MIJIN BUZUWA complete Hausa Novels.txt

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   41 / 144

120K to 123K   out of 431K words

Zuciyar shi a cunkushe yana jin bacin rai wanka yayi ya fito ya shirya gado ya koma ya kwanta da niyar taba aiki a laptop din shi .
Amma sai yasamu kan shi da jin kasala nan ya fara tunane abinda na fada masu yau tunane ya zurfafa dayi sosai har zuwa daukan yarinyar daje yi da yamman nan.
Ido ya lumshe yana tuna irin yanayin dayaji lokacin da muke hada jiki wurin amsan yarinyar yace a fili khadija khadija yana girgiza kai a hankali.
Bude idon shine yaga Nafisa tsaye tana mashi kallon tuhuma dakyat ta iya daga kafa zuwa wurin da yake kwance tace yaya naga yanayin ka gaba daya ya sauya ne ?
Samad ina kakai min yarinya yau wuni guda ace batai kuka ba nifa wanan abin ya daure min kai.
Gun wa kakai ta baka fada min ba yace muna gidan Yusuf da ita muna aiki shiyasa kika ga ban damu da kiran da kike min ba din tunda nasan yarinyar na wuri na.
Wani irin ajiyan zuciya ta sauke tare da zama a bakin gadon tana fadin sai yanzu hankalina ya kwanta wallahi.
Gobe da safe zan bar gidan nan zamu je gyara ma amarya gida juyowa yayi yana kallon ta tare da tambayan ta wai a wakike cikin wanan bukin ne don naga kin mayar dashi kamar bukin gidan ku .
Ga buki can za a yi a kaduna amma banji kina shirin zuwa ba sai wanan bukin da baki da wani dalili dashi kike maganan shi haka.
Tace bukin wa za ayi a kaduna din idan ma na sani bazan tafi ba wanan kai ya shafa don ni bai shafe ni ba yace haka kika ce tace kwarai kuwa.
Gyara kwanciyan shi yayi ya bata baya tace don kawai za ai bukin kannen Fati zan kwashi kafana in je don ban san ciwon kaina ba ko may ?
Mutanen da basu sona basu kauna na basuki su bude ido suji ance na mutu ba a yau din nan kake son in kusance su.
Ban son Fati ban kaunan ta da duk wani nata don su, , , enough Nafisa ya ishe ki ya isa haka baki zuwa ya isa wanan kalamin ba da Fati kikeyi ba dani kike yi don nima zurian gidan ne ko kin manta ne da hakan ?
A kusan tsatso daya muka fito da Fatin da kike aibantawa haka da yan uwan ta may Fati ta tare maki a duniyan nan da baki kaunar ta haka saboda wani bakin kishi naki can mara dalili.
Matan nan tun shigowan ki gidan nan kika dauki tsanar duniya kika dagwara mata katse shi tayi da fadin muka dai dagwara mata don bani kadai takewa abinda takeyi ba.
Yace matsalan ki daban nawa daban ko may Fati tayi min nimijin tane kuma uban diyan ta zan zauna da ita a ko wani irin hali.
Samad ni kake fada ma kai mijin Fati ne kuma uban diyan ta kake ni kake fadawa haka a gaba yace an fada maki kiyi abinda zakiyi.
Wani shuumi murmushi ta sauke tace dama maza haka kuke don kana takama da wanan dandanin da taima shine har kake ganin ta a mace take yanzu.
Kutawa tayi tafita daga dakin rai a bace ita samad zai kawo wa wani maganan wata matar shi can wai fati wai may yasa shirin ta akoda yaushe yake lalacewa ne idan tayi.
Tasan dai tanayi amma kuma maimakon yayi aiki yadda take so sai komai yazo ya lalace daga baya taki jinin fati da diyan ta a duniyan nan amma mace kamar kaska duk wanan abinda takeyi sai fatin ta dawo a rayuwan samad din.
Tana ganin taje gida tayi aiki akan kowa nashi amma kuma yanzu ta lura asiri bai cika kama samad din ba idan tayi ko tayi bai wani dadewa yana tasiri a jikin shi sai abin ya kare.
Kudi dai bata da matsalan shi ko nawane ta bukata tana samu a gurin samad din yanzu abinda tafi zargi shine mahaifiyar shi take lalata mata aikin ta don haka wanan karon da hajiya mama zata kara don na samad din mai sauki ne.
