MIJIN BUZUWA complete Hausa Novels.txt

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   136 / 144

405K to 408K   out of 431K words

a lokaci daya komai nawa ya canza kamar ma kada inje garin mu taga na wani kara kiba da haske sosai sai yau take ganin abinda su madam suka sha fada mata a kaina.
Wani iri taji a ranta tare da fadin shike nan bakin bakin su madam yaja min tabbatar wanan abin ga yarinyar nan yanzu yaushe har ta bunkashe haka ne wai ?
Lalai tayi sake da yawa da idon ta ya rufe bata hango haka ba tunda wuri anya yanzu kuwa zata iya taron wanan da take gani a gaban ta zata iya shawo kanta kuwa ?
Don idan batayi da gaske ba tana kallo zata kwace mata komai nata a gidan tasan dai idan kyau ne ko fari take rudan mutane dashi wanan ma ba baya ba haka kuma ga ilimin da take dashi wanda take gani dashi take kara amfani wurin ganin bayan ta a gidan.
Kai anya nan gama ko zata iya karawa da Dijan nan da yanzu gaba daya komai nata ya sauya ya zama na hamshakan matan da ake iya damawa da ita.
Duk kokarin ta wurin taga ta shiga sahun matan manyan abuja abun ya faskara sai ta dan jona dasu kwana biyu sai su bare ko don suna daukan ta bare ne ita haka ke faruwa.
Dama ance mutum bai ganin illar shi abinda bata gane ba shine halinta na rasgin tauhidi ke kore mata mutane.
Don da ta dan kwana biyu da kawance da mace zakaji ta fito mata da kudirin ta tana tambayan ta ko tasan gidan wani boka ko malami da aikin shi ke ci kamar yanka ?
Ko tace ita kishiyanta take son kashewa ko ta haukata ta ko ta batar da ita ta shiga duniya a manta da ita gaba daya ire iren wanan maganan ke ba matan da take son mamuwa tsoro suke gudun ta kwana biyu ta daina jin su.
Hakane yasa ta kula da mata masu zaman kansu a Abuja don su basu da lasisi haka take gare su ko ina ta fada rataya ne.
Ina tsaye har suka gyara falon zuwa wajen gidan da ko ina dake da bukatan gyara a gidan suka feshe ko ina da kamshi gidan ya dawo daidai.
Nafisa ko tana daki ta kasa fitowa sai tunane take tana sakawa tana sancewa don komai ya juye mata a lokaci guda a gidan ga samad dake wanan fushin ko kallon inda take baya yi.
Har Ihisan laifin take ganin ya shafa don ya shigo yarinyar na kiriniya ya daka mata tsawa taki dainawa ya kamata yai mata dukan tsiya a gabanta.
Idan da dane sai dai yayi dariya ya wuce idan tana irin wanan halin ta manta ita abinda taiwa uwa da yaranta a baya data hanasu shakuwa ma da uban su gaba daya.
Idan ya shigo ko kallon yarinyar baiyi yanzu sai dai ta sha alwashin ba zata yarda ya mayar mata da ya wani part ba da abinta zata zauna.
Nikan muna shiga nayi wanka tare da dauro alwala nayi sallah nafito kitchen na nufa don dora girkin dare da kaina don ina son burge maigidan yau.
Komai na hada sai da akai la,asar ne na fito na koma daki na dan jima a ciki kafin in fito in duba girki na sai da na tabbatar komai yayi yadda nake so.
Na dawo falo wurin su Altine muka zauna kallo suke wanda ni ba gane kan kallon ban dade da zama ba na mike zuwa ciki don gwada wani abinda Anty salbiya ta taba bani ban taba amfani dashi ba.
Sai yau tunda nice zan karbi girki a gidan nayi kamar yadda tace min ina gamawa na zauna bakin gadona don inyi waya da maryam don naga bata shigo ba.
Mun dan dade muna wayan inda take fada min zancen su da Suraj ya tabbata don karshen satin nan zasu je gurin iyayyen ta a tsayar da magana.
Murna nayi mata sosai tare da fatan alheri gare ta nace zamu koma a innuwa daya ke nan tace ke dai bari ni abin mamaki ma yake bani.
Ba a mamaki da ikon Allah nace baki ganina yanzu Allah ya dora ni akan Nafisa a gidan nan abinda kowa ke min fargaba a baya.
Idan Yusuf yana fadin zan iya sai inga ta ina zan iya da wanan shedaniyar ashe abin daga Allah ne kaidai ka dogara gare shi kaga aiki da cikawa.
Khadija in banda abinki in bamake ba ai wanan buzuwan tana da saurin kawarwa don gata nan da abubuwan fada kala kala tare da ita.
