ne kawai nasan mommy tafita yasa ka kirani kamar yadda nake da kunya kai ma nasan zakaji kunyan waya a gaban ta ai.
Muryan mommy ne take fadin khadija kun koma lafiya jiya ya karatun Allah ya tsare ya kare ban iya cewa komai ba sai daburcewan da nayi a lokacin.
Hello khadija ba kya jine ina magana kin yi shiru nan ma ban iya magana ba shiru nayi mata a lokacin sai naji tayi murmushi.
Wayan na kashe sai da na gama girkin sai kuma cin abincin ya gagare ni duk da yunwar da nake ji din da farko .
Waya na dauko na tura mashi text kamar haka baka kyauta min ba ya zakai min haka ka san girman mommy a idona kuwa ai sai kasa ta zargi wani abu a zuciyar ta a gare mu.
Na gama na tura mai maryam ta shigo dakin tana fadin wai yau na gaji wallahi zama tayi tana kallon yanayin da ta samay a ciki.
May ya faru tace tana kallon fuska na cikin damuwa ga yadda ta ganni din sake tambayana tayi tana maida hankalin ta gare ni.
Ga abinci can ki diba ina kika tsaya har yamma haka lis wallahi mugun malamin nan namu ya tsaida mu haka yau test din yayi wuta sosai tamike tana fadin har kin ci ne ke tana kallo na.
Kaina girgiza mata tace kin ci wani abin ke nan ko naga ko karyawan kirki baki tsaya kinyi ba kika fita yau.
Wallahi da yunwa na dawo sai da na gama kuma naji ban son cin komai ki sha wanu abu mai ruwa kila yunwa ne yai maki yawa ya hanaki cin abincin.
Ta debo ta fara ci tayi nisa ga ci nake cewa da ita kin san may wanan mutumin yai min yau maryam.
Da sauri ta dago kanta tana fadin wani mutumi mamud ko wa nace wani mamud kuma AA fa don ya maidani karamar yarinya wai a gaban mommy zai kirani yai waya dani.
Maimakon inga damuwa itama a fuskan ta sai naga sabanin hakan a fuskanta dariya ta soma tana fadin lalai wanan dan barki ne .
Ya daure tamau yanzu a gurin mommy ta gama sanin komai a tsakanin ku ke nan ?
Komai kamar yaya ya dai daure ni wallahi tace ai maganin ki ke nan tunda bakya jin shawara ai gara da ya fito maki tanan.
Haushin ta naji sosai a rai na don rashin nuna jin haushin hakan dayayi min da ta nuna rashin damuwan ta akaina.
Bayan ta gama ta mike lokacin nayo alwala zanyi sallah itama ta shiga bayin ta dauro alwala muka gabatar da sallah mu.
Zaune nake bayan na idar da sallah ban bar wurin ba sai da nayi isha,i na mike ina nade sallaya maryam ta mike ta dauki heater tare da dauko cup ta hada min shayi mai kauri saida ta gama ta miko min.
Kamar ba zan karba sai dai na mika hannu ko ba komai nasan shan tea din zai taimaka min ga yunwa da ke ciki na.
Tunda na kwanta ban sake bi ta kan komai ba har barci ya dauke ni a haka yadda nake cikin dare na falka na ga ta rufe min kofa itama tana kwance a kusa dani ranan a dakina ta kwana.
Zaune take a falon madam datai ma tsuke tunda safe ta isa gidan madam din a yadda ta ganta sai take tambayan ta ko lafiya haka da safe.
Madam gaskiya yanzu samad ya rikice min tunda na haihu din nan na rasa gane kan shi gaba daya.
Jiya fa a gaban wanan kishiyar uwar tashi yake fada min wai aure zai kara saboda kawai nace sai ya fada min wace yarinya ne tazo gaida shi har take bare mai ayyaba tana bashi ?
Ke a ina kika ji wanan labarin ne wai waya fada maki ne shiya daure min kai tace kai tsaye su hajiya karima ne da suka je gaida shi.
Baki ga irin wullakancin da security din asibitin nan sukai min bane suka fitar dani waje yana kallo baiyi magana ba.
Haba Nafisa kullun ina fada maki magani fa bai ci sai da siyasa da kissa da kisisina da kutungwila na mata.
Ya zama dole yanzu ki bishi a sannu ko banza kin zubar da jinin haihuwa a gidan ki kiga komai da kikayi na asiri yanzu ya karye.
