zai tafi da kwalban a bincika masa ko na maye a ciki muna shiga falon akwai wani carpet wuri hawa step din saman AA nan ma nace wa laraba ban yarda da gurin ba.
Ta sake kiran maigadin ya shigo suka daga yace akwai rami bayan daken din ya tona saida naji tsoro nan ma wani abune an cacaka mai allurai sunfi a kirga aka bine.
Maigadin yace wanan matar takai shuuma wallahi sai ya cire abu har gurin kofan ta ya fita dashi gidan haka na wuni sukuku a gidan.
Sai AA ya kwashe kwana shidda a Niger bai dawo ba ya kama jumma tunda maryam ta sauke ni na shiga gida tace zata shigo da dare ta kawo min sako dana bata tazo mun dade muna hira ta wuce.
Washe gari har mun rufe gida akai ta bugawa muka bude AA ne ya dawo a cikin dare nidai ina dakin ban fito ba sai gashi ya shigo ba laifi nayi mai sannu da zuwa da tambayan mai jiki.
Yace da sauki tare da tambayana lafiya ta nace Alhamdullahi haka muke zaune a gidan ba wani sakin fuska a tare dani sai wani rawan kai da yake min ban kula ba don nasan don matar bata nan ne.
Sai da ta share sati biyu ta dawo da yamma ina jin hayaniyar su nasan ta dawo ke nan sai ga ihisan ta shigo min har part dina.
Ban fita taron ta ba tunda da zasu tafi bata sallamay ni ba ita ma na gama abinci na kai mai muna zaune sai gata ta shigo part din shi da kayan dake jikinta data dawo dashi wani shadda ne blue yasha aiki da zare yellow.
Abinci yake ci ina zaune a gefen shi ina game da waya na ta shigo ta samu wuri ta zauna can naji tace ke ban dago ba don kiran rainin da tayi min ta sake fadin dake nake magana fa.
Nace ki je gun yaysn da kika haifa ki magana dasu hakana ba dai ni khadija ba tace kin san abinda kika yi ai nace ko da ban sani ba na sani din don nasan ba alheri bane ya kawo ki nan yanzu.
Tace amma dai kin san na dawo yau ko may zaisa ki kawo masa abincin ki kuma nace kin duba lokacin da kika dawo ko ko tsoron ki zanji in canza lokaci in bar maki shi.
Table din ta buga da hannu ta saida kayan sama suka girgiza tace wallahi kinyi kadan ke baki isa ba wallahi nace isar ke nan kikaga haka ke wacece da za a ji tsoron ki wai.
Ya dago rai bace yace mata Nafisa bar nan tun kan na bata maki rai ina mun gama wana maganan tun dazu tace wallahi ba zata bari ba don ita zatai girki tunda ta dawo yau.
Yace sai kiyi mu gani tunda jidali kika dawo dashi ke wata irin mace ce da bata da godiyan Allah kwana nawa ina can tare dake bata bata ranta ba kan haka yanzun ma kin dawo din ba zaki bari a zauna lafiya ba .
Nidai ban sake kula ta ba nan suka gama sa insa din su har ta gaji ta fice tunda na kwanta ban motasa ba shima bai nemay ni ba nasan yana cike da bacin rai ne.
Tunda na koma part dina banjin dadi don haka na samu guri na kwanta can cikin barcin da na dan samu ya dauke ni naji mara na ya yanka min.
Tun ina ji kamar mafalki nake har yakai na bude idona na dan saurare sai ya dan lafa min na sake rufe idona sai kuma ya dan kara cunkula na na bude ido ciwo sosai yake min dabaran kiran maryam nayi a waya .
Sai dai wayan ta yana busy naja tsuki na wurgar da wayan ga maran yana addabata da ciwo irin wanda ban taba jin sa ba.
A hankali na mike zaune daidai lokacin da naji ya lafa min din na sauko na nufi falo in duba laraba na samu laraba din ta fita bata nan cikin part din kitchen na nufa don in duba kanwa na daiga kanwar najika na nufo falo sai naji kafata ya rike min lokacin laraba ta shigo dauke da kayan wanki a hannun ta .
Tana ganina tace subbahanallahi uwar dakina lafiya dai ko nace mama marata ke min ciwo yanzun kuma kafata ya rike min sosai ban iya dagawa.