Matar da bautan ubangiji ma sai taga dama takeyin sa bata san wani abu ba sai shirka da bata ina cikin sauraren maryam ne ban san shigowan shi dakin ba don ban masan lokaci yaja haka ba.
Fuskana na kallon cikin dakin na shagala da wayan sai ji nayi an dafa ni ta baya a firgice na juya yana shi na gani a tsaye yana min wani irin kallo a cikin gajiya.
Dawa kike waya haka kika shagala nace maryam ce na kira muke waya don naga bata shigo ba yau tasan kuma mun dawo.
Tana fada maki ke nan wanan satin za a je zancen su ko ban bashi amsa ba nace sannu da dawowa don ban yarda yaji akan may muke magana.
Jin bai amsa ba yasa na dago kaina ina kallon shi shima kallon nawa yakeyi nace lafiya kake min wanan kallon ko wani laifin nayi kuma ?
Ba tare da ya amsa min ba shima yace wai may kika ci haka a gidane kika bun kasa da yawa kin wani koma wata big madam dake , ?
Kallon shi nayi ina murmushi nace kila dai idon ka ne ya gane maka hakan ni ban wani canza ba ai danaji a jikina ko ?
Kara matsowa yayi kusa dani yana gyara corth din shi daya rataya a kafadan shi da kyau yana wani lumshe idanuwan shi yace.
Kun gudu kun barni ina kewan ku daga ke har yaran ya fada yana zama a kusa dani nace ai gamu mun dawo ko har wani dadewa mukayi balle kace kayi kewan mu.
Kanshi ya dora akan kafada na kamar wani karamin yaro yana sauke ajiyan zuciya yace nayi kewan ki wallahi a kusa dani ban taba sanin dadin mata biyu ba sai wanan tafiyan da kukayi.
Najini kamar wani maraya can Deedar ajiyan zuciya na sauke tare da fadin kai yaya banda abinka kai dake da wata a gida shine zakace mun barka maraya kuma.
Tura fuskanshi yayi cikin kaina yana sunsunan dadaden man kitson da akai min kitso dashi tarre da rike min hannaye na.
Yace kowa da matsayin sa a gare ni don haka ki yarda dani I miss you kwana biyun nan da kukayi sosai wallahi.
Wani iri naji har cikin raina a lokacin ina mai jin dadin wanan furcin nasa a gare ni sai naji kamar ba wanda ya kaini a gare shi a lokacin.
Muryan shi naji cikin sarkewa yana fadin wanan kamshin naki yai min dadi wallahi yana kara dora kanshi a saman kaina yana shaka.
Kai na girgiza tare da kokarin jaye kaina daga gare shi ina fadin ka tashi ka watsa ruwa ka ji dadin jikin ka kada wani yazo nan ya samay mu a haka kuma.
Korata kike yine daga nan da sauri nace don may zan kore ka gani dai nayi ka gaji kana bukatan hutu yanzu kafin a kira sallah.
Murmushi yayi tare da mikewa tsaye yana gyara kayan jikin shi da suka dan takure daya zauna ina mamakin yawan tsabatan shi har nakan yi tunane wai yaya yake da matan shi masu kazantar tsiya ?
Mace tun zanin safe dashi zata wuni a jiki wata kila ma ta kwanta haka dashi don ko washe gari dashi zaki ganta ta tashi.
Muryan shi ne ya katse min tunane na da yace may zan samu inci ne yau tun safe rabo na da saka wani abu a cikina dana sha dan cock .
Nace abinci na nan na girka ma sai dai idan wani abin kake so kuma a dafa ma yanzu yace zan dan sha tea kadan idan zan samu kafin anjima inci abincin don hanji na ya warware.
Nace barin kawo maka kafin ka fito wanka yace dakin kyauta min ya juya ya fice daga dakin ajiyan zuciya na sauke bayan fitar shi dakin.
Wai yau nice AA ke fadin yayi kewan mu da bakin shi yake fada min hakan tare da nuna min da gaskiya yake fadi yadda naga jikin shi yana mutuwa dan zaman da yayi a kusa dani.
Mikewa nayi zuwa kitchen na hada mai ruwan tea tare da daukan kayan na nufi part din shi baya ciki yana bayi sai kamshin mai dadi ke tashi a dakin.
Kayan daya cire na kwashe na aje inda muke aje kayan dauda ina shirin fita daga dakin ne ya fito daga wankan muryan shi yasani juyowa yana tambayan ina tea din yake ?
Nace yana dinning na aje ma nan zaki kawo min in sha yunwa nake ji sosai nace kai mai mata har uku biyu a gari zaice yana jin yunwa haka.
Kallona yake mai kama da harara na fice ina dariya yace zaki dawo ai yana murmushi na dawo dauke da kayan a gaba shi na hada mai komai ya zauna a bakin gado ya na sha muna dan taba hira sama sama.