Don ko yanzu a tafin hannun ta yake don dai sai abinda tace dashi a gidan bai musa mata inba wani lokaci da yakan dan turza mata ba wai shi a dole ga namiji.
Tasha alwashin wanan karon sai taga bayan duk wani mai mata aiki ta bayan fage akan samad din zata raba shi da kowa nasa taga yarda uwan nashi zatayi.
Da haka barci ya dauke ta tana rungumay da yar diyar ta mumunan mafalkin da tayine ya falkan da ita sai gumi take hadawa a dakin duk da sanyin ac dake dakin alokacin.
Wacece wanan macen da tayi mafalki da ita samad din ta ya rike ma hannu yara na binsu a baya kodai don ta kwanta da zancen Fati ne a ranta tayi wana mafalkin haka.
Mace tare da samad din ta kaita kada tana fadin wanan ba gaskiya bane koma may ne gobe zata je wurin malamin ta a duba mata agani.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Jikina yayi sanyi sosai da kayan da naga ya sayo min musu kya dagani kasan ai kashe kudi a wurin sarkan maryam ta daga tana fadin.
Wanan kan kizo kiji kudin shi zai kai a kala dubu dari uku fa saurin kallon ta nayi nace kai haba wanan dai kila mafa fashion ne kawai.
Khadija wallahi gold ne haba baki ganin shi ko agogon nan ban debe tsamanin shi ma fashion bane nace a wani dalili zai sayo min kaya haka masu tsada bayan yasan iyayyena talkawane idan naje gida dasu may zan fada masu akan wanan kayan haka ?
Rigunan ta sake tabawa tana daga su tace wallahi ko kayan nan anan zasu kai dari biyu kila koma sufi zaune nakai ina fadin shi wani irin mutum ne da baijin wuyan kashe kudi haka ?
Maryam dariya tayi tace khadija ke nan baki san ko waye shi ba yasa kike fadin haka bafa karamin mutum bane wallahi kudi na shigo mai ta kowani hanya.
Zasu iya sai da fili daya a wuni su samu milayan dari riba bakomai bane wanan a gare su wallahi kwanaki da mijin yaya na zai sai wani fili AA akace sai ya gani ya sa mashi hannu zai iya samun filin.
To mutum da ke samun kudi haka don ya sayo wanan ai kamar ki jefa allura ne a cikin teku gare shi gashi nan muna ganin shi a banza amma mijin yayana yakai wata uku yana neman ganin shi bai samu ganin shi ba.
Da sauri nace shi din tace wallahi Allah khadija wanan AA din kuwa shine don na tambayi anty na nayi mata kwatancen shi tace shine kuwa wallahi ba karamin kudi yake dashi ba ai.
Banda abinki duk wanda kika ga ya auri buzuwa gidan shi har ta zauna haka ai ya mallaki abinda ya mallakane.
Dubi shadda da tasa ranan da gwalagwala a hannun ta da wuya ke ko shaddan nan da zaki ji kudin shi zaki sha mamaki wallahi.
Ido na lunshe na koma na kwanta ina tunane a raina gaskiya ya zama dole in raba dasu kada suzo su batani haka da itin kayan nan in zo gaba abin ya damay ni na saba da saka mai kyau in sha in kuma ci maikyau.
Ranan da banda mai bani irin wanan yaya zanyi ga iyayyena tallakawa ne lis muna neman abinda zamuci a gidan mu.
Muryan maryam ne ya dawo dani daga tunanen da nakeyi tana fadin khadija zaki iya samun fiye ma da hakan gun samari don kyauki ne ya jawo maki haka .
Don ke din baki da maraba da yan buzaye dole ne na miji ya ganki ya rude haka sai dai shi AA nashi sallon son yazo daban da na sauran maza ne.
Yace dake sona yake yi da kike fadin haka kawai dai mutunci ne a tsakanin mu kune dai dake da Yusuf kuke ganin haka din amma ni ba wani abu makamancin so daya taba hada ni dashi.
Balle yanzu nasan da wuya su kara dawowa inda nake don na fada masu mamud zan aura kuma har na gabatar dashi a garesu sun gaisa dashi dazun.
Kikayi may khadija amma wallahi baki kyauta ma kanki ba wanan wani irin cin fuskane haka kikayi masu lalle kan da wuya su dawo gurin ki kuma sai dai da yake maza ne basu fushi da abinda suke so kai tsaye.
Mun dauki lokaci muna maganan da ita har dai nagaji na kyake ta tanayi ita kadai na bata baya.