Ai ba karamin hikima bane aka samo na haihuwa asibiti da mata ke yi yanzu bature ya taimaka ma mata da ya fito da wanan hikimar haka na haihuwa asibiti.
Kinga ko da za a dawo da mace gidan ta an wanke komai a asibiti kinga wanan uwar tafiyan na haihuwa yafi komai karya asiri ga mutane ba matan ba ba mazan ba.
Shiyasa iyayyen mu na da basu wasa dashi a gida zakiga da sauri ake fitar dashi gida asamu gefe a binne shi amma mu matan yanzu sakacin mu yayi yawa ga komai wallahi.
Yanzu ya zama dole gare ki ki lalaba shi ki kara sabon shiri sosai a kanshi dan kada yazo ya bijire maki nan gaba.
Zancen kuma aure ni nasan ba dagaske yakeyi ba don ba abinda kika rasa da ake so gun mace yana kuma son ki tsakani da Allah.
Zancen kuma ita yar iskan yarinyar dake dmson maki kutse a gidan ki ta dauke maki hankalin mijin ki tambaya zamu muji da gaskiya ne hakane ?
Idan da gaske ne sai mu san ta inda zamu fito da zancen nata ga wanan irin arziki da ya taso ma mijin ki haka ina zamu bari muba wata daman da zata shigo ciki muna kallo.
Yar iska bamu san ko wace iri bace ita tazo tafimu iyawa dashi babu yadda zamuyi ko wacece zata shigo maki kin san itama ta shirya.
Don kishi da buzuwa ba wasa bane duk matan nahiyar nan namu sun sani shiyasa suke tsoron ku buzaye don cire ice har sayen shi komai tsufan shi ba wasa bane gare ku.
Madam duk da haka ya zama dole gare ni in tashi tsaye in hana gaba da bayan shi motsi a gare shi ko mace ba zai iya daga ido ya kalla da sunan tausayi ba balle so.
Yanzu dai duk ba wanan ba sai fa kin kwantar da hankalin ki ko ta siyasa zaki iya gano gaskiyar maganan gare shi idan kin kwanta amma.
Tace a sanyaye naji zan gwada yin abinda kika ce min din tai mata godiya tare da sallama ta nufi gida tana ba kanta hakkuri.
A ranan ya samu sallama bayan dawowan Yusuf da bayanin abinda ya girgiza shi daga malam don yace a lemon da ta tare shi dashi yasha batare da yayi bissimillah ba.
Yayi arziki akwai tsari sosai na Allah a jikin shi da ba karamin wahala zaiyi ba don ba maganin alheri akabata tabashi ba.
Ya iso gida zuciyar shi ba dadi wanka ya shiga don ya tsabtace jikin shi don baijin zai iyacin abinci ga yadda yake jin kanshi a lokacin.
Yana zaune bakin gado ta shigo dakin ta saba diyar ta a kafada tana rangaji tana zuwa ta azamai yarinyar saman jikin shi itama ta samu wuri ta zauna a gefen shi.
Yadda taga bai sake fuskan shi ba yasata fadin har yanzu abinda ya faru ne kake ma fushi haka ko jikin naka ne har yanzu.
Kallon ta yayi yace may ya faru kamar bai fahince ta ba tace akan maganan nan na asibiti da ya faru raina ne ya baci a lokacin nayi haka ba tare da nayi tunanen komai ba.
Wanan matsalan ki ne sai dai ki sani duk abinda zaki karbo daga yau da sunan malakana a gidan nan kada ki sake karbo wanda zai cuta min haka don ki sani nasan abinda kika zuba min a lemon da kika bani ranan.
Kuma shiya haifa min wanan ciwon danayi ban hanaki yin abinda kike ganin shine mafita a gare ki ba don dama haka yawancin mata kuke da wanan shigeshigen din sai dai ki sani ba zaki taba mallakana ke kaidai ba domin ni din mijin mace hudu.
Yana fadin haka ya mika mata yar tare da mikewa ya bar mata dakin nan ya barta cike da mamaki tana wasi wasin ko dai wani ya fada mai a gidan.
To ina ma wani ya ganni nida na zuba a cikin dakina amma yaya akayi wanan maganan ya koma kunnen shi haka.
