MIJIN BUZUWA complete Hausa Novels.txt

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   117 / 144

348K to 351K   out of 431K words

min din.
Deedar ya jikin ba dai inda kike ji yanzu ko ya tambaya yana kokarin taba min jiki nace lafiya nake nurse din dake dakin bai hanashi tabani ba yana fadin maman twin's ke nan ?
Murmushi nayi masa na turo baki nace ban san ya akayi na dauko wanan hannun ba ko ita dake da gadon abinta bata haifa sai ni.
Yace nowarder nikan ina mamaki ina kika dauko tagwaye kuma nace maman mu ce tagwayen itama namiji ne abokin tagwacin ta ai.
Amma mama ta kyauta min wallahi don nike da wanan baiwan data sam baku a zurianta gashi ita bata samu ba ni na samu ta sanadin ta.
Maryam ne ta shigo dauke da yaran a hannun ta da suka sha kayan sanyi da farin showel tace ga kyautar Allah ka rika dazu ka dauke su ba ai masu wanka ba.
Sai da ya karbi yaran ya dade yana masu kallon kwab dukkan su biyu ya dago yace wa maryam wanan sun dara uwar su ma fari nake gani tace shi muke fada da mama yanzu.
Wa yan nan gaskiya kamar diyan wasu halfcase dasu ya kara maimaitawa yana mikawa maryam su nace daga inda nake maryam dan ban ruwa in hade maganin nan.
Ta kwantar da yaran a gefe na yace ruwan zafi fa zaki bata tasha kada ki debo mata na sanyi shiyasa nace mommy ta taso yau din nan tazo.
Nace a wanan lokacin yace jirgin yamma zasu biyo ita da Altine zasu zo da sauri nace ashe baka manta da alkawrin da kai mata ba ke nan yace yana raina ai.
Don naso tazo tun kan a haihu don ban dauka tarbon wata zaki yi haka ba na dauka ko sai irin tsakiyan wata din nan ne haihuwan idan naje sai in zo da ita.
Har yakai kofa zai fita bayan ya tsare ni da ido nasha maganin sai ya juyo yana fadin Nafisa ko ta shigo dakin nan na tare da fadin kasan ba a kimtsa ba kila tana jiran a rarage ne ta shigo.
Kai ya girgiza ya fita maryam ce ta kalle ni tana fadin kai namiji ji mutumin nan yadda yake rawan kai da samun yaran nan yanzu.
Nace haka yake ai idan an mai haihuwa sai dai son yaran nasa a baki ne kawai ai baida jan diyan shi a jikin shi shi.
Tace to ke zaki yarda ne aikrce zaki koya ma yaran manne masa ko baiso kuwa don idan ma baki koya masu ba sai wata tazo kiga yana nan nan da diyan ta kina kallo.
Ajiyan zuciya na sauke tun yanzu zan fara fuskantar wani abu kuma akan yaran da basufi awa daya da fadowa duniya ta mu ba mai cike da rikici a cikin ta.
Sai lokacin nace maryam ta miko min yaran don in masu addua na karanta masu adduoin tsari tare da bude farinjin su na karanto masu adduan tsari daga zina.
Biyar laraba ta gama abinci har lokacin nurse din nan mai kirki tana gidan tana ta koya mun komai da zanyi akaina da babeis din.
Abincin suka debo min nurse din nan ta sani a gaba ina ci mommy suka iso gidan ina jin muryan su sai gasu dakin da murnan su suka shigo sai naga har da ya Aminana suka zo.
Ina ganin ta nayi narai narai da idanu kamar zanyi kuka saboda dadin ganin ta da nayi gaishe su na fara yi mommy ta karaso inda yaran suke tana fadin khadija aike ke da sannu yara manya haka dasu kamar ba tagwaye ba don Allah.
Nan dai ake anata hira sai ga Laraba tazo tana kirana dagani maganane da ita haka na mike mommy tace dawo ki saka hijjabin ki ko nan da falo zaki yanzu ki kula da hakan.
Na samu laraba take cewa muje kitchen naga abinda aka shigo dashi sai dana dan duba nace mommy za a kira ta san yadda za ayi dasu ai.
Nama ne mai yawan gaske sai kan shanu har biyu da kafafuwan su da sauran tarkace ya kwaso dakin na koma suna zaune nace mommy Laraba na magana dake da Anty Altine a falon.
