MIJIN BUZUWA complete Hausa Novels.txt

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   83 / 144

246K to 249K   out of 431K words

yace ta koma tayi sallama kafin fa shigo.
Ta koma baya sai taiyi sallama ta shigo tace maman su na kirnshi a falo yace yaji koda ta fita ya dan dade zaune a gurin yai waya yana bada sakon abinda za a sawo mai yaci.
Ya mike tare da fadin ina zuwa yana fitowa ya samay ta tacika fam tana jiran shi a gaban yan uwanta ta haushi da fada.
Akan may zai tafi dakina bayan banice da girki ba ita bata son cin amana don an raina mata zai zo gabanta gaban kowa ya shige dakina ya zauna.
Nafisa wai may kika dauki kanki bazan shiga dakin matana ba don kina zaune ko may ina mutanen da kike fadi a gaban su na shige.
Take taji zafin zancen shi don wata ita da yan uwanta ya raina ma hankali yake fadin ina mutanen da zaiji nauyin su.
Tace to barin fada maka in ma mayaudariyar bata fada ma yau nice da girki a gidan nan kaima ka sani don haka banga dalikin shiga dakin ta ba yanzu.
Wai ke kina da hankali kuwa banda shi kamar yadda ke kirana kullun mara hankali sai kai min yace ta yaya za a sallamo ki daga asibiti yau kan lalura kuma likita ya fada maki dokokin da zaki tsare kice wai zakiyi wani girki can a gidan nan.
Dama nasan hada baki kayi da likita ya fada min haka don ka samu damar kebewa da matar ka kun mai dani bi can ko ?
Idan mun hada baki da likita ya fada maki haka hada baki nayi dashi jini ya zubo maki sai tace mai waya sani ma ko hakanen.
Wai kaima baka da zuciya ne may kake tsunta wurin wanan yarinyar daka rasa a wurina bada taya ka kwanan banza da takeyi kullun.
Amma banga laifin ka ba don kayi haka tunda dole ka rarashe ta kada asirin ka ya tono ta gane kai mace ne a gurin ta.
Yace eh lallai Nafisa na yarda yau tunda kin fada da bakin ki ashe kin san sherin da kikayi a haka tace banyi komai ba amma nasan hakane ma.
Idan taya ni kwana takeyi ya zama laifi ne tayi kokari tunda tasan hakkina a kanta ta taimaka min.
Yau dai ba inda zaka tafi ta rike taimakonta an yafe don mai abu ta dawo yanzu ke don Allah ban iya shirmay ki kullun fada a kan abu daya.
Yarinyar nan bata ko san kina wanan haukan ba don ita tana da hankali tafiki kaifin tunane tace don ta fini iya kissa ba.
Ciki dai ne tare dakai mukayi kuma tare zamu raine shi a gidan nan kaji na fada ma ga inda iyalin ka suke suna bukatan taimakon ka zaka shige wurin mara moriya.
Juyawa yayu ya wuce ya barta na baiyi nisa ga tafiyan shi ba mai sakon shi yayi sallama dauke da sako a hannun sa ya karba ya aje masu leda daya ya wuce da sauran part dina.
Bata fasa fada ba dashi tana saman bakin ta yashi ya mika mun keda yana fadin gyara min daya in ci .
Yanzun dai kaima kaji dai da kunnen ka ji da kunnuwan ka abinda nake fada ma yanzu waya ta buga mai yai ta ringing yaji dauka sai cin naman shi yake yi ya kyale wayan yana ta ruri a gefen shi.

ZAINAN IDRIS MAKAWA
SEENABu
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Ni dai suna cikin rikicin su n rufo kofan part dina na barsu can suna yi barci nayi ranan sosai saboda dan nauyin mutane dana sha kwana biyu.
Ban samu zuwa gidan anty hauwa ba sai da aka kwana hudu don jigilan karatu da nake fama dashi gashi yanzu girki da nawa da ba nawa ba duk ya zama min dole inyi saboda a part dina yake cin abinci.
Duk da Nafisa tana zaune a gida tana bedrest amma haka bai hanata aiwatar da sherin ta na sheri kamar yadda ta saba akan maigidan da ni.
Burin ta kullun shine ta wayi gari taga ta daina gani na acikin gidan gz baki daya don haka ne kawai take gani samun kwanciyan hankalin ta da ta rasa.