Yau da wuri muka dawo dawo daga class bamu dade irin yadda mukan dade acikin makaranta ba maryam ta rigani dawowa har na samu ta gama abinci ko.
Dafa dukan manja yaji atarudu ta hada muna sai naman datayi amfini dashi a ciki danye zaune nake ina cin don ita tace tasha tea da tadawo don maryam bata wasa da cikin ta ko kadan.
Na kusan gama cine wata Ruth Samuel ta shigo dakin tana cewa ina da bako a waje yana jirana maryam ne ta kallo ni bayan Ruth tafita daga dakin tana fadin yanzun haka mamud ne dan kadafin tsiya ya biyo ki.
Nace kada kiga laifin dan bawan Allah a banza don nagane ke son wanda baisan kinayi ba kike yi yasa kike ganin laifin mamud din.
Hijjab dina karami na dauka ina sawa nake maganan na fita waje ban jira may zatace ba kada ta bata min rai.
A zatona mamud din ne yazo amma ina fita sai banga motar shi ba a wurin fitowa Yusuf yayi daga cikin motar da yazo da ita yana min hannu.
Zuwan Yusuf din ya bani mamaki matuka don banyi zaton zasu kara dawowa inda nake ba kuma .
Na iso inda yake tare da sallama yanayin shi kawai ya nuna min bai cikin dadin rai a lokacin yace ya karatu nace Alhamdullahi.
Shirune ya dan biyo baya sai ido daya kura min yace dama nazo ne neman alfarma a gurin ki idan zaki iya yi min .
Da sauri nace in zan iya may zai hana in maka tunda har kataso kazo gare ni a wanan lokacin haka.
Ajiyan zuciya ya sauke yace ina son ki shiga ki shirya yanzu ki fito in kai ki asibiti ki gaida Abdulsamad ne yau kwanan shi biyu kwance bai da lafiya ya dawo da ciwon ciki sosai tunda ya dawo.
Subbahanallahi na fada mace ciwon ciki kuma kodai yaci wani abin ne baku sani ba yace ciki da kai yake fadin yana mai ciwo tun kwana biyu da dawowan shi waje.
Ko ranan da muka zo wurin ki cikin karfin hali nasa shi muka zo ke kuma sai kika bata muna rai da dan banufen ki.
Murmushi nayi nace kuka dai bata ranku ga banza amma ni ban bata maku raiba gaskiya yace kin ko san kishin maza yafi na mata khadija ?
Kishi akan may zaiyi kishi kuma don dan wanan magana kawai yace wallahi ba don nasan Abdul tun farko baida lafiya ba da sai in ce har da maganar dan banufen nan ya sashi ciwo haka.
Sai dai bai karamin magana ba tun wanan lokacin a kan ki yanzu ma ni naga dacewan haka nazo daukan ki muje ki duba shi don Allah.
Nace gaskiya ba zan iya zuwa ba da sauri yace khadija kada muyi haka dake mana na dauka zan iya saki abu kiyi don ni koma badon niba ai yaci kije ki gaida Abdulsamad din tunda akwai mutunci.
Kai na girgiza tare da fadin Allah dai ya bashi lafiya amma ni ba zan tafi ba idan ma naje matar shi ta ganni may kake son in fada mata kuma don komai tamun tana da gaskiyan ta.
Balle ma bazaku hadu ba don ita tana gida bata faye zuwa ba sai sa a mommy ce dai a gurin nashi take jinyan shi.
Ko zan tafi bani kadai zan tafi ba sai inda maryam na fada yace gaskiya ne hakan yana da kyau ai wallahi ni ma kin ga na rude ban ko kawo haka ga raina ba sai yanzu.
Don Allah ki daure kizo muje khadija yin hakan yana da kyau sosai wallahi ciki na koma na fadama maryan zuwan Yusuf din tace muje don Allah ki duba shi gaisuwa ai ladane gare shi so sai.
Mun shirya ba laifi don zakace ba asibiti zamu tafi ba don maryam ne ta saka in shirya haka don kada muje mu hadu da buzuwa a can ta raina muna wayo.
Nace in sha Allahu ma baza mu hadu ba har mu dawo muka fito muka kama hanya ina gaba tare dashi maryam na zaune a baya.
Yusuf ya kawar da shirun da motar yayi a lokacin yace nasan zaiyi mamakin ganin ku yau saidai don Allah ki tuna a wani hali yake yanzu.
