isheki ba ki fuskanci rayuwan dake gaban ki da kanshi zai dawo ya koma kunyar ki a gidan nan zaki ce na fada maki watarana.
Gani da komai da namiji ke so a gurin mace gyagije ki koya mata hillan mu na mata ki nuna mata ke ma kin iya fa.
Muka fito muna dariya suna zaune da su madam suna kwasan kanu labarai a gurin nafisa sai gamu mun fito madam tunda ta kyala ido taga anty Hauwa tasha jinin jikin ta muna fita daga falon tace.
Nafisa may ya kawo hauwa black din JJ gurin wanan yarinyar kuma Nafisa tace waye ita din sai da ta kalli kofan da muka bi tace ashe akwai shegiyar kuwa.
Indai wanan yarinyar da Hauwan JJ take hurda a garin nan idan baki mike tsaye da kyau ba watarana sunan ki sorry a gidan nan.
Nafisa ta dafe kirji tace kin barni a duhu sai zuba kike yi haka tace itace fa hajiya sabuwa ranan take bamu labarin ta wurin hatsabin banci ga kudi amma ba wanda ya isa ya rabi mijin ta yanzu har gida zata ci mashi mutunci.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Na dawo daga raka su anty a yadda na samay su falon ya nuna min suna wani magana mai muhinmanci ne.
Har na dan shige naji muryan Nafisa tana fadin ba wata hauwa zaki jira ba ko uwar hauwa ce bani shayin ta kamar in wuce sai na dawo baya.
Ke karamar shu,uma kin tsargune da ganin anty hauwa gidan nan gida kan dole ta shigo cikin sa tunda yar uwarta na cikin sa.
Ba a hana guzamay irin wa yan nan shigowa ba na nuna su madam da yan uwanta nace sai matan kirki irin su anty hauwa za a hana .
Ai in kin ga bakina sun daina shiga gidan nan tabbatar da nice bani gidan nan barin gidan nan kuma gare ku tankar hasaran ku ne kuma don a tare zamu fita daku.
Karya kike wallahi ai wanda ya riga kwana ya riga ka tashi na cabe da fadin ke nan zaki rigani fita kenan ko ?
Tunda kin rigani shiga ke mai gayyan tsiya ba ai magana ba sai ni dana tarkato baki alheri zaki magana.
Bakina yan yar arzikine irin alheri ko ruwan gidan AA bai ishesu kallo ba balle abinci gidan shi wanan sai yan yunwa irin ku masu gayar har dangin su da abikan bushasha a zo ataya su cin arziki banza ta fadi.
Ke yarinya kada kice zaki fada min magana inji madam to uwata kin tsargune ko kin sha ruwan gidan nan ne ke ma ?
Na wuce ina dariyan ke ta nan nafisa da yan uwanta suka shiga magana ina jin su ban tsaya bin ta kansu ba na shige part dina.
Ina shiga ban tsaya falo ba daki na shige na dauro alwala na fito na fara sallah nakai wani lokaci ina sallatus tasbihi ga ubangijina na gama na bude kur,anina na shiga tulawa a gurin.
Sai sha biyu da wani abu na daga wurin falo na shiga na samu laraba zaune tana kallo zama nayi ina fadin mama yunwa nake ji ban karya ba yau.
Tace na gama abinci naga kina son dafa duka mai ganye shina dafa muna uwar dakina naji dadin ganin ki haka kin maida komai ba komai ba yanzu ki barsu da halin su.
Allah bai barci bai gyangyadi yana kallon kowa da halin sa ne mai hakkuri shike da riba wata rana ai ta mike ta zubo min abincin ba laifi naji dadin abinvin sosai.
Nafisa ta kalli madam bata damu da wa yanda ke falon ba a lokacin tace ni na rasa jinin wanan shigiyar ko wani irine madam.
Jifa abinda arnen bokan na ya fada shekaran jiya nashikan naga fa,idar shi sosai don jiya sun kwasa da Yusuf amma wanan kamar abin bai haukan ta ba ita.
Madam tace irin su shegu basu shigowa ai sai sun shirya ba a banza suke shigowa duniya ba ki dai bi a sannu har ta haihu kinji boka yace sai ta haihu zata hudu .
Samira dake zaune tana ma baby wasa ta dan dago ta kalle su sai kuma taci gaba da yin wasa da hannun yarinyar.