Yanyala ta isa lafiya a cikin kwana biyu da tayi a gida mai ma nafisa aiki ya gama hada masu surukulen da zai bata ta kawo wa Nafisa din inda ya jadda mata zasu ga haske sosai ga aikin su .
Bata kara kwana kauyen ba ta shigo mota ta juyo Nigeria cike da gajiya da bautar uwar gijiyan nata.
Bata iso abuja ba sai washe gari bayan ta sha bakar wahala a hanya ta iso gidan a gajiye da ita.
Ina kofar gida na shirya zan tafi gidan anty hauwa naga isowar ta alaman rashin gaskiya karara a tare da ita nikan kallo daya nai mata naji gabana ya fadi.
Lah, illaha illah, anta subbahanaka inni kuntun minal zalumin, na fadi.
Ta gwautani kamar mara gaskiya da ita ta shige na bita da kallo ta gefen ido sai kamay kamay take yi.
Driver yana jirana mu tafi na bude mota na shiga har mun danyi nisa da gida sai na tuna ban dauki tsaraban da na sayawa anty hauwa ba.
Nace ya juya nayi mantuwa a gidan ya juya kan motar muka koma gida na fita don in dauko tsaraban.
Suna falo zaune yadda na barsu sai yanyala dake ta fitar da maganunuwa daga cikin jakka ta tana ma nafisa baya su .
Daidai ta daga wani farin kwalba da ruwa a ciki sa fari tana mika ma Nafisan na shigo falon gaba dayan su sai da suka razana da ganina a wanan lokacin.
Ban bi ta kan su ba na bude part dina na shiga na dauki abin da zan dauka na fito ina rufe kofan ina karanta addunan neman tsari da kariya a wurin Allah.
Na sake ficewa ba tare da na kula suba na samu driver muka wuce har lokacin gaba na bai bar faduwa ba har muka isa gidan anty hauwa da ba wani nisa don a unguwa daya muke dasu sai dai akwai dan jayawa kadan.
Na samu bata nan sai yar ta da tazo hutu daga saudiya da muka zauna da ita muna hira dama mun saba tun a waya da ita idan maryam ta kira ta takan bani mu gaisa da haka har muka saba din da ita.
Sosai muke jin dadin hiran mu wanda ba wani hira bane sai na yanayin karatun nan kasar mu da inda take karatu a saudiya.
Mahaifiyar ta da ta buga ma waya ta sheda mata zuwa na ne ta dawo da fara,anta a fuska take taro na har kasa nakai ina gaida ita zuwa tayi inda nake tana fadin.
Kai haba khadija zauna mana ke fa yanzu ba bakuwar gidan nan bace don gashi ma yanzu naji mamakin ganin wanan mai kama da kura ta sake jiki dake haka har kuna dariya.
Hummaira tace lah mami na san anty khadija fa tun a waya mukan gaisa da ita time to time har zancen auren ta na sani.
Ledan da na shigo dashi ne na mika ma anty a cikin ladani ina fadin ga dan tsaraba nan ba yawa na riko maki anty.
Karban ledan tayi tana budewa da sauri ta dago kai tana fadin kai kai kai khadija wanan tsaraban manya haka duk ani daya.
Gaskiya wanan ba abin fitarwa bane kowa ya gani wanan sai idan na shiga daki ni kadai hummaira dake kallon uwar nata tace mami idan naji kin fadi haka rowa kike son muna.
Anty khadija may kika kawo ma mami take kokarin yi min rowa ta mike zuwa wurin uwar sai ta dauke ledan ta boye nan suka kama yar boya da uwar.
Sun bani sha,awa sosai yadda sukeyi da uwar nata kamar kawayen juna karshe dai sai ta bude ledan hummaira nagani ta fada jikin uwar tana murna tare da fadin.
Wai mami ashe da rabon zanci wanan abin tambayar yar tayi may ye sunan abin ina kallon su ina dariya daga inda nake zaune.
Juyowa anty tayi inda nake tana fadin khadija fada mata sunan shi murmusawa nayi ina fadin kilishi wanan anty ba na nan bane a kebbi na aika aka sawo min don yafi dadi.
Kai bari mu dana muji tace tana bude ledan ta balla kadan ta mika ma hummaira din wai anty tace bayan ta gutsura ta tauna tace wanan wani gari ake yin sa don Allah nace wata course mate din mu ce take sawo shi mijin ta dan can ne wai kilishin gwandu.