Mikewa sukayi sun samay ta ta nuna masu kayan da abinda nace mommy ta duba tace dayake akwai frezer sai a saka zuwa gobe amma kayan cikin a dan diba ke Altine ai mata ferfusu da zata sha kafin ta kwanta yau.
Bayan sun gama adana komai yadda ya dace mommy na shigowa dakin tace ikon Allah ance naka sai naka yau mune a gidan babangida ake halarta muna komai a matsayin mu na manyan shi.
Ance ma hakurci mawadaci abinda muke mashi nuni dashi ke nan tuntuni ya kasa fahinta na tuna da mukazo zaman yar nan Ihisan irin taskun da Nafisa ta nuna muna a gidan nan lokacin.
Altine ce ta tambaya ina take ne mommy tace tana kasansu ai nace ta dawo jiya mommy tace jiya jiyan nan dai nace eh jiya suka dawo daga can.
Altine ta kara tambaya tashigo taga tagwaye ko laraba ne ta basu amsa da ko leke ba wanda ya shigo daga sashen ta tana fadi ta fita.
Lokacin na bata rai nace ban ma son su shigo din mommy don mafalkin danayi kafin in haihu nan dai na koro masu abinda nake tajiwa akan yaran nace mafalkin hakan nayi da Nafisa din.
Da sauri Altine tace indai ina gidan nan kuwa ba zasu ga yaran nan ba har su dauka don wallahi kemaymay zan masu idan sun shigo .
Mommy tace dole muyi taka tsantsan kan haka don hajiya mama saida ta fada min haka dana shiga muyi sallama da ita wallahi tace don Allah musa ido kan shu,umar matar shi ashe kinga da batu ke nan a gidan nan.
Ya Amina da ba gwanar magana ba sai fadi take Allah to ya kare yanzu mommy kina ganin zamu iya hana mata su ta dauke su din nace in dai har anyi suna basu sanu taba su shike nan ai.
Anty Altine kamar yadda nake kiranta tace har bayan suna indai ina gidan nan bazata dauke su ba may ye amfanin boye mata an san manufar ta ne.
Ai gara a nuna mata tunda itama haka take wa mutune idan ta haihu har yanzu wayasan diyan ta a cikin dangi.
Nan dai suka sha hira akan nafisa din har wani lokaci sai kafin in kwanta nace ma mommy yaya zasu kwanciya.
Tace bari taje dakin da ba kowa su sauka a ciki nace ya Amina tace a a mommy ke ce dai zaki zauna dasu nan mana ni da Altine sai muje can dakin ko dakin laraba.
Mommy tace dake dai Amina zamu tsaya nan din don dare da sauran lalura don bamu san yaran ko suna fitinan dare ba.
Ni barci ya cika min ido koda AA ya shigo masu da ledan kaji gassasu ya dan duba yaran suka gaisa da baki yadan yi hira da Altine tana tambayan shi ina tarin buzayen gidan shi .
Dariya yayi yana nuna ta ya fita ya Amina ce ta tayar dani wai in tashi in kewaya kafin a kwanta don inji dadin barci da dadi ruwa ta surka min na shiga na fito take fada min wai ga kajinan in ci na gyada kai nace bazan iya ci ba anty mommy ta hauni da fada tana fadin zaki yi jagon wasa khadija jego fa baison hakana daure kici ko kadan ne da dan ruwan tea sai ki kwanta.
Badon naso ba haka na daure na sha tea din na kwanta can cikin dare nake jin muryan su wai namijin ya hana su barci yana kuka.
Ruwa suka bashi sai ya dan fara barci kuma yasa kuka ya falka sai da mommy ta goya shi suka dan samu barci tana fadin yunwa yake ji yasa bai runtsa ba.
Washegari koda bakwai yayi har nayi wanka na shirya ko suna ta hada hadan wanka da hada abin karyawa zuwa tara duk mun karya muna zaune sai ga Nafisa da madam sun shigo dakin .
Sai da naji gabana ya fadi Altine dake kitchen ne ta shigo dakin da saurin ta taja ta tsaye a bakin gado.
Bayan sun gaisa dasu mommy tace ga kawayen ta sunzo suga babies su gaida mai jego tana wani fara an dole ta nufi bakin gadon da yaran ke kwace suna barci.
Altine tace dakata kada ki taba su don Allah barci suke yi ta riga nafisa dukawa gurin da yaran su wani kallo Nafisa tayi mata tace nice zaki hana daukan yaran ?