Na idar da sallah a zahar ina zaune sai ga Samira da ihisan a dakin sun samay ni falo ihisan tace abinci anty.
Nace maman ki zatai fada ida kinci abinci nan Samira tace anan zamuci ban son abincin part din mu ba dadi kamar naki.
Laraba nace ra dibo masu sun zauna sun fara ci Samira tace anty haihuwan baby zakiyi irin na Ami din mu nace wa ya fada maki.
Tace Amin mu da madam naji suna magana dazun wai sai kin haihu zasu huda ki su huda baby anty kada ki haifi irin baby Ami don Allah.
Ami bata son baby nan nata tayi ta dukanta tana zagi wai jinin ki nada karfi ba a iya hudaki yanzu inji madam ta dago tana tambayana.
Eh Samira sai na haihu tare da Amin din ku za, a hudamu idan na haihu amma itace zataji ciwo ai idan an huda mu din fuska ta bata.
Tace shiyasa sukace ke boka yace baki huduwa da sauki sai Abbi din don shi tun shekarajiya an huda shi.
Duk da gabana yana faduwa da zance yarinyar amma sai na biyewa shirmay ta ina fahintar wani abu hartace wai a filon Abbi ansaka mai abu shiyasa ya hudu da sauri.
Shigowan maryam ya katse muna hiran yaran da muke sauraran abi boye daga shirmay su na fahinci iyayyan suna hira ne a gaban su.
Maryam ta bisu da harara nace ya haka kuma ta zauna tana aje jakka da gyalenta a gefe suna gamawa suka mike anan suka bar kayan da sukaci abincin suka fice.
Shegu suma sun iya kwadai irin iyayye su nace maryam ai zuwan ki ya katse muna jin laraba ne yau nan dai na kora mata abinda yarinyar tace.
Ido waje maryam tace mun shiga uku wanan matar dai a haka zata mutu ga bin bokaye da yan tsubbu yanzu ya za ayi nace shinake tunane.
Maryam ni na dade da sanin haka tun fadan mu da ita na rasa gane kan AA a gidan nan magana ma sama sama yake hada mu yauma karewa fita yayi bai shigo part din nan ba.
Yanzun kin gane ni sai naga ki bari sai idan yana gida kije dakin gyara mai ki bude filon a gaban shi ki nuna mai tare da tambayan shi wanan nasa ne idan kin gani amma kafin nan ki fara dubawa idan gaskiya ne.
Duk wanan sakacin ki ne da mijin ki khadija kallon ta nayi tare da fadin sakacina kamar ya fa tace wallahi sakacin ku ne khadija.
Khady ke malama ce kin iya karantawa ki rubuta da kanki yanzun bansan matsalanki ba khady duk kin yi laushi da yawa baki irin wanan kiza kizan naki.
Laraba tace ayyah ai abin ba hakana bane ke dai kada Allah ya hada ki da irin wa yan nan matan shu,umai barin ta banza akayi kike zato.
Jifa fa ba fasa yinsa ake ba a kullun jifanka ake amma ai uwar dakina tana kokari wuri ibada sosai wallahi.
Nan dai muke ana ta tataunawa kan matsalan har yamma ta tafi kamar yadda bai damu ta duba mu ba nima haka na dage mai kafa har ya gama borensa.
Ina daga daki wayana dake falo ya dauki ruri laraba ta kawo min dakin hajiya mamace kan layi mun gaisa ta tambaye ni jiki na ce alhamdullahi mama.
Tace to yaya ina akwai canji fa alamarin gidan naku ko yanzu nace akwai mama tace ban kirashi ba shima bai kira ba tun ranan.
Nace mama kiyi hakkuri abin sai a sannu da addua don kullun halinta kara baiyana yake na sheri.
Nagama waya na kashe falo na fito naji ana sallama laraba ce ta leka security din gidan ta gani a kofa na yace Alhaji na da boko waje yace a kira masa daya daga cikin matan gidan nan.
Nace bakon ya fadi haka yace eh sai dai naga suna da zubi da Alhajin gidan nan sosai sai dai na gidan nan yafi shi tsayi da haske sosai.
Daki na koma na dako hijjab na fita duk da ban san shi ba amma ganin shi da kakin soja yasa na fahinci shine.