Gaskiya wanan yaci sunan sa ainihin kilishi irin na da wanda muka sani ke nan sallaman maryam mukaji muka amsa anty tana kokarin boye ledan a bayan ta don ganin shigowar maryam din.
Nace anty ai ba sai kin boye ba don na dibar mata nata jiya da aka kawo min shi wanan naki ne na kawo maki.
Zama maryam din tayi kusa da ita suka sa ta a tsakiya nan suka far ma kilishin da ci maryam ne take fadin ta buzuwa ashe kin samu shigowa din.
Hararan ta nayi nace ba buzuwa buzaye anty tace kin ga na manta wanan yar kwadan ta cika ni da surutun banza wai ya kuke a gidan.
Murmushi nayi tare da fadin muna nan dai anty humamaira ne ta mike tana fadin mami kawo ledan in kai maki daki boye ledan tayi a karshinta tare da cewa sai mun raba na dibarwa daddyn ku nasa kin san yana son shi sosai shima.
Hummaira ta shige a shagwabe uwar ta juyo gare ni tana fadin kedai ina jinki kanwata nace suna can yanzu ma nabarsu kamar kullun nan nake labarta masu abinda na gani yanzu kafin in fito.
Tace ai indai wa yan nan ne aikin su ke nan ba fasawa zasuyi ba ko basu cin riba ke dai dama abinda yasa nake neman ba wani abu bane sai in kara fada maki ki kula sosai.
Ina son ki kuma classic lady sosai khadija kin ga kwalliyan nan yana daukan hankali maza sosai tundai irin mazan nan naku da suke yara ga kuma sanadarin a hannun su, shine kudi.
Ki dage sosai kada ki ji kiuyan komai ki dinga masa abincin da yafi so kina daurewa a gurin shimfida kinuna mai cewa ke ma gwanace ta wanan famnin har kin fishi iyawa.
Dariya maryam tayi tare da fadin Allah yasa anty wanan kamar kifin rijiya take fa ba abinda ban fada mata ba.
Wanan kuma wani abune dake kara haska kwarjin mace ga miji khadija shiyasa zaki ga wasu mata ba kyaune dasu ba amma miji yanaji dasu kamar ya lashe a gida.
Kin san fa maza su a wanan fannin basu da wasa ko ita buxuwan ai da wanan abin take samun galabarshi ba komai ba.
Don idan ba kin tsaya wasa ba ai duk inda wata buzuwa zata tsaya khadija zaki iya tsayawa may ake so gun mace gyara da wayewa yanzu duk kina dasu sai lafabin aure wanda nasan ko rantsuwa nayi bani kaffaran haka.
Kin fi wanan buzuwa ladabin aure a gare shi So kina da dama da zakiyi amfani da naki baiwan wurin gwada mata ita ba komai bace a idon ki .
Idan har kin rike wanan abin dana fada maki babban makamin ki ya zamo Allah shi zaki sa a gaba ya taimaka maki akan komai da zakiyi.
Wallahi khadija ni na fada maki zakiji buzuwan nan tadawo tana fadin kin kwace mata miji ne da asiri ko wani abu.
Yanzu akwai wata kawata yar libiya ce matar zan turaku wurin ta zata baki training akan komai na rayuwa na riga da na mata magana akan matsalan ki.
Don haka ki daure ki dan yi sequzy din kan ki ki rage lokacin don ki samu ganawa da ita a kullun just three week ko four kawai ya isa ki haddace komai da kike so.
Zan shiga dubai zan hado maki duk wani abinda zaki bukata maryam tace akwai wasu kayan lates da mijin ta ya sawo mata a matsayin kayan lefe.
Tace ok ku kwaso mu bada dinkun nan su a modern design suyi maki express masu kyau na gani na fada najan ra,ayi .
Ki gani idan baki haukata wanan buzuwan da makarabanta ba suma su madam din ai ba don Allah suke tare da ita ba .
Abin hannun ta da mijin ku, ke sake mata ne suke gwadayi a wurin ta dan bata san ciwon kanta ba sam.
Yanzu abinda nake kara son ki dashi shine ki koyi dabara ta tanadin abinda kike samu daga gare shi ta yadda ke ma zaki iya gina kan ki ki zauna a kafan ki, ki kafu.