Tace ban hanaki ba amma aladan mune ba a taba yaro idan baiyi sati da haihuwa ba don haka barsu nan har zuwa gaba madam tace amma ai itama uwace a gurin su ko ko baki sheda ta bace.
Haka umurnin yake daga kakanin yaran komu nan ai kin ga daukan su mukeyi ba dai ko zargina kike son yi komay nafisa ta fada.
Babu zancen zargi anan amma ki barsu nan ikon Allah yaran ma rowan su akeyi ke nan nidai kaina na duke ina cin ferfesun da aka aje min yaji kayan yaji na gargajiya sai kamshi yake yi.
Kiri kiri sukai wa juna sai da Altine tayi masu na mahaukata ta nuna masu ita tsohuwar yar barikice itama suka fice baram baram a part din .
Mommy tace yau Altine kin cece mu da muna kadai a dakin nan ai kyale su zamuyi su dauki yaran ajiyan zuciya na sauke baya fitar su.
Mommy tace falo zamu koma duk wanda yazo muce suna ciki don zasu iya biyo muna ta wani hanya kuma tunda sun fahinci an gane su.
Laraba ce ta shigo tana fadin abin mamaki yau naga bakuwa a gidan nan cikin buzayen da suka zo tana sallah har sallah walha take yi.
Jiya ma tunda tai magariba take zaune tana karatun kur,ani wurin har aka kira sallah isha,i tanayi mommy ne ta bata amsa da fadin ke ance maki duka suka taru suka zama daya akwai na Allah a cikin su ai sosai ma yanzu wayewan kai na addini ina ne bai ratsaba.
Kukan da babyn mace tayi ne yasa hankalin su ya koma kanta mommy ke fadin yaran nan yunwa suke ji ya kamata su fara kama nono haka na Amina kara gyara nonon nan a basu su sha .
Fuska na tabe shigowan maryam dakin na mayar da hankalina gare ta gaisawa tayi dasu mommy ta mike ta nufo ni da yarinyar.
Falo suka koma naji dadin hakan nan suka barni da ya Amina da maryam ina koya min yadda zan rika yaran.
Haka dai na daure yarinyar tana kamawa tana sakewa sai barci ta koma kuma na samu saida.
Ya Amina ne tacewa maryam kin makara maryam baki samu rikicin buzuwan ku da Altine ba kan daukan yaran nan da sauri maryam tace sun dauke su ne ?
Tace ai Altine ta hana su yau munga hauka badon Altine ba kan da mukan ai bamu iya tijaran su don yadda suka hakikance sai sun dauki yaran.
Nan dai ta bata labarin abinda ya faru tace mun dai gode Altinen na nan nace yar mijin ki ne fa sai ta harare ni kallon mu ya Amina tayi tace ta ina tazama yar mijin ta kuma ?
Maryam tace tambaye ta dai yaya nace ta sojan gidan su mommy da sauri tace Suraj nace shifa in Allah ya yarda tace ko shine naji ana rikici da uwar ya samu mata Abuja tace bata yarda ba yar yar uwanta zata hada shi da ita.
Wata sabuwa ke nan dama nasan sai an kwasa da Umma don da ganin ta irin matan nan ne dake mulkin diyan su sosai.
Muna cikin maganan mommy ta shigo dakin sai mukai shiru tace in fita kuna siri ne ya Amina tace a, a mommy ashe maryam din khadija ne Suraj ke so nan Abuja.
Da sauri mommy tace wace maryam nace wanan maryam dai tawa mommy ta sake fara a tana fadin dako yayi dacen mata wallahi dama shi irin ku yake so ai wayyyayu mata kamar shi.
Duk wace uwar ta kawo yace batai mai ba ita kuma taki bari ya kawo wace yake so idan mijin kine ubangiji Allah ya ingata tsakanin ku.
Suraj yana da kirki wallahi bai biyo halin sauran yaran dakin ba da nuna banbanci uwar ce dai matsala yanzu yana nan kan ya dage.
Ko zuwan nan dayayi last naga sun zauna wurin Alhaji nasan ko zancen ne ya Amina tace ita bata ganin yadda ya girma baiyi aure ba mommy tace wa yaya Allah dai ya kyauta.
Shine ai take ganin laifin hajiya mama wai ita ke sakewa diyan ta itakan ai bata da wasa ga yaro ko auren yayi ko yana under control din ta ne.
Suraj din daine ma bai faye bin dokan ta ba sani lokaci nace Allah dai ya shawo muna kan ta da abin baiyi dadi bako gaskiya.