Tace ubangiji ya sauke ki lafiya ko in fada ma Alhaji don na barshi a waje yanzu kaina girgiza mata na samu kafan ya sake min na karaso gurin kujera na zauna cikin karfin hali.
Na dauki kanwar nasha ina aje cup din yana shigowa falon kallon yanayina yayi ya fahinci banjin dadi yace lafiya kike kuwa Deedar ga AC kuma kina zufa haka.
Na goge zufan cikin karfin hali nace haka na yake min kwanan nan cikin ya kara murda min na nade wuri daya yace nace baki da lafiya ko muje asibitii ne na girgiza kai nace ba komai ai zai bari.
Yadan dade tsaye a kaina yana kallona ya juya fita daga dakin da kyar na samu na daga zuwa dakina laraba tana tsaye ta kallona har na shige maryam na samu tana kirana da kyar na daga wayan nace maryam kizo da saurin don Allah cikin wani irin murya mai ban tausyi.
Tace haihuwa ne ko may khady nace nima ban sani ba ki dai zo don Allah tace gata zuwa yanzu ta kashe wayan.
Ya lafa min ya taso ba a dauki lokaci ba sai ga maryam ta shigo ta samay ni ina yarfar da hannu ta iso gurin a rude tana fadin haihuwar ne khady ban sani ba maryam ko shine yazo wani irin ciwon mara dai nake ji maryam.
Can ya yanka min nace wayo maryam zan mutu wallahi ta rude tace barin in kira mama kila tasan haihuwa ita laraba na shigowa dakin tana kallon yanayina tace wanan kan haihuwa ne sai dai kila da sauran lokaci.
Waya maryam ta dauka tra kira anty Hauwa tai mata bayani tace bari ta turo sister Larai ta dubani ba ajima ba aka kira maryam ta dauki waya sai ta fita.
Tare suka shigo da matar da aka kira da sister larai din tana zuwa tace in kwanta ta dubani tana dubawa tace haihuwa ne yazo sosai a dan ban tea ko kunu in sha don ba a so nakuda da yunwa.
Da sauri laraba ta hado min tea mai zafi ta kawo na karba na sha da kyat do ni ba gwanan shan tea bace na sha na dire cup din kasa ina kallo sister din ta gyara guri a dakin leda ta shinfida sabo da ta bare shi a gaban mu.
Tace su dan fita daga falo su jira mu ta hada allurai tayi min cikin ikon Allah tana min alluran kamar ta jawo nakudan kusa ne na koma ba zama ba tsayi.
Maryam ta kira tana tambayan ta akwai leda a kusa yadda maryam taga ina cije baki itama ta fara kamar mai nakudan tace don Allah fita wanan rakin ki har yafi na mai nakudan gaskiya ai.
Da ya wani taso min tace kwanta kwata da sauri da taimakon ta na nisa da karfi tana kiran oya push pushi niko Allah nake kira a bakina.
AA yana shigowa falon don ya dubani a yarda ya barni kuka yaro yana gauraye falon yaja ya tsaya yana kallon maryam data rude sai kuma ya nufi kuryan dakin ya daga labulen dakin .
Don ya tabbatar maryam na fadin Alhamdullahi ta haihu ta hau murna laraba ma sai hamdala take zubawa a gurin da mamaki ya sake labulen dakin yana fadin dama haihuwa zatayi ne mama tace eh Alhaji.
Haihuwar ce tazo da sauki wallahi kiran ds ka kwala wa maryam daga ciki ta shigo da sauri dakin tace karbi yaron miko min wani zani again jikins rawq ta bude wardrobe dina ta dauko zani.
Tana mika wa ta fito yana tsaye ya kasa zama a dakin ta mikawa laraba yaron mai matukar kama da uban sa sai dai shi farine sol yafi uban fari.
Mikewa yayi da sauri ya karaso wurin laraba kamar zai karbi yaron Laraba tace bari a goge shi Alhaji.
Yace to to mama ikon Allah haka abin yazo da sauki kuma ikon Allah sai hamdala yake zubawa ban dauki lokaci ba macen ta fito sai kuka take zuba har yafi na namijin kamar yai tsuntsuwa ya fada dakin yace wani again ?
Kafin wani lokaci matar da yake aikin su ne ta saba ta ta gyara yarinyar ta aza saman gado ta kwala wa maryam kira ta shigo tace dauki baby girl din ki bamu wuri.