Watau ke nan abinda ta zuba mai ne ya jawo mashi haka ba maganin kwarai aka bata ba kena cutar ta akayi akan maganin da ta kashe makuden kudi akan shk a bazan zai tafi ba zaiyi aiki akan shi ba tunda had ya gane may ake ciki.
Ko dai shima yana irin nata ne har yaje wani ya fada mai abinda tayi mai tace kai wanda ke kwance haka ba lafiya ina zai iya zuwa ?
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Kwance nake saman katifan dakina ina karanta handout dina maryam zaune a bakin katifan tana gyara kumbar kafan ta.
Waka take wanda take damuna dashi sai ya hanani yin karatun tunanen mamud nakeyi wanda ya kai sati biyu yanzu bai lekoni ba kuma banji daga gareshi ba har wanan lokaci.
Hijjab dina dake gefe na dauka na rufe jikina dashi tace sanyi kike ji ko may da zaki rufe jiki haka nace sanyi nake ji wallahi.
Na kara jawo handout inci gaba da karatu tace wai ni ko dazun sai naji kina waya ina son in fito in tambaya wakiraki ko mutumin naki ne naga ya dade bai zo ba kuma banji yana kiranki ba.
Maryam kin damay ni fa karatu nake kuma kin gani a, a wani karatu yanzu inga kina tunane ke kika ga wanan din na gyara kwanciya ina bata baya.
Sai da ta gama abinda takeyi tace don Allah tace muje mini market mu sayo kayan miya nace ban zuwa tare da lumshe idona.
Fada min a jiki naji tayi tana dariya tare da sake ihu daidai kunnuwa na a zabure na mike na biyo bayan ta da gudu zuwa waje.
Dagani sai dan body hook da nake sakawa a ciki in dora abaya kaina ba dan kwali gashina dana daure ya fado min a baya don duk zuben filani na gajeshi wurin kakannin mahaifan daddy na.
A daidai lokacin nz hango motar su tana fakin a daidai inda suke tsayawa da mota idan sunzo guri na ban dauka su bane sai da na duba da kyau don gurin na kowa da kowane masu zuwa wurin yan matan su.
Itama maryam din ta gansu da sauri ta dawo inda nake tsaye tana fadin su yaya Yusuf ne can ko ?
Ba yadda zanyi don sun gama gani na gashi ko dan kwali babu akaina da sauri na koma ciki ita ce ta tafi wurin su tana gaidasu.
Yusuf ne ya tambaye ta gudun may muke haka kamar yara tace wallahi khadija ce ta biyo ni da gudu wai ina damun ta tana karatu.
Na fito daga ciki na dora a baya saman kayan ina hararan khadija na iso inda suke tundaga nesa ya watso min harara yi nayi kamar banganshi ba na kawar da kaina ga kallon shi ina gaida su baki daya.
Har muka gama gaisawa da Yusuf yana tambayana karatu da kwana biyu nace lafiya maryam taso ta bar gurin da dabara Yusuf yace ta tsaya ai .
Munzo muyi maku sallama ne zamu tafi umura gobe idan Allah ya kaimu mukayi masu adduan adawo lafiya Allah yasa a karbi ibada.
Daga ida yake zaune baiyi magana ba tun zuwa su yace ashe baki jin magana baki daina saka kaya irin wanan ki fito dasu waje ba ?
Nace wasu kaya kuma ina duban kaina da shigan da nayi yace ai kema kin sani yaya kika fito waje dazun ?
Haba yaushe zaka daina samin ido hakane aiko wanda zan aura yanzu bai isa ya zaba min kayan da zans saka ba a jikina sai idan naje gidan shi.
Murmushi mai kama da yake ya sakar min yana fadin au haka ne fa kuma gaskiya na faye sa ido.
Yusuf yace kajiki da wani magana kuma akwai wanda yafishi sanin ya kamata akan ki ne yanzu dole ya nuna bacin rai ga abinda yake da iko dashi.
Dariya nayi sosai nace sai kace nice buzuwa ko anty Fati wanan dokan yanzu ai sai daddy na yakai can.
A bari a rabu lafiya kin ga tafiya zai yi kada a rabu kuna halin naku kuma kinga zai tafi dake a zuciya kila ba zai maki addua ba idan yaje.
Addua kan kulun ai mahaifa na suna min shi kuma yana tasiri gare ni wanan bakin naki kuwa anya wataran bazai mutu ba khadija ?