Shiru maryam tayi na fahinci ta dan shiga damuwa mommy tace idan kina son abinki yana son ki in Allah yayi ai dole ta hakkura saukin abin daya ne idan taji ace ke din yar masu hali ne zata iya yarda daga baya.
Fita tayi tana rufo kofa muka kwashe da dariya nace mun zama yan kurkuku ke nan kofan ma sai an rufe mu a ciki ya Amina tace dole ni yanzu ma yadda in an watse zaku kwashe da ita nake ji ai.
Nace idan mommy bazasu zauna ba wallahi saidai in koma gida ban iya masifan wanan matar gaskiya yanzun dai sai yadda shawara ya tsaya ai don ban tsamani baban maigidan zai yarda ta zauna har arbain ba saboda gudun yadda akayi wancan karon.
AA ne ya budo dakin ya shigo gaisawa sukayi da ya Amina sai maryam data gaida shi ya amsa ya Amina ta mike zata fita yace zauna fita zanyi ai maryam kira min mommy falo.
Maryam ta mike zuwa kiran mommy din daga can bata dawo dakin ba momy ta shigo tana fadin kai Altine akwai tsiya wallahi.
Yana duke yana duba yaran yana kare masu kallo yace nurse din nan ne data karbi haihuwan yaran ta bugo min wai za a kaisu su amshi riga kafi yanzu can asibitin su.
Dama ashe kiranta wai yar maryam tayi makwabtane tayi kokari sosai wallahi matar kuma na tambaye ta mai za a bata tace wai ai gida ne tunda yar maryam ta turo ta sai ku fadi abinda za a bata mommy.
And kuma mommy ya akayi ina office yanzu nafisa ta kirani tana kuka wai tazo ganin yaran an hanata daukan su ita da kawayen ta.
Kafin mommy tayi magana sai ga Altine kamar an turo ta dakin momy nacewa ba hanata daukan su ai mukayi ba kasan ai haka ba zai yuyu ba babangida.
Altine ta cabe da fadin haka tace ma an hanata dauka idan bata da wani manufa may ye don ance suna barci a barsu sai bayan suna zata matsa sai sun dauke su.
Yace ke mahaukaciya da uwata nake magana tace ni kuma yarana nake karewa ba wallahi tsohon su yanzun an daina hakana irin hakane sai abu ya zo ya samu yaro a haife shi lafiya sai daga baya a rasa gane kan yaro .
Amma idan anyi suna yaro yasha addua duk wanda zai dauka ya dauka ana ta fadakarwa akan hakan yanzun duniya ya lalace wallahi ba a gane mugu a fuska barci suke akace su barsu don jiya basu bari anyi barci ba da dadi dan namijin yanata kuka da dare.
Yanzun dai na fahinci kece mai rashin mutuncin wa mata na ke nan ke kika sakata kuka ko wai harda kuka tayi don an ce su bari su tashi kila tana da wani manufa kenan akan su.
Taga yara bulbul gwanin ban sha,awa ta kwaso wani gaiyan buzayen ta suzo lashe min diya kai ya girgiza yace ke mahaukaciya ce tace naji dai ita wake daukan nata idan ta haifa ai ta sani sherin matane kawai irin namu.
Muko nan mun san komai wallahi sai anyi suna zamu bari kowa ya dauke su yace ke kada ki aibanta min mata fa an fada maki matana muguwa ce .
Bansan lokacin da na saka masu baki ga zancen su ba nace may ye na naci idan bata san sherin data kulla ba tun jiya ai na haihu bata shigo sai yau zata kwaso munafukan ta su zo min.
Wurina ya juya yana nuna ni yace mommy ki ji a gaban ku take fada kan yaranta ya juya zai fita yana fadin Altine ji mana ta bishi baya suka fita daga dakin.
Momy tace aini na gode da zuwan Altine dako Alhaji bai so a zo da ita ba sai da akace babangidan ne yace tazo ya yarda tazo.
Irin su ne daidai dasu ai momy don ta nuna masu ita ma ta iya ya fita sun dade sai ga Altine ta dawo dakin tana fadin ikon Allah.
Ina kawar buzuwa da suka shigo dazun bakar matar nan mai zubin yan duniya yanzun suna fitowa wallahi muna tsaye da tsohon su kawai mu kaga ta yanke jiki ta fadi.

117 / 144

Chapters