Nan dai ma banyi magana ba sai murmushin da na danyi kawai yace maryam khadija ta fada maki abinda tayi muna ranan ko ?
Wallahi ta fada min bata kyauta ba ai nayi mata magana kasan tayi nisa yanzu ga son dan banufen nan bata jin kira sai ta kai.
Da sauri yace ehyehh tayi nisa fa kikace har ya shiga gidane bamu sani ba komay ?
Amma khadija idan kin muna haka baki kyauta muna ba wallahi yaya zaki yi da abokina kuma idan kika fitar da wanan mamud din ?
Nace Allah kadai yasan wa zan aura yanzu da kuke wanan magana niko mamud din ina shakku a gare shi ne don ban faye son mutum mai mata ba a rayuwana .
Murmusgi Yusuf yayi yana kada kanshi yace yanzu dai kikai magana dama nayi zaton don ki musguna na munane kikai hakan.
Nace a a wallahi ni gaskiya na na fada maku har cikin raina bandai son mai mata ne a rayuwana yasa nike shakkan shi.
Tsaya yayi ya sayo kayan dubiya asibiti ya dawo ya shiga motar muka tafi dan jefi jefi yake dan jan mu da magana har muka kai inda zamu.
Motar ta shiga cikin Turkeys hospital ya samu wuri ya faka muka fito zuwa cikin dakin da aka kwantar dashi wurin tsit yake baka cewa akwai mutane saboda natsuwan da wurin ke dashi.
Da sallama muka shiga dakin yana gaba muna bayan shi biye har zuwa cikin dakin yana kwance rai,rai ya doran hannun shi daya saman goshin mommy tana zaune gefe saman kujera tana duban wayan hannun ta.
Sallaman mu yasa ta dago kan ta tana amsa muna tare da zuba muna idanu don bata sheda ko suwaye tafe don maryam ce ke bin Yusuf din.
Sannun ku da zuwa tace muka amsa da sannu mommy muna gaida ita sai can tace khadija kune tafe kun san baida lafiya ne ashe , ?
Yusuf ya karba da fadin wallahi sunji mommy yanzu na gansu shigowa nan din na karaso dasu ya mai jiki nace da mommy .
Mai jiki gashi nan yaji sauki yau ai mun ga hankalin shi jiya kan da muka zo abin ai ba dama wallahi.
Maida hannkali na nayi inda yake kwance yana saye da wandon three quarter fari sai yar riga irin na shan iskan maza din nan mara hannu amma rigar na da kauri blue colour.
Ya jikin nace a cikin wani irin murya mai taushi da sanyin jiki tare da dan kura mai manyan idanuwa na a hankali ya sauke hannun shi saman kan shi yace da sauki.
Shirune ya biyo dakin na dan wani lokaci Yusuf ne ya karaso zuwa bakin gadon suna magana dashi wanda ba lalai ne mu jisu ba.
Ledan da muka shigo dashi ya mika wa mommy yana fadin mu muka zo dashi tace kai khadija ina laifin zuwan da kukayi ke da ke makaranta kikaje yin wani dawainiya kuma haka ?
Tana nuna mashi daga inda yake kwance tare da fadin kako gane ta yarinyar nan ne kawar su Binta da suka kwana wurin ta kawar matan officer na layin mu.
Murmushi yayi mata kawai ba tare da yace komai ba muna nan tsaye jin yace yace Deedar akwai ayaba ki bare min in ci kai na gyada mai ba tare da nasan ko akwaishi ba.
Na bude ledan ina ciro ayaba daga ciki na fara barewa na miko mai tashi yayi zaine ya dan jingina jikin shi da filo ina mika mai a hankali yana karba dakin yayi tsit a lokacin.
Kofan aka turo wasu mata ne suka shigo dakin hamshakai dasu idon su caraf a kaina a yadda nake tsaye wurin kan shi ina bare mai ayaban ina bashi yana ci ko mommy ido ta zuba muna tana kallon mu sai take gani kamar da can musan junane ko kuma namu daine yazo daya bata sani ba.
Shigowan matan ya dauke mata hankali ga barin kallon mu ta maida hankalin ta gare su suna gaisawa dasu.
Kun fara jerabawa ne ko da saura ya tambaye ni mutum ba zai iya fahintar abinda yake fadi ba saini dake kusa nake jin shi nima a hankali na mayar mashi da amsa da cewa next week zamu fara insha Allah.
A yadda muke magana zaka dauka wani magana mai

41 / 144

Chapters