cin amarci na juyawa nayi na kyaleshi ba tare da nayi magana ba kuma.
Dan dariya yayi yace don nace ina cin amarcina laifine kuma nace wanan ne cin amarcin gida tab da yan sa ido.
Dariya ya soma min tare da fadin nafa lura wanan amaryan tawa wurine bata samu ba da amarcin yafi nan da zan samu ashe.
Yana fadin haka tare da rufe system din nashi ya hawo gadon tare da runguma na zuwa jikin shi ranan kan bai sarara min ba sai da ya debi rabon shi a jikina son ranshi.
Duk da ba wani gudun mawa na taimakamashi dashi ba amma hakan bai hana shi yai min sheri ba nikan wai yaya zanyi da wanan mutumin ne wai.
Ashe shi yana min hakane don tsokana yaji tsiwa na sai dai bai sani ba yanzu baki ya mutu kunyan shi da nauyin shi nake ji yanzu sosai.
Ana gobe zai wuce ne na tura maryam kasu don ban iya zuwa ta sawo min tsaraban da zai kai min kaduna din.
Banyi tunanen komai ba na shirya tsaraban kamar yadda nake bukatan su jira nake ya shigo in fada mai wayana yai kara shine a layin ya kirani falo.
Da mamaki na tashi ban fita sai da na tsaya gaban mirrow na kalli fuskana tare da fesa kamshi a jiki na fito shar dani.
Sai dai may ina fito na samay shi zaune a falon ga Nafisa a gefen shi tana kada kafa daya saman daya ta mike kafafuwan ta kofana dukkan su suka zura ma ido su ga fitowana.
Tunda na tun karo falon na samay su a haka nima na gyara fuska na nadaure shi da kyau nazo da sallama na, shiya dago yana amsa min tare da nuna min kujera da in zauna.
Da bissimillah na kai zaune ina mai sauraren su sai can naji ya ce kowan ku nan ina son ku bani hankalinku ku saurare ni .
Ai kai muke sauraro tace cikin kada kafan da takeyi har lokacin ta yace ina son ku sani kowa a nan auro ta nayi don mu zauna tare mu raya sunna ma,aiki SAW nidai kai kawai na iya gyadawa sai faman tunane nake mai ya kawo wanan maganan haka.
Wani hararan shi takeyi da yake wanan maganan batare da itama tayi magana ba yace Nafisa kin san dai Na sai maki motar ki akan wanan auren na Deedar kika ce baki son wanda na saya maki din kika dauki daya daga cikin wanda nake shiga ban kuma hanaki ko yi maki magana a kan hakan.
Yanzu may ya kawo wanan maganan agaban wace ba ayi da ita ba tun farko yace maganan ya shafe ta ne dole ayi shi da ita tunda haka kike so.
Yace kin san da haka ko baki sani ba tace na sani mana kuma wanan ra,ayinane haka shi nake so shiyasa na dauke ta yace good.
To akan may ita zanyi tafiya nace malam musa driver ya dinga kaita makaranta kika hana shi alhalin kin san itama din mata ta tace tana da ikon yin yadda kikayi a gidan nan.
Ta kalle shi tace eh ni na hanashi din ya kai ta don ban san da wanan maganan ba saboda baka fada min komai akan haka ba.
Kaga ke nan ina da ikon da zan hana wani yin abuda kayan ka a gidan don nice za ka tambaya akan haka idan wani abu ya faru.
Yace malam musa bai fada maki nine na saka shi yin hakan bane da kikai mashi warning akan dauka Deedar a motana.
Ina son ji idan bake bace sai in kira shi yanzu gashi nan a bakin kofa yazo ya fada muna nashi dalilin da zan sa shi abu yakiyi ko yau yabar min gidana da aikina don ba zan dauki wulkanci akan iyali na ba ga kowa.
Samad na fada maka nice na hana a fita da motar nan akan na hana matar ka shiga mota ne wai ka zaunar dani anan ina wani magana ne can na daban.
Yace wanan din naki dauke shi wani magana ba ke nan idan anyi maki hakan zakiji dadi a ranki ki fada min eh ko a, a ya tambaye ta.
Mikewa tayi tana fadin akan matar ka ta fada ma na hana ta fita a mota shine ka zaunar dani nan taga ka wullakanta ni ko may.