AA kan kasa hakkuri yayi sai da ya karbi yaran tun ba ai masu wanka ba yai masu addu a ya fito ya bari ana gyara muna jiki.
Direct wurin Nafisa ya nufa yana washe baki yace ki min murna mata na ta haihu yanzu tace may kace yace nace Khadija ta haihu yanzu ta zabura ta mike tsaye tare da fadin ina yace a dakin ta mana.
Kana gidan nan ta haihu Samad yace yanzun na shiga in dubata na samu ta haihu tace nashigs uku ya zaro ido yace haihuwan kika shiga uku ko may ?
Hannun ta yana saman kirjin ta tace ka barni don Allah da abinda ya samay ni a gidan nan can kuma tace may aka samu yace mace da namiji ta zube saman kujera kamar ba kashi a jikin ta jagwab
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Daga inda yake tsaye a gurin ya buga ma mommy waya yana sanar da ita zancen haihuwan sai yusuf da ya kira tare da kiran mahaifana ya sheda masu.
Tana zaune ta zuba mai ido tana sauraren abinda yake fadi a cikin murna tun tana sheda shi har ta dinga ganin ya koma mata wani abin,ki a zuciyar ta.
Jirin da take jine yasata dafe kanta da hannun ta daya sai rintse idanuwanta da tayi tana jin shi sama sama yana farin ciki.
Fitowan laraba part dina yasa ta bude ido ta sauke kanta tana fatan raba tace ai yaran sun mutu ko sai taji laraba na fadin Alhaji matar data karbi haihu tana bukatan ganin ka.
Yana cikin fara,a yake fadin to, to mama gani nan zuwa ya dakatar da wayan da yakeyi suna zaune tare da bakin da tazo dasu sai yanyala da itama hankalin ta a tashe yake wurin.
Yana barin gurin ta kalli yan uwan nata a cikin yare take magana rai bace tana fadin shike nan ta kara min asiraina dana binne a gidan nan .
Dayar tace asiri kika birni Addah tunawa da wace take maganar ko wacece ta ja tsuki tayi daki yanyala ta mike ta bi bayan ta zuwa dakin.
Samun ta tayi tana safa da marwa a tsakiyar dakin tare da dan bubuga dundun hannuta wani saman wani tana jin motsiyan yanyala ta juya da sauri tana kallon kofan.
Yanyala wanan yarinyar ta gama dani a gidan nan an fada min kada in yarda a zubar da jinin haihuwa a gidan don komai da nasha wahalan nema na girka kaina zai lalace yanzu ga wanan banzan tazo ta haihu min a cikin gida na shiga uku ban san ta ina zan fara ba kai na ya daure da yawa yanyala.
Yanyala tace madam ya kamata a kira tun lokacin bai kure ba muji shawaran ta don ba abinda za aiwa sanyin jiki bane.
Kira biyu madam ta dauki wayan ta fara mata kirari tana fadin sai ke manyan mata a gidan Abdulsamad ba wata bayan ke a gidan nan.
Madam yau ba wanan a gare ni madam kashina ya bushe a garin nan yarinyar nan ta gama dani a gidan nan.
Cikin tsoro madam ke tambayan may ya faru kuma wani abin tai maki daga dawowanki jiyan nan tace madam yarinyar na shu,umace ta haihu min a cikin gida madam ta kara min duk wani abu danake tunkaho dashi a gidan nan na kwarai.
Ta haihu madam tace hankali tashe tana tambayan Nafisan tace gashi na fada maki kinji wallahi ta haihu ko minti talatin ba a yiba.
Cikin rudewa madam tace gani nan zuwa yanzu ki jirani don Allah ki natsu Nafisa har in zo musan abinyi tace ina jiran ki ai ban iya komai saura kiris in fasa ihu Allah ya kare ni.
Koda ya shiga dakin ya samu na shiga wanka muna ciki da nurse din data karbi haihuwan nawa jin shigowan shi maryam tai mata magana gashi ya shigo sai ta fito daga bayin ta barni a ciki.
Takardan da ta rubuta magani ta dauka ta mika mai tana sharce zufan da tayi na wahala tare da fadin wanan nake son a sawo min zan mata ne ta dan samu saukin tsamin da jikin ta yayi sai dana gyara jikina na fito daga bayin ta shiga gyara yaran wankan farko tayi masu ta kawo zaitun ta goge jikin su dashi kafin ta kara masu wanka na biyu sai ihu suke calarawa.
