MIJIN BUZUWA complete Hausa Novels.txt

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   22 / 144

63K to 66K   out of 431K words

nayi ina sauraren ta tace abu daya zuwa biyu ne na farko gaba dayan mu sai mu dage da addua gaba dayan mu na biyu kuma kiyi kokari ki cusa mashi so da kaunar ki ta yadda buzuwa ba zata iya mashi gibi ba.
Har muka gama magana ta fita ban iya cewa komai ba ta barni ina cike da tunane a raina na yadda abubuwa ke zo min a haka.

Sai dare sosai suka shiga Abuja inda Yusuf ya aje shi gida ya nufi nashi gidan da motar shi da ya bari gidan don tafiya da ba shiri sukayi.
Ko da yashigo gidan shiru yaji kamar yau mutanen gidan nashi basu ciki bai tsaya falon ba ya haura sama inda dakunan kwanan su yake.
Ga kaya nan ko ina a warwatse ko ina agidan anyi amfani dasu an kasa kawar dasu don tsabagen kiuya da lalaci har ya kai kofan dakin ya tura a hankali ya shiga.
Baiyi mamakin ganin ta a yanayin da ya samay ta ba don duk kwanankin nan a yamutse take a gidan ba wani gyara ko kwaliya da take samun yi .
Tana zaune saman gado gashin kanta a wawatse ba gyara ta dago ido ta kalle shi tare da kallon agogon bangon dake dakin tace Samad ina kafito a wanan lokacin.
Aikena kikayi da kike tambayana ya bata amsa tare da wuce wa wurin wardrobe din shi yana rage kayan jikin shi.
Samad neman mata kafara ko mai yace idan na nemay su ba namiji nake ba wallahi baka isa ba ta fadi da karfi ya juyo gare ta yace ban isa ba fa ki ka ce Nafisa.
Tace baka isa ba wallahi may na rage ka dashi a wanda ban baka da har zaka lakanci neman mata a yanzu daga sama.
Ya ciro wani dogon jallabiya baka yana fadin waya san iyaka Nafisa baki san komai ba banda son kan ki da kashin kudi abaki kuma baki godiya.
Kudi dole ne ka bani don kasan sune buri na kuma akwaisu bathroom ya shiga ya barta ta ta fadin bakaken maganganu gare shi har ya fito bata fasa magana ba.
Gadon ya duba yace duba don Allah wai a inda mutum zai kwanta ke nan ya fara kakabe shimfidar da wani dan karamin towel daya fito dashi daga ban dakin.
Yace mace sai tarin kazanta na fada maki bani son wanan kazantar taki amma ke abin sai gaba yake yi gare ki.
Ai kasan a haka nake kuma ka aure ni na dauka idan kin shigo cikin daula zaki canza ne ashe ni ban san abin a jinin ki yake ba.
Kazantar ne a jina na yake Samad yace in ba ajiin ki yake ba za a ce duk yawan ku baku iya gyaran wuri tace samad wa kake so in sa aiki a cikin gidan nan.
Kafa san daga kanne na sai yayyena anan sai kuma kawu naina da gwago na yace may yasa kika boye min hakan da farko kin fada min yan aiki ne kika samo min kuma biyan su nake duk wata.
Sai yanzu zaki ce min wai yan uwan ki ne na jini baki iya saka su aiki a gidan nan kin zo gidan nan kin samu masu aiki kika ce baki yarda dasu ba.
Na baki go ahead da zaki kawo wanda kika yarda su suyi mana aiki ashe ke yaudarana kikayi ki kwaso yan uwanki kika cika min gida dasu.
Samad ta fada da karfi kawo yan uwana danayi a gidan shi ne kake kira da yaudara yace yaudara ne mana mutum da gidan shi ba dama ya shigo ya huta a ciki yaji dadin ranshi.
Samad yau ni kake fada ma haka don ka gani da ciki kake kokarin ka wulakantani yanzu ko may babu zancen wullakanci sai maganar gaskiya.
Haukace mai tayi ranan tana fadin bai isa ya rabata da yan uwanta ba don tare ya gansu ya kuma yarda ya aureta a hakan.
