku kwana nan ba ke nan ?
Tace tunda kika ga yakiramu ai haka yake nufi damu nace bari yazo ni zan fita nagan shi da sauri tace ke baki san halin shi bane bari kawai yazo din mu tafi gobe sai mu dawo muyi sallama ba shike nan ba.
Zainab tace ni nafi sakewa a nan wallahi amma can gidan duk a tukure muke wallahi shegiyar matar nan tashi bata bari mutum ya wala a gidan.
Dariya nayi mata sosai da take fadin haka ba a jima ba sai gashi ya kirats yana fadin su fito nace barin je in gashi tace bari dai mu tafi ban son fadan nan nasa wallahi.
Maryam tace ku bari ta fita ta gan shi mana ai zai yarda ku kwana nan idan ta roke shi baku san ko waye bane yaya AA kawai.
Mikewa nayi na fita batare da na kula da kayan dake jikina ba a lokacin yana zaune a cikin motar shi ya fitar da kafa daya waje yana shakan iskan dake kadawa a lokacin .
Na iso gurin sallama nayi mai ya dago kai da sauri yayi min wani irin kallo ya kawar da kan shi kuma kallon da ada in yayi min nasan na bata mashi rai ke nan.
Sai dai yau ban san may yake nufi da hakan ba da yayi min shi nace don Allah ka barsu su kwana guna tunda gobe ne kawai haduwan zasu koma gida jibi.
Ya sake kallo na a karo na biyu yace su ke son kwana nan din sukace maki nace suke son hakan bani ba yace to shike nan indai zaki basu kulawan da ya dace may zai hana nace mai sai yadago ya dube nayi saurin kawar da kaina gefe daya nima.
Nace na gode na juya zan tafi naji yace khadija nayi saurin juyowa sai naga ya kada kai kawai sai kuma yace may yasa kika fito waje haka da wanan kayan ?
Don Allah ki bar fitowa haka na roke ki please kallon kayan dake jikin nawa nayi sai lokacin na ga kayan don na cire abayan da na dora sama da muka dawo daki.
Ki kula daga yau ban son ganin mace a waje haka gara idan mace tana cikin gidan ta zata iya amfani dashi haka ko ga mijin ta.
Kai na rausaya cikin wani irin jan aji da ban san nayi ba nace ga matar da bata da miji fa itama sai a hanatayin yadda take so ko may.
Yayi tsuki yace na dai fada maki ban so ki kula daga yau kada in sake ganin ki haka a waje daga yau.
Jikina ne yayi sanyi na kasa yin wani magana kuma ya kawar da kan shi gefe bai sake magana ba sai ya mayar da kafan shi daya dake waje tare da jan kofar motar yana fadin ni na tafi sai da safen ku.
Kin dai ji abinda nace dake ki kiyaye duk abinda nace dake ban so ban so ne ya rufe motar yai mata key gurin nake tsaye kamar wace aka kafe har ya bace ma gani na naja kafata na koma ciki.
Ina shiga na samay su har sun shirya suna jiran shigowa na dakin nace dasu yadda na gansu a takure yace ku fito bai yarda ba wai.
Zainab tace ai dama na sani don kada kice mun hana ki ne do ba mu son kwana din amma ninasan ba zai yarda ba ta fada a sanyaye.
Tare da fadin tashi muje Binta binta din taja wani tsuki tana shirin mikewa nace ya tafi fa tace don Allah ki bari nace wallahi ya tafi tun dazu na tsaya magana ne a waje.
Wai da gaske kikeyi khadija nace wallahi ya tafi yace sai da safen ku tunda anan kuke son kwana indai kula daku naso ce mashi mudake nan wake kula damu ?
Da sauri tace da kin muna tsiya wallahi nan dai muka sake muna ta hiran mu kayan bukin da muka dawo dashi a tare dasu mukai amfani dashi.
Sai hiran buzuwa da Binta ke ta bamu a dakin wanda inda tasan yadda raina yake baci da ta daina bamu labarin abin haushi haka.
Washe gari ma kusan tare dasu muka wuni a hostel din mu sai da yamma muka je gidan tare dasu yiwa sauran yan uwa sallama.
Mommy tace khadija kice bakin naki ne dai wanan irin fresh da sukayo haka wurin ki dan kwana daya da rabi injin dai ba dan abincin naku suka cinye ba.
Shine ya shigo nan ya gan mu kallo daya yai muna ya kawar da kanshi gare mu gaishe shi suke yi yace da alama kunji dadin zama a inda kukaje din ke nan.
Mun dan jima tare dasu mukai masu sallama suka rako mu zamu tafi sai ga driver yace ance ida zamu koma a sauke mu .

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Tunda mukai waya da Ya Amina tace min bata da lafiya sosai sai naji hankalina bai kwanta min ba ina bukatan zuwa kaduna weekend in dubata.
Kwatsam aka wayi gari inace wa maryam kaduna zan tafi yau in duba jikin Ya Amina da bata da lafiya tace shine baki fada min zaki tafi ba muje tare .
Nace kada ki damu watarana mu tafi tunda muna tare ai har bakin titi ta rako ni na shiga mota ta koma ita.
Da wuri na isa don sammakon da nayi na samu jikin nata da sauki sosai na fahinci ciki ne ta samu ashe yana bata matsala dama haka take ciki da wahala ita.
Gidan da bai samun gyara saboda laulayin da takeyi yasa gidan yayi datti da yawa sai da nayi wa gidan tas na yi wanka na kwanta don in huta.