Yace baki son gaskiya ke dama do baki san shi ba to bari kuji dukkan ku abina abina nane idan ban ma kowa shamaki da abina daga yau kada wata ta kara yiwa yar uwar ta shamaki dashi.
Dama ai arzikin ta biyo taci ba kuma zataci komai ba daga gare ka sai dan karen wahala kafin ta kara gaba munafuka har kin iya shigewa daki da miji kiyi gulman wani dashi jin dasin may kika samu a gurin shi.
Zagin ne naji yai min yawa har na kasa daure don karshe cewa tayi dole in fita in bar mata gidanta in koma wurin matsayitan iyayyena makwadaita.
Dani dake waya fi tsiya Nafisa ai yanzu ba sai an bincika wanda yafi wani talauci ba anan don ke mai arzikin ne da baki fada ba wallahi.
Ko mutum ya shigo gidan ba sai ya tambaya don ku yunwa ya koro dake da yan uwan ki kuka samu wurin lebewa ki bari kiyi prouding da abinda kika ne ma da kan ki ba abin miji na kowa ba.
Sannan da kike fadi sai na bar gidan nan ki tuna ke ba Allah bace ba kuma kowa kike ba da kin isa ko shigowa ma gidan banyi balle in zauna kina gani na kuma baki da abinda zaki min.
In har kin ga na bar gidan nan sai dai gawa na wallahi amma badon ke da sherin ki ba don kunyi min kadan dake da duk da abinda kike takama a gidan.
Karya kike kema kin san nafi karfiki wallahi don banga abinda zan tsaya ma fada ba nan nace balle ni da banga abinda zan ma kishi ba nan iliterat din banza dake sai shegen bakin karya da cika baki.
Gani fitan naso yai yawa ne yasa shi dakatar damu da tsaya tare da fadin ya isa hakana ban kira ku nan ba don kuyi min fitina na kiraku ne don in ja maku kunne.
Bayan haka zanyi tafiya gobe zuwa gida ban son in dawo in samu kunyi wani fitina a tsakanin idan haka ya faru nayi bincike ko wacece mai laifi zan hukunta ta wallahi.
Ya sa hannu a aljihun shi yana ciro kudi ya aza a saman table din gaban shi ya juya gurin ta yana fadin dauki gudu wani kallo tayi mashi tare da watsa ma kudin harara tana fadin kudin ma da zaka ban sai a gabants zaka bani kuma daidai da nata ko may yace.
Eh nayi hakane don fita daga zargin ku na mata ya kirgo wani yana mika mata tare da fadin wanan dubu goma ne kiyi wa ihisan lalura dashi kafin in dawo .
Yana fadin haka ya mike ya fara tafiya ya juyo yana fadin shike nan kuna iya tafiya bangane muna iya tafiya ba sauran jamma,a yaya kake son inyi dasu wanan matsalan ki ne yace yana tafiya cikin daga murya bayan na kwashi kudin na mike nake fadin mungode Allah umfana arziki.
Nan na barta tana ta masifa wai bai mata kara ba yarsa kawai ya sani ita dayan fa afa yai mata sai yanzu ne da aka hure mashi kunne zaice bai ma sauran lalura sai ita tayi masu ko may ?
Ni kan sai a lokacin ma nake sanin dayar yarinyar mai tsiwan ba diyar shi bace dama abin na daure min kai ina mamakin lokacin da suka haifi yar da ta kai haka girma.
Nafisa ji take kamar ta mayar mai da kudin shi gashi kuma tana bukatan kudi a hannun ta da zaitai sabon lalura ita tai girki ranan don haka sai da ta saka shi daki ta lalashe shi ya kara masu wani abu.
Washe gari tun da safe suka bar garin zuwa kd don yana son zuwa kano ya dawo kaduna a ranan shine dalilin yin sammakon su.
Wanan karon ni kadai ce a gidan tunda na dawo school ban fita koda falo ba ina part dina yau kallo na kunna ina yi tunda ba wani girki zanyi ba ranan.
Idan bai part dina bana wahal da kaina gurin girki sai dai in samu dan snack inci in kwanta jin anturo kofan dakin na kalli kofa ihisan ce ta shigo da kanta boya an tsefe ba kitso ta shigo wurina.