Dariya nayi nace yau dai kun tuna mu ke nan aka kawo muna ziyara haka yace bakin ki zuwa gida ki kara gaida shi da jiki ba ai shi baiyi fushi ba gashi yazo.
Dan satan kallon shi nayi naga hankalin shi baya gare mu nan dai mukayi sallama dasu suka tafi.
Da yamma ina kwance sai ga kiran shi ya shigo min a wayana nayi makai dalilin kiran shi sai cewa yayi fito gani bakin hostel din ku kai tsaye kamar yadda ya saba ya katse kiran.
Na shirya na fito shi kadai na sama kamar yadda nayi tsamani bayan na gaidashine yake fadin dawowa nayi don dazu muna barin wurin nan Abba ya kirani.
Yana son mommy ta koma gida kafin in wuce don haka nake son ki rakani musai masu abinda ya dace diban lokaci nayi a wayana bakwai da rabi na dare don haka akwai lokaci.
Ciki na koma na shirya sai da na zauna ya tayar da mota nace kana dai son ka ban wahala kai da sukai ma hidima dakai da matar ka ni may ye nawa a ciki yanzu.
Na dauka yanzu ma ai da shigan dazu zaki fito tunda ban isa in baki umarni ba ban dai ga dama bai don ba mai iko dani a yanzu.
Allah yakaimu in dawo lafiya zanyi maganin wanan fitsaran naki lokaci daya .
Ka fara maganin fitsariyar matar ta gida mai fita rabi tsira wace bata damu da hijjab ba balle gyale kafin kazo kafa min dokan ka .
Sallon yaudara kawai zaka wani gama kalle min jiki kawani ce kai baka son haka na bayan sai da ka kalle ni tsab.
Dama badon akalle ki kika saka ba idan ni kadai zan kalla ba matsala bane a gare ni wasune kawai ban son suga abinda nagani din.
Don kanawa a gare ni zaka hana wasu su kalle ni kada ka mata ni yanzu a kasuwa nake banda hakkin kowa ai kaina amma ga masu hakki baka tsa, , ,
Jinin hannun shi kawai nayi a jikina yana fadin barin fara gwadawa in gani ko tayi min tunda a kasuwa kike kinga idan yayi min basai kin tallata ma wasu mazan ba.
Bugu nakai ma hannun nashi sosai da yakai ma jikina yana shafawa bai san ina yi ba sai kokarin gwaucewa nake yi ina buge hannun shi.
Fuskan shi a daure bai fasa min abinda yakeyi ba wuri ya samu ya sauka daga titi.
Da karfi nace bude min in fita ina kokarin bude kofar motar a gigice hannun shi naji yana cire min dan gyalen da na yafa saman dogon rigar da nasa.
A take gashin kaina dana tufke daniyar in na samu lokaci inje gurin kitso ya bayana a fili hannu yasa yana wasa da gashin har zuwa inda ya tsaya.
Take naji wani hawayen bakin ciki ya silalo min a fuska na haka bai sa ya daina abinda yake min ba sai ma ji danayi ta rungumay tsam a jikin shi yana sauke wani irin numfashi yana shafa na son ran shi.
Kara sautin kuka na nayi a lokacin sai naji ya sake ni yana fadin are you crying bocouse of dis akasuwa fa kike yanzu.
Hannun shi yakai saman fuskana yana wasa da hawayen dake zubo min din sai kuma naji ya rungumay ni zuwa jikin shi tsam na dan wani lokaci.
Sai da ya gaji don karan kanshi naji ya sake ni ya koma saman kujeran motar ya kwanta yana maida numfashi a hankali.
Kaina na dukar naci gaba da kukan abinda yai min din can kuma naji ya tada mota a hankali ya hau titi ba tare da yayi magana ba .
Kofan bakin wani plaza mai girma ya tsaya ban taba sanin akwai wuri haka a abuja ya bude motar a hankali tare da fadin fito mu shiga ki zaba masu abinda ya dace dasu kuma ki share wanan hawayen kada ace satoki nayi.
Sai lokacin na dago kaina na dubi wurin nace ka sani har kullun Allah ba zai taba baka sa a akaina ba mayaudari kawai.
Dariya naji yayi yana bude motar yace banda wanda Allah ya bani yanzu a kanki kuma koko kina nufin karfin ki ne ya kwace ki a kaina .
Kuma ki daina kira da mayaudari don da yardan ki muka fito nan