Haka ya kwana da tarin bakin ciki babu kunya washe gari kuma sai gata ta neman sulhu dashi don dai kawai ya biya mata bukatan ta don bata iya hakkuri dashi duk yadda ranta ya baci dashi ga wasu kudi da take son karba a wurin shi masu yawa don ai mata aiki a kan shi.
Bata samu ko daya ba ranan don asubanci yayi ya fita wirin aiki da wuri koda yaje gurin aikin bai iya aiwatar da komai ba.
Yusuf ya shigo ya samay shi a haka yake tambayan shi wai may ke faruwa dashi ne bai tsaya boye mashi ba ya sanar dashi halin da yake ciki da nafisa a gidan shi.
Da yan uwanta da suka cika maigida da sunan yan aiki ta kwaso yana biyan su a wata ashe ba haka abin yake ba.
Kai inji Yusuf lamarin Nafisa akwai daure kai wallahi Abdul yace nima bashi ba kazantar nan ke damuna Yusuf.
Ka san dai halina da kyakyami wallahi komai na gidan nan yanzu kazantar shi nake ji in ba ruwan gora ba ban iya cin komai a gida na .
Yusuf yaya zanyi da wanan masifa dana dauko ma kaina nasan ina son nafisa sosai why da ba zata gyara halin ta ba may ye ban ma Nafisa a rayuwan ta.
Kamar karta samu cikin nan yanzu abin ya karkare jagule mata mace ba wanka ba saka sutura a jiki idan anyi magana sai tace wai lalurar cikine haka take cikin ta.
Au dama ta taba ciki ke nan naga auren budurwa mukai mata wani kallo ya jefe shi dashi yace Nenan yar waye idan bata taba haihuwa ba nima daga bayan nan na fahinci yar tace ashe.
Yanzun haka zan kare ga yawon restaurant ina cin abinci a garin nan kamar wani mara galihu dani.
Kai innalillahi abin nakune akwai daure kai wallahi saukin abin khadija zata dawo next week zaka dan samu sauki a awurin ta.
Saukin may zan samu a gurin ta ya tambayi Yusuf a yanayin rashin fahintar maganan shi Yusuf yace koba komai tunda ta iya girki naga ai zata dan dinga maka idan tana da time.
No ban san in jefa rayuwan yarinyar ga halaka ko kadan nafi son ayi komai a kaidance yace kana nufin auren ta zakayi.
Shiru yayi ya dafe kanshi bai sake magana ba ya fahinci bai son maganan don haka ya kyale shi tare da canza topic.
Yusuf na fita ya jawo wayan shi ya kira layina muna gida ya Hauwa mai jego ya kira wayana ina wanke kayan miya a kitchen aka kawo min wayan.
Sai da ya kusa katsewa na dauka tare da sallama yace ina kika shiga kika bar waya na ruri haka nace ina kitchen ina girki wa ya hauwa da ta haihu.
Kuna gidan ta ke nan ya tambaya nace eh may kike girka mata nace miyar shuwaka zanyi mata da tuwon shikafa.
Ke wa ya koya maki girki haka ne wai nace girkin ma har sai an koya ma mutum yin shi idai kana mace ai zaka iya girki ko wani iri dole.
Aranshi yace ga macen da ta san kanta ba sai kuma yace ke wace irin yarinyace da baki iya kiran mutane kiji ko sun sauka lafiya ?
Na aiku tafiyan dare ne ko ni na saka ku yin tafiyan da kuyi din yace OK haka zaki ce ma nace haka din ne ma ai.
Sai naji ya kashe wayan dariya nayi nace zaka kaji ai ka daina in yar da magoro in huta da kuda har dare muna gidan sai tara muka dawo gida a gajiye .
Ban kara bi ta kanshi ba har akai bukin suna aka watse lafiya drinks din da suka kawo muna yayi muna rana do shi mukai amfani dashi wurin taron sunan.
Mun fara shiri don tare da yaAmina zamuyi tafiyan kamar yadda na fada mata yace zai turo mota hakan ne ya faru sai ga mota zuwa sha biyun rana ya tsaya a kofan gidan mu.
Nan muka fito mukayi haraman tafiya nasha nashi ha a wurin mama da daddy kafin mu wuce muka dauki hanyar Abuja tare da ita don zata kwana a wurin mu.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU


INA BUKATAN ADDUAN KU YAN UWA ALLAH YASA MU DACE
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Kamar yadda yace nice mai tsara mashi tafiyan haka yasani a gaba dole sai dana tsara mashi zuwa gidan da zai yi da abinda zai kai gida.
Da farko na dauka zolayane sai da naga abin nasa da gaske ne na tsaya na tsara da taimakon maryam nayi komai.
Wanan karon bai sai kayan tsaraba ba kudi muka tsara zai bayar idan yaje sai abincin da zai sai ma iyayyen shi don rage ma mahaifin shi nauyi.
Da yamma lis suka isa kaduna don haka ya wuce gidan shi bai shigo wurin su hajiya ba sai da safe bayan ya karya ya shiga gaida su.
Sai da yagama gaida abokan zaman hajiya suka wuce nata part din dake daga can ciki yana fuskantar part din mommy.
Sai dai tsakanin su akwai dan filin tsakar gida da shuke shuken filawoyi a gurin da wani babban icen ambrale dake basu innuwa a gidan.
A kofa su kai sallama ta amsa masu daga ciki suka shigo ko ina na falon tsab yake sai kamshin turen wuta dake tashi a falon.
Tana zaune tare da kannen shi Binta da zainab su uku a falon gaida shi kannen nasa keyi ya amsa masu a tsatsaye tare da zama saman center capet din falon shi da Yusuf.
Gaida hajiyan sula farayi a cikin ladabi inda hajiyan ke nuna farin ciki da ganin su tare da fara,a a fuskanta.
Tana man kamar yadda take a cikin gyaran ta ko yaushe atamphar super ne ja a jikin ta babu wani alamar tsufa ko girma a tare da ita hutu da jin dadin da mijin su ke basu ya kama ta.
Cike da kula take amsa masu tare da tambayan da Nafisa suka zo ne Yusuf yace su kadai suka zo don Nafisa cikin ta ya fara girma yanzu.
Tace cikin mamaki ciki ke ga Nafisan bamu sani ba mu tana kallon su cike da kulawa Yusuf yace wallahi hajiya ai cikin ma yanzu zai kai wata shida ko bakwai.
Ikon Allah to Allah ya raba lafiya ashe da baka fada yanzu ba da sai dai muji haihuwa kawai.
Yace ba akai ga haka ba ai hajiya zakuji ne don dai ba a tare ne Affan ne ya shigo falon bai mai da hankali shi wurin su ba sai fada ma hajiyan dayayi a jiki yana fadin wai yaji ciwo a waje.
Tace baka ga Abban ku bane Affan daba gaida su ba yaron ya dan kara lafewa a jikin kakan nashi Yusuf yace malam Affan kuna lafiya ina daddy yake ?
Hajiya ke fadin maza ka gaida Abban ka da baban ku daga jikin kakan yace ina wuni bazakaje kusa dasu ka gaida su ba in ji Binta dake dagawa daga inda take zaune zainab ko sai charting take a wayan ta.
A dadare yaron ya isa gurin su yana kara gaida su Yusuf ya jawo yaron a jikinshi yana tambayan shi dan uwan shi yace yana gurin mommy su.
Hajiya tace ai shi wanan dan lake ne tunda uwar tabar gidan ga ta koma gidan su kullun yana can like da ita.
Da sauri Yusuf din yace hajiya Fati ta koma gida ne kuma tace to mu rike ta ne nan tunda abin yaki ci yaki karewa haka.
Ai gara dai ta koma gida ko hankalinta zai kwanta a can anan taki ta sake sai rama da takeyi kullun Abdul ya mika hannu yana tambayan yaron labarin makaranta.
Yayin da Yusuf da hajiya ke magana akan komawan fati din gidan su yace zamu lekata kagin mu koma abin ne sai an hada da hakkuri.
Don Fati taki tayi hakkuri da yanayin Nafisa amma ai ita ta zabi ta zauna nan kaduna cewan ta hankalin ta yafi kwanciya da nan din.
Wayan zainab dake gefe ne yayi kara ta dauka tana fadin Khadija Adamu wallahi nayi fushi dake ai tana mikewa ta shige dakin su.
May wanan yarinyar ta bugo ta fada ma zainab yanzu ko dai komai da sanin su take aiwatar wa yace a zuciyar shi sai ga khadijan ta fito tana hajiya ga khadija na son gaida ke.
Ta amshi wayan da faraa a fuskan ta muka fara gaiswa da ita ba wani dogon magana bane gaida ita kawai nayi tana sa min albarka.
Ta mikama zainab wayan ta ta sake shigewa ciki shiru falon yayi sai hajiyan ne ke fadin yar albarka yariyar na da hankali sosai wallahi.