Daga inda nake ina shafa mai ina mamaki a raina wai nice na haihu haka yau na dandani abinda ake fadi gamay da haihu.
Wai cikin suna fadin abin yazo min da sauki ke nan gaskiya nagaida mata a gaisheku iyayyen gida don dai kune gidan.
Komai ya kamala sai wani irin barci da nake ji yasa na kwanta nurse din nan ba karamin kokari tayi min ba sai data gyara ni ta gyara yara ta dawo kan daki laraba na fadin ta bari ta gyara tace aikin ta take yi ai.
Mahaifa ne suke muhawaran inda za a rufe maryam da laraba ke kuskus din rufewa inda buzuwa ba zata gani ba don tana iya wani sheri dashi.
Laraba ne tace bari taiwa sabo security magana taji nan ta fita gurin su ya tare ta yana washe baki tare da fadin ashe uwar dakin mu ta sauka yanzu maigida ke fada muna wanan abin farin cikin daya samay mu yau .
Ta gaya mai abinda take bukata dashi yace akwai ko yadda za ayi sosai ma nan ya nuna mata bayan gidan engine din wutan gida na stand by yace yasan yarda zaiyi ta fita tazo mai dashi ya faki idon mutane ya nufi gurin ya rufe ya mayar da kasa kamar ba a taba gurin ba da farko.
Madam ne tsaye tana rike haba tana tafa hannayen ta tace ai rudewa ya kasa barin in tambaya mai shegiya ta dire mai nasan itama bazai wuce mace ba tunda an fada muna sannan yaya halittan yarinyar yazo ?
Daga inda Yanyala take zaune take fadin biyu fa ta haifa madam data dafe kirji sai da takai zaune bata sani ba tace tagwaye matane zallah ko?
Mace da namiji naji yana bugawa iyayyen sa kaita fara girgizawa tana fadin shike nan ko a yanzun ta ci galaban mu gurin wanan.
Madam shine damuwa ji irin kudin dana narka wurin cikin yarinyar nan kan in haifi namiji kowa kuma na fada min namiji ne a ciki na ashe shegiyar yarinyar nan ta sa an musaya mata da dana.
Yanzu abinda nake son ki dashi ki kwantar da hankalin ki ina wanan abinda na dutse ya bayar tace yana nan tace gobe idan Allah ya kaimu zan shigo sai mu amfani dashi.
Bar yan iska ba suna murnan an haifi namiji da mace ba to sai mun lalata ruyuwan yaran su koma dolaye ko sakarkaru sai muga yadda za ayi kuma.
Ajiyan zuciya Nafisa ta sauke tana fadin sai yanzu hankali na ya kwanta don da har na mance da zancen maganin nan.
Yanzu ko har naji sanyi a raina shegiya sai ta kare rayuwanta wurin yawon neman magani wa yaran bata gane komai ba.
Don Allah madam kada ki wuce goben baki shigo ba don kin san ka,idan maganin an haihu gari ya waye ne kowa ya gama ganin lafiyayyen da sai aga ya sauya daga baya kuma.
Karki damu badon yau munyi da hornarable zai shigo ba ai da anan ma zan kwana wallahi tace ke dai da wanan hornor din naki mutu karaba ke nan.
Tana mikewa tace ya za, ayi da tsohon zuma ake magani abu tun muna da jajayen sawo idan da ban gama da dan baza ba da yanzu bai dade da gudu ba ya barni tunda yaci moriyar ganga ya samu rabon shi suka tafa.
Ina kwance barci nake ji saidai ban iya yiba a lokacin don yadda nake jin jikina wani kala inayi ina shafa cikina tare da tuno abinda ya wuce dan awanin da suka shige.
Muryan AA ne dakin yana fadin wanan ne maganin don yace akwai wanda babu sunan sa sai dai akwai irin shi kudin su daya da wancan din.
Ta karba ta duba tare da fadin sune inda nake kwance ya dan kalla yana fadin barci take ne ?
Sai lokacin na motsa tun shigowan shi dakin ya karaso bakin gadon yana mai kura min ido kaina na sada kasa don na kasa jure kallon da yake