Tunda ya fara shiri Nafisa take tsaye a kansa tana fada dashi akan may zaiyi tafiya yanzu bayan yasan halin da take ciki zata iya haihuwa ko yau ko gobe.
Ya dago yana ce mata tafiyan ya kama shi ne dole don haka na fada maki gobe zan dawo insha Allahu may nene kuma na fada yanzu.
Tace yanzun dai baka damu dani bane ban san may kake yawan zuwa yi gida ba akai akai haka ?
Au ke da kike zuwa gida wani abu kike zuwa yi a can tace zaka hada kaina da kaine nifa kasan ba nan iyayyena suke ba ya zama dole in rika duba su a kai akai.
Da kyat ya samu ta barshi zai tafi koshi don yace aikin shine zai sa ya tafi yasa Nafisan ta daga mai kafa.
Da suka isa kaduna zaria suka wuce kai tsaye don ganawa da kawun nashi dake neman shi ida sukai saa sun samu kawon a gida wanda ya nuna jin dadin shi da amsa mai kiran da yake mai din.
Bayan gaisuwa sun natsu ne kasun ke fadin ba wani abune yasa na kiraka ba sai yar wata magana da ta taso daga mahaifiyar ka a gamay da kai.
Zama ya gyara don ya saurari may mahaufiyar nashi hajiya mama tazo ma kawun nashi dashi duk sunyi tsit suna sauraron kawun.
Yace tazo nan ta samay hankali a tashe take fada min abinda ke faruwa dakai na rayuwa musanman da kai da iyalin ka.
Dama yasan maganan ba zai wuce wanan ba ai yace cikin karfin hali kawu wani abin tace nayi kuma yanzu ?
Yace eh to tace bata ce ba kasan dai tsakanin da da mahaifi akwai wani kulawa da damuwa na musanman shiyasa tazo min akai ya kamata a taimaka ma da addua da wani taimako.
Shine na kwantar mata da hankali nace zan yi wani abu akai don kasan naka sai naka a yadda naga damuwa a tare da mahaifiyar taka.
Yasa bayan mun rabu naje wurin wanj malami tsohone aminin mahaifin mu tun yana raye nakai mashi wanan matsalar taka.
To Alhamdullahi ya karbi maganan namu sosai da muhinmanci ida ya ce in bashi sati hudu zaiyi istihara sai a san abinda za a yi bayan satin hudun dana koma sai yace dani yana bukatsn ganin ka sai kazo da kanka zakuyi magana dashi.
Wanan ne yasa na kiraka don kazo ku samu ganawa dashi kaji may zai fada maka sai musan mafita ga zancen.
Zama Abdulsamad din ya gyara acikin ranshi yana fafin ikon Allah ita kuma mama tanan ta bullo min kuma yanzu bayan tasan ban son irin abubuwan nan tun farko.
Amma a fili cewa yayi to kawu ba matsala amma dai sai dai ina fata aikin shi ba na kaucewa Allah bane dai ?
Murmushi kawun nashi yayi yace haram haram kana ganin munyi kama da masu kaucewa alamarin Allah ne ya kamata ka shedi mahaifiyar ka kasan halin ta.
Yanzu haka ma bata san komai ba tukun a wanan zance nafi son muyi magana ta maza da maza kafin ta samu labarin komai.
Yace hakan na dakyau kawu don nima ban isa can gurin su ba tukun nan muka fara zuwa yanzu sai mun koma zan isa gidan.
Tashi sukayi zuwa gidan tsoho malam illu don su gana dashi sun samu yana ganawa da wani babban mutum don haka suka zau a motar su suna jiran fitowan mutumin.
Bayan mutumin ya fito ne kawun nashi ya ce su taso su shiga daga ciki suka fito daga motar zuwa ciki amma sai Yusuf yace zai jira shi a waje.
Ya juyo yana fadin haba haba Yusuf ya zakace haka kuma mushiga don Allah zai fi akwai abin da baka sani bane nawa.
Kawun yace mu shiga mana ai ba komai bane wanan mushiga daga ciki kawai mugan shi.
Cikin suka shiga tsohon yana kishingide saman farin buzu irin na dabbobi da malaman da ke zama a sama.
Yana ganin su ya dan dago daga kwanciyan manya da yayi nan suka zube don girmamawa suka fara gaida tsohon yace salihu kune tafe yanzu ?
Yace eh baba yaron da kace yazo ne dan wurin ita kanwar tawa hafsat yazo yau daga can abuja inda yake aiki don amsa kiran da kai mashi din.
Tsohon ya daga kai yana kallon su Abdul din yana jijiga kai yace Allahu Akbar yanzu wanan jikan mahaifi ku ne Allah ya jikan malam shaibu suka amsa da amin .
Ya dauko wani tasbaha ya rike a hannun shi ya dan murza ya mikawa Abdul din baya ya ce shine wanan din ko kawu salihu yace shine baba.
Yace canki daya a nan yana mika mashi tasbahan dake a hannun shi Abdulsamad din ya mika ya zabi dayan dan tasbahan tsohon ta girgiza kai yana murmushi.
Ya dago kai yace Abdul yake ko yace eh Abdulsamad yake sunnan kakan shi yaci na wurin mahaifin shi yace to kamar yadda na fada ma zanyi istihara akan jikan nawa Allah ya bani iko nayi.
Sai dai naga abubuwa da dama da suke faruwa da

33 / 144

Chapters