Ta juya tana fadin yarinyar nan da nasa ku rage ma hanya wani lokaci da zaku koma abujane Yusuf yace oh khadija tana da kirki sosao wallahi.
Ai nikan dan leka ta wani lokaci mu gaisa idan na samu lokaci tace ka kyauta haka ake son mutum ya zaba ma kanshi abu na gari.
Yace hajiya babu komai a tsakanin na da ita wani dai ma yake raayin ta yanzu haka don yabawa da hankalin ta da yayi har lokacin hira yake da dan shi dabai sake jiki dashi ba.
Ya dago kai yana fadin hajiya ko Abba ya fito yanzu mu gaisa dashi kafin ya fita tayi murmushi tace ai yanzu Alhaji ya rage fita kasuwa don yanayin girma da kuma jikin shi yana gida koda yaushe.
Binta ta kwala wa kira tazo ta kira mata mommy a dakin ta don tai masu iso gurin Alhajin mommy ta shigo tare da Binta dataje kiran ta hajiya ke fadin dan ki zaki wa iso gurin Alhaji wai.
Mommy tana murmushi tace kai hajiya sai kace wani bako a gidan Alhajin yana nan falo ya fito yanzu ma na baro wirin sa ta juya ta fita zuwa fada ma Alhajin zuwan su.
Sai lokacin ya dubi hajiya yace wanan karon ban riko komai ba yana sa hannu a cikin aljihun shi yace ga dai kudi a kasa fa aba su mommy dubu daridari sai yaran nan a raba masu dari biyu ke kuma ki dauki sauran ya zube kudin a gefen mahaifiyar sai kuma abinci da anjima za a shigo dashi.
Ta kasa boye farin cikin ta nan ta shiga saka mai albarka mommy ne ta dawo dakin tana fada masu su shiga yana jiran su har mommy ta juya hajiya tace .
Mommu yara da alama adduan mu ya fara kana dan ki yanzu ga kudi ya kawo a raba ga kuma kayan abinci a tafe.
Komawa mommy tayi dakin tana fadin kai madallah Allah mun gode maka da dan mu ya fara dawowa gare mu.
Haka ake so wallahi amma da babangida kamar wanda baida kowa a duniya da gatan ka zaka bari shedan yana rudin ka.
Ga dan uwaka nan Suraj sai shine ke bamu talafi bawai don bamu dashi ba don nemawa kansa albarkan mahaifa kawai don Allah aci gaba da kula da hakkin mahaifa dana.
A da ya tsani mommy sosai don yana ganin nuna mashi kulawan da take kamar duk a munafunci ne sai yanzu yake fahintar halinta ne kawai a hakan ga yaran gida musanman na hajiyan su da takan nuna nata ne.
Ita mommy Allah bai bata haihuwa da yawa a gidan ba daga Sadiq danta na fari sai salma kuma ba wasu manya bane sosai yanzu ma suke a secondary.
Yace mommy in sha Allahu za a gyara kwanan nan ma zaki tafi abuja wurin mu don Nafisa ta kusa haihuwa ke nake son kije tare da iya na zaria ku zauna a gidan.
Ba mommy ba har hajiya sai da tayi mamakin jin wai yau Abdul ne da kansa ke fadin wani nasa yaje gidan shi ya zauna don matar shi da zata haihu.
Kirikiri a baya tace bai yarda kowa nasa yaje gidan shi ba don suna zuwa suna tayar kashi da hankali a gidan shi haka Nafisa ta fada mai a baya.
Hajiyan su ce tace yar ikon naka tasan da haka kuwa yace haba hajiya sai ta san da hakan mahaifana da yan uwana zasu zo gidana.
Idan na gama shiri zan aiko a dauke su yanzu idan na shiga gurin Abba zan sanar dashi bukatan hakan don ba zan so ta haihu babu wani dan uwana a kusa ba.
Allah ya kaimu mommy tace da murnan ta fita daga dakin cikin farin cikin canjin da suka gani gareshi.
Wayan shine yayi kara ya mike yana amsawa ya bar Yusuf a gurin hajiyan Yusuf yace hajiya muna bukatar adduan ki kamar kulun yanzu haka akwai yarinyar da Abdul ya fara so ina ganin zata iya zama da Nafisa.
Duk wanan shiri nane don ba mace matsoraciya bane zata iya gwabzawa da halin nafisa ba don haka a tayamu da addua akan zancen in lokaci yayi nasan zakifi kowa farin ciki da zancen.
Hajiya tace ashe ba batun mayar da Fati kuke yi ba ku wani tashin hankalin kuke shiri daukowa yace hajiya wanan shi kadai ne nake ganin mafita ga alamarin.
Tace to shike nan addua dama kulun munayi

22 / 144

Chapters