Da fara,a a fuskana nace yaya Suraj kaine a gidan mu yau sannu da zuwa ya amsa min tare da fadin ko kece amaryan ta mu nadan yi murmushi nace bissimillah ka tsaya nan mana.
Yace nazo security din kun sunce maigidan yayi tafiya duk da ban sani ba nace eh yace ok yanzu muka sauka shine nazo nan in dan watsa ruwa kafin in samu masauki.
Ashe maigida ma baya nan nace ko bayanan aimu muna nan yaya shigo daga ciki na fara tafiya ya biyo ni zuwa ciki part din AA na nufa dashi na bude dayan dakin nace ya shiga tare da fadin barin je in hada ma abinci yaya.
Yace ya gode nafice a falo muka hade da Nafisa tana huci tare da fadin dama na sani har kwasan mazan naki yakai ki dauki kato ki kai sashen miji na.
Waye kato naji ya fada daga bayan mu ashe ya fito yaba da sakon a sawo mai katin waya ya samu muna magana.
Sai da naga kaduwa a tare da ita data ganshi ya nunata yana fadin har yanzu wanan halin tsiyar taki yana nan ashe yace to na dawo kasan zamu zuba dake a gidan nan don a nan zan zauna daku kwana biyu kafin in kama gida.
Naji dadin har cikin raina ya sake nuna ta yace ki natsu a dan zaman da zanyi a gidan nan tare da ku don ko mijin ki ya takani yasan halina ba raga mai zanyi ba balle ke.
Murmushi nayi na wuce part dina naje nace wa laraba mama yau muna da bako yaya Suraj ne ya dawo anan zai zauna tare damu kwana biyu.
Abinci lafiyayye muka hada mai takar wanda nake hada ma AA na kai mai a dinning na aje na kwankwasa kofan nace abinci na kan table.
Ya dan leko yana fadin ya gode na fita saida na koma nake fada ma laraba ashe wai maigidan yai tafiya ne tace ikon Allah kuma shine babu ko sanarwa haka ?
Nace ba komai mama ni dai Allah ya sauke ni lafiya shine addua na ko yaushe yanzun banda lokacin komai a rayuwana.
Nafisa ko a bangaren ta tun fafatawan ta da Suraj ta shige daki sukuku tana kiran madam ta dauka tace madam kina ina yanzu ?
Madam tace wani matsalane kuma ya faru yanzu tace wanan dan iskan ne yau yazo gidan mu bakiga yadda nake kaduwa ba don tsoron shegen mutumin nan nake a rayuwa na.
Madam tace ke ki debe wanan tsoron ki nuna masa shi din may har yaushe zaki tsaya wani kanin miji yana baki tsoro kamarki yanzu kuma.
Nan dai ta bata karfin gwiwa akan zaman da zaiyi a gidan kan kada ta sarara mai don tasan AA bazai yarda ba ai mata wullakaci.
Iyakata dashi in kai mai abin karyawa kafin ya fita idan ya dawo da dare kuma in kai may yau weekend bai fita ba yana dakin shi kwance.
Daga can yake jin dararakun su ya sauko ya samu wani buzu zaune yana sharara masu labari sai dariya suke kwasa saukowa yayi daga sama tun kan benen yake fadin kai may ye haka su waye hakan kuma.
Gaba daya suka maida kallon su gare shi har ya sauko kasa yace wa yan nan fa daga ina suke haka ne ?
Ya nuna namiji yace kai tashi ka fice cikin karfin hali tace ya fice gidan ka ne gidan dan uwana ne fa yace ok belt din jikin shi yake zarewa a hankali.
Kagin buzun yai azaman tashi har ya make shi a kasa ko ya nana kasa ya fara kai mai belt da shuri duk matan suka mike suka fara kururuwa.
Ihun su muka ji nida Labara muna rigen fitowa abinda muka gani yasa mu ja baya daga kofa na muka tsaya kallo abinda ke faruwa.
Sauran mazan dake waje suna dafa shayi suka shigo gidan nan ya hada dasu yai ta aika masu shuri da bugu da belt.
Hankalina ya tashi na fara rokon shi yayi hakkuri Nafisa ko wuri daya ta manne da yan uwan ta suna kyarma ya na huci ya nunata yace sai nayi maganin ki a gidan nan shegun karuwai kawai.