Shawara mai amfani ranan tayi min sosai wanda ni ban kawo wutan yin shi ba a raina nace ashe magani ne a gonar yaro ba sai nabi wani hanya ba can nike da maganin a tare dani.
Sai da nayi sallah la,asar a gidan tasa drivern su ya kaini gida tare da maryam muka fito zuwa gidan namu.
Mun samu su madam a gidan ana shewa da hayaniya an barbaje ana ciye ciye maryam na biye dani a bayana muna tafe muna hira.
Zan taka falon naji gabana ya fadi addua nayi saurin kawowa a bakina da sallama mara sauti na shiga sai dana karanto adduan .
Alama nagani daga na garin magani a kofan shiga part din da sauri na rike maryam ina mata nuni da abinda na gani idanuwa suka watso muna suna Allah Allah in taka abin da aka barbada din.
Sai sukaga naja na tsaya fita mukayi da maryam din a waje muka tsaya muna shawaran abin yi maryam ce ta kawo shawaran may zai hana mu shiga makwabtan mu muyi fitsari mu zuba.
Dariya ta bani nace kina ganin haka zai yuyu tace ba ance yana kara asiri ba nace ban fa taba shiga gidan kowa ba anan maryam asalima ba wanda ya sanmu.
Yanzu dai bari ki gani ashe suna leken mu maryam ne ta gansu take fada min adduan neman tsari na karanto naji gabana ya daina faduwa shiga muka sakeyi main kitchen din gidan na nufa na dako tsintsiya da mofa suna kallo na share abin maryam na zuba ruwa.
Muka bude part din muka shiga muna shiga maryam tace wai Allah ya somu yau khadija kina da kula wallahi da nice ai afkawa zanyi hakana batare dana halkanta ba.
Nace maryam kullun ido akan komai yake a gidan nan bakina kuma bai daina karanto addua don sanin halin wace muke zaune da ita.
Idan naji gabana yana yawan faduwa maryam tun ina gidan mu nai nitice din haka wani abune mara kyau ke shirin faruwa dani.
Kin san ance ko wani mutum yana da sing din shi na gane abu kula da hakan ne kawai mutane basu yi.
Amma yanzu kin ji zuciyana wasai nake jin shi alaman abin ya gushe ke nan a gare ni Allah ya tsare ya kare maryam tace nace amin.
Madam ta fara magana a falon bayan shigan mu wurina tace Nafisa anya wanan kishiyar taki ita kadaine kuwa.
Ko dai tana da aljannun da ke nuna mata abune haka ji yarinyar nan yanzu abinda tai muna fa ta nuna muna ta gane may mukayi mata.
Kin manta ne madam jikar mayune fa tana ganin har hanji banyi mamakin haka ba don dama malam ya fada muna haka kin manta ne ?
Idan tasan wata ai bata san wata ba don wanan da zan saka a kasan gadon dakin shi yafi zama shu,umi a gare su don ko ta mutu ko hauka kota kwanta ciwon da ba magani.
Ina da tabbacin sosai ga wanan aikin yanzu shigar su kawai nake jira dakin su kwanta da ta kwanta shegiya sai buxunta ba ita ba.
Bayan mun hutane nacewa maryam ta dora min girki zan tafi dakin shi in dan gyara na fito ina saye a cikin dogon rika na zaman gida.
Na daura dan kwalin rigar a kaina rigar free ce don shan iska akayi shi baida wani nauyi sosai.
Na tura kofan da sallama na nashiga dakin nabi da kallo a hankali gadon dakin naga alaman an daga take sai gabana ya harba min dammm.
Wurin na nufa kamar wace ake turawa sai kawai na daga gadon na shiga dubawa abubuwa ne ba zaka gane akwaisu ba a dakin an nade a cikin farin leda a ka cusa can; daga gefe daya.
Ban dakin na shiga nayo fitsari na zuba mai na sharo abin sai dai ban zubar ba na aje a cikon dusbin sai ya dawo in tambaye shi idan ba nasa bane.
Na gyaro dakin ko ina na rufo mai na fito basu falon a lokacin har na koma part dina na samu maryam tayi nisa ga aikin da take min.
Bata tafi ba sai da mukai sallah magariba ta dauki kayan da zata kaiwa anty ta tafi ya saura ni kadaice a part din .
Na

83 / 144

Chapters