Nace a, a Ihisan ke ce tazo har gurina da surutun ta irin na yara fadi wanan fadi wofi muna hira yarinyar na dan debe min kewa har tayi barci a dakin kwane a jikina.
A hankali nayi dabaran kama kanta ina mata kitso kalaba nayi mata manya irin na yara don bata kwaso uwarta ba ubanta ta fi daukowa sosai ha halitta.
Kalaban yai mata kyau na mike na dauko man kitso a dakina da yan ribos na kama mata kan har lokacin bata falka daga barcin da takeyi ba.
Ashe suna can suna neman yarinyar a falo dakuna har wajen gidan basu ganta ba hankalin su ya tashi sosai har suka buga ma uwar waye ta baro inda take zuwa gida hankali tashe.
Tun a hanya ta kira AA tana fada mashi batan yarinyar shima hankalin shi ya tashi sosai sai fama buge bugen waya yake a duba yarinyar wurare da dama.
Yusuf da yaga yadda duk ya firgice gashi suna garin kano yamma yai masu basu gama abinda ya kaisu garin ba shima ya shiga damuwar batan yarinyar sosai.
Yusuf din ne yace khadija ko tasan abinda ake ciki a gidan naji bata bugo maka waya ba sai lokacin ya tuna ya kira layina.
Hankali a tashe yana fadin kina ina nace gida yace bakiji ihisan ta bace ba ne baki bugo min ba nace kamar yaya ta bace ga ihisan a gurina tayi barci tun Four muke dakin nan da ita fa.
Ajiyan zuciya naji ya sauke ya ja tsuki yana fadin kaji fa ashe tana part din Deedar tana barci tun karfe hudu mahaukatan baza basu duba ba sunce sun duba ko ina a gidan kuma.
Kiran uwar yayi yana fada mata yarinyar na nan gurina tana barci suje su dauke ta tace may uban wa yace ta daukar min yarinya.
Idan tai mata wani sheri fa wani irin magana kike fada Nafisa sherin may zatai mata kuma Deedar fa nace maki ta gidana.
Tsuki taja ta kashe wayan tana isa gidan part dina tayo direct ba sallama ta banko kofan dakin idon ta akan yarinyar dake barci saman kujera.
Direct wurin yarinyar ta nufa ta dago ta tare da fadin uban wa yace ki dauko min diya wani sheri kika kawo tanan ki na mata yar bakin ciki, yar nawa guda daya da Allah ya bani itama neman ta kike da sheri ko may.
Idan haihuwa banza ne ki haifi naki mana ki dinga kallo idan kina son yara a dakin ki daga yau kada ki sake taba min yarinya a gidan idan ba haka ba ranki zai baci kin aza haka ake samun haihuwa a ruwa ko may ke da haihuwa ai sai daki kalla in kin ce naci kika iya.
Ban iya mata magana ba sai kallon ta da nakeyi ina mamakin wanan haukan nata ta dauko yarinyar da karfi tana dube dube a jikin kamar may neman wani abu.
Har takai kofa fita da yarinyar a sabale saman kafadan ta ta juyo tana fadin kuma bari kiji idan wani abu ya samu ya ta nan da sati daya wallahi sai mun shiga kotu dake.
Baki da hankali nace mata kina tunanen kowa ma irin ki ne muguwa ke kika san wanan zancen ni ban san shi yar ki ta kawo kanta inda nake bani na dauko taba kuma ko gobe tazo wuri na bazan koreta ba don ni ba mahaukaciya bace irin ki.
Kije ki mutu ranan don tazo wurin makiyiyar ki, don Allah fice min da haukan ki na banza mara dalili ki sa ido ki gani idan na shiga harkan yar ki in dai ba ita tazo inda nake .
Tace zaki gane baki da wayo duk ranan da wani abu ya samu ya ta, wama ya sani ko saceta kikai niyar ki yi Allah ya tona maki asiri kika fito da ita.
Har ta fita mamakin kishi irin na Nafisa mai kama da kishin hauka nakeyi yanzu may na yarinya a cikin kishin mu bafa ni na dauko ta itace ta kawo kanta inda nake.
Idona na lumshe maganganun ta suna min zafi a rai na nace ya Allah kana gani kuma kana jin Allah kai min mafita akan wanan aure.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Bayan sun dawo daga kano Yusuf ne dauke da kaya niki niki zai shiga gida dashi ya bishi da kallo tare da fadin wanan kaysn kuma haka daga ina suke.