Wani dadi naji a raina yau ga mai maganin shegu yazo gidan juyawa yayi wurina yace duk wa yan nan a nan suke ne kai na gyada mai ya waro ido yace duk wanan taron a gun mutum daya yake mutum kusan ashirin da wani abu.
AA wani irin mutum ne shi da baida tunane yaya gidan ka zai zama happy family da wanan kwama calan haka zai dawo zamu hadu dashi gidan nan.
A daidai wanan lokacin ne maryam ta shigo ta samu an gama rikicin yana masu sababi duk sun shige daki sun boye.
Part dina muka shiga ba abinda muke sai labarin muna dariya mukaji anyi nocking din kofa.
Laraba ta mike tana dubawa shine tsaye a kofan yake tambaya ina ina tace gani a ciki yace kice mata zan shigo.
Ta juya ta fada min da sauri muka gyara ya shigo da sallaman shi waban karon ya canza kayan jikin shi zuwa jallabiya.
Wuri ya samu ya zauna tun ban mai iso ba yace madam gurin ki nazo sai dai naga kamar kina da bakuwa yanzu din nace kawatace ba bakuwa bace ai yaya.
Yace good zan so in tambaye ki wani abu gamay da gidan nan dafatan zaki ban amsa yadda nake so ba tare da kin boye min komai ba.
Nace insha Allahu yaya idan na sani zan fada ma yace good buzayen su nawane a gidan nan nace gaskiya ban san adadin su ba yaya kai ya gyada ya sake fadin kina ganin sun kai how long a nan nace ban sani ba don nima anan na samay su gaskiya.
Yace kina nufin duk dadewan nan suna gidan nan tare daku nace eh yace wanan wani irin rayuwa ne haka ina mutum zaiji dasin rayuwan sa a haka ?
AA wani irin mutum ya zama da baida lissafi wallahi dan zama nan mutanen nan suna takura min sosai ba dama mutum ya dawo da gajiya ya huta sai sun damay shi.
Kada ki damu zanyi maganin abin insha Allahu maryam tace mun gode yaya wallahi da abin yai dadi gidan sam babu kwanciyar hankali ko kadan .
Yace kada ku damu ku dan bani time mu gani har ya dawo ya mike ya fita yanufi kofan fita wajen gidan kiran wani buzu yayi yace ya kidaya mashi su nawa ne a gidan nan.
Na fito rakiyar maryam yana zaune saman motar shi muka gaida shi yake fadin zata koma ke nan nace eh yace barin sauke ta don nima gari zan shiga nayi mata sallama na fita.
Gidan ya koma shiru kamar ba taron nan a cikin sa nace wuta soja ga wuta ga halbi don dole yau kowa ya natsu badon Allah ba.
Ashe bayan sun fita ya bugi ciki maryam yaji komai na gidan tunda ya fahinci na boye mai wani abu ba gidan dake faruwa.
Washe gari nayi bakin course mate dina tun da nai aure zuwan su na fako ke nan gurina mun dade dasu sun fito na rakasu zasu tafi lokacin motar AA ya shigo gidan ban ko kalli inda motar take ba balle sannu da zuwa.
Shima kallon mamaki yake aika min daga inda nake muka gama magana suka ja motar su muna dariya suka tafi ni kuma na juya na shiga ciki ban kara bi ta kan sa ba kuma.
Wai ashe hakan da nai mai yaji zafi kodana shiga ban fada ma mama ya dawo ba na shige ciki don yin sallah la,asar.
Ina sallah ya shigo dakin bai ko sauya kayan jikin shi ba muryan shi naji suna gaisawa da laraba a falo tana mai sannu da zuwa ya leko dakin ina sallah tsaye yai min dakin ni kuma danaga haka ban yi saurin katse sallah ba.
Sai dana gama addua na shafa na mike ina ninke sallaya na gurin muryan shi naji yana fadin ke baki san nayi tafiya bane da baki iya yiwa mutum sannu da dawowa ba ?
Da zaka tafi ka fada min nai maka Allah ya tsare hanya ne da zaka zo ka tsare ni yanzu Allah dai na ganin ka duk abinda kuyi a gidan shine gata na.
Na fadi ina nufar side drower dina don aje carpet din sallah yace kina nufin sai na biyo ki nan na fada maki zanyi tafiya kin min wullakancin da kika saba yi min zaki gaida ni da dawowa komay ?
Zama nayi a bakin gadon