Yusuf din yace dashi sako ne aka bani inzo ma mutanen gidan dashi bishin ya sake yi da kallo yana mamakin ida kayan suka fito sai dai bayi magana ba suka shiga.
Bayan sun gaisa da Fati ne Yusuf din ya mika mata leda tare da fadin wanan khadijja ce tace azo ma su AFFAN dashi wai akwai wani leda a ciki naki ne tanaa gaida ku.
Dagaa inda take zaune ta tace tauuu, ta mika hannu ta karbi kayan tare an gode kallon mamaki ne a fuskan AA ddin karara sai kuma baiyi magana ba ya basar.
Ba wani sako bane a ciki sai takalman makaranta da school baga har da littafai da warmers na makarantan yara masu kyau.
Tun a gaban su ta bude kayan tana kallo murmushin da ta sake a fuuskan tane ya bashi mamaki tace to ashe monday akwai rigima wurin babana sai nayi wa kayan sheda.
Taci gaba da bude dayan ledan turararuka ne a cikin na jiki humra dana daki masu kamashi sosai don ana bude su falon ya dauki kamshi.
Allah yasa ai amfani dashi AA ya fada yana mai tabe baki tare da komawa saman kujera yayi balancen da kyau.
Malam bafa kai ka sayo su ba balle kace wani abu yar kanwar tace ta aiko mata da tsara ta shafa.
Rai fati ta hade da sauri saboda akwai ta da saurin yin fushi da mutum, don haka yana fadin wanan magana ta fuske, dashi ba tare da tayi magana ba.
Yaran ne suka dawo daga gidan mahaifan shi suna ganin shi suka dan zabura don jin dadin gani shi komay suka tuna kuma sai suka ja suka tsaya suna fadin sannu da zuwa Abba.
Kamar yadda ya saba yi da yaran cikin rashin sakewa ya amsa masu Yusuf ne yace a,a Affan an dawo ke nan sai suka nufi wurin shi idon su yana kan school bag din da suka gani a gaban uwar su.
Karamin ne ya rarafa wurin uwar yana tambayan ta cikin kashe murya yana fadin mama Abba ne ya sayo muna ?
Cikin muryan ta a yadda take magana kamar an sata yi dole tace wa yaron Anty ku ce ta sayo maku har da takalma da cooler.
Dayan yaron ma yaje gurin yana tambayan ta mama wace antyn mu ta sayo muna ?
Yusuf ya ce da yaran mommy ku amaryan Abban ku da tazo wancan karon tace a kawo maku murna yaran suka shiga yi tare da fadin mama itace tace zamu hutu Abuja ko ?
Wani tsawa ta daka ma yaron sai da ya gigice tace kai rabani da maganan banza don Allah, ku magana baya isan ku .
Kallon ta mijin yayi yaga yadda ta hade fuska ya fahinci fushin maganan dayayi take yi har wanan karon zata sauke ga yaran .
Kallon yaran yayi shima cikin daure fuska tare da fadin kai ku kwashi kaya ku ku shige ciki ban son yawan surutu fon Allah.
Yaran suka shige gwanin ban tausayi tare da daukan kayan su ita bata dauki lokaci ba ta mike ta mara ma yaran baya.
Nuna ta yayi ga Yusuf yana fadin duba don Allah mutum ya zo daga tafiya ko ruwa ba zata iya bashi ba wai matar mutunce haka tun tasowan mu da safe fa na buga mata waya amma bai sa mu samu taro a wurin ta ba.
Yusuf gajeren murmushi kawai yayi tare da fadin ina ruwan fati ita dai bata taba canzawa haka rayuwan ta yake sai hakuri kawai irin haka.
Kai AA ya girgiza tare da fadin rashin sanin ciwon kaine yanzu ita deedar baga ta can tana hakkuri da halin Nafisa ba tasan komai fa amma bata taba nuna min hakan ko anyi mata sai dain in suyi a gaban idona.
Bata fita kurciya ne sa ba kusa ba Yusuf yace ai ba zaka hafa Fati da khadija ba don yanayin su ba daya bane matsalan ita Fati akwai saurin fushi da kowa kuma bata da sakewa.
Ya