Na dauka Nafisa zata shigo tace na shiga mata lokacin ta duk da saura yan mintuna lokacina ya cika sai dai banda yadda zanyi dole in bi umurnin shi.
Na mike bayan ya gama sha ya miko min kofin yana fadin yagode sai dan zufan daya fara tunane nayi nace wai ita wanan wata irin mace ce da zata bar miji haka ya zauna da yunwa.
Allah kadai yasan yadda yake zama da yunwa da take ita kadai a gidan gasu da yawa saidai yawan ya zama na banza gareshi don babu mai iya dora abinci idan ba yunwa yaci su ba sun kwamce suyi tashan ruwan bakin shayi.
Ina fita ya sauke ajiyan zuciya tare da tunane a ranshi irin saukin kan dake gare ni a dai barni da fadin magana ko yaya yazo min a bakina kuma yanzu ya saba da wanan.
Wanda maganan nawa daidai yake da amsan abinda zaka fada min sai dai ya lura yanzu ina dan rage yaba magana kamar da can baya.
Daki na koma na kara shiyawa don yau nasan zan dadana kuda na a wurin shi yadda yake mazarin nan akaina sai Allah.
Ana sallami isha,i ya dawo gida ranan shiya kirani da kansa kwaliya na caba sosai kamar mai shirin fita wani wuri a lokacin.
Na dauki kayan abincin shi zan fita Altine ce ke min wasa wai su rufe kofa ne na tafi ke nan ina dariya na juyo nace lalai kan idan kunji shiru ku rufe.
Zaune yake a dinning din tunda na shigo ya kura min ido kamar tsohon maye har na iso gareshi da sallama a bakina.
Kallona yake tundaga samana har kasa ya dawo da idon a fuskana na fara gaida shi da wuni ya amsa min tare da fadin in kama maki ne.
Ina iyawa na bashi amsa na aje kayan tare da jan kujera daya na zauna akai nace may zan fara zuba maka bayan na gama jera mai abincin .
Yace koma may na samu don yau ina son in cika cikina da wanan girkin danayi missing na kwana biyu daga nan sai in dora da abinda aka hanani din dazun.
Abinci kadan na zuba mai don nasan ba zai ci ba tunda yana ganin naman kai a gaban shi don yana son shi sosai da bindin sa.
Plate din abincin ya jawo a gaban shi yana fadin kin kara kyau sosai wanan kwaliyan kamar mai zuwa buki nace bako bukin zan tafi ba duk wanan kwalliyan don ka nayi ko zan koma amarya yau.
Kai ya gigizs yana fadin har kina tunanen komawa wata amarya ce ke da kulun sabuwar amarya kike a gurina ban taba ganin macen da ta haihu ba kuna komai nata yana nan a yadda yake.
Wani kallo nayi mai nace dama tunanen ka ke nan ashe barin kara zake damtse na furin gyara kada watarana kaga gazawana .
Ban tunanen akwai wanan ranan a rayuwana ya bani amsa yana debo abincin sai naga ya dan tsaya yana dube duben hannun shi can ya girgiza kai yakai loma a bakin shi tare da bissimillah.
Ashe aune abincin yakeyi ko nima na masa wani sihiri sai baiga komai ba don yanzu tsoron kaidin mata yake gaba daya ba Nafisa kawai zata iya mai sheri ba kowane akan wanan.
Yana ci muna hira wanda hiran akan yan uwanane yake tambayana a cikin hikima nan yake fadin na hana Alkasim din ki komawa ne don a sama mashi aiki ya fara daga baya sai ya koma ya karo karatun shi.
Naji dadin jin wanan maganan don zan su mutanen da muke tare da dadewa suyi alfahari da samu na nima a duniya tun yanzu.
Bayan ya gama na kwashe kayan zuwa part dina na rage wanan kayan zuwa kayan barci na gyara duk wani sassan jikina nayi masu saida safe na fito.
Yana kwance yana jira na ban bata lokaci ba wurin ba bori kai ya hau ranan nice na nuna masa gwanintana ya rasa duniyan da yake ciki sai wani lokaci muka sarara ma junan mu nan ma bamu kwanta ba hira muka dasa akan bukin da zamu tafi.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/23/21, 7:58 AM - Fatima Amarya: Mamaki nake a raina yadda naga Nafisa ta koma wata saliha a dan kwana biyun gashi kuma ba wani hurda dake hadashi da ita a gidan.
Rana girkin nafisa ne duk da na saka mai abinci kamar yadda ya umurce ni sai dai ban kai ba har karfe tara na dare sai ga wayan shi ya tambayan abincin shi.
Dan jim nayi kafin in ce ina zuwa bayan wayan na mike na dauki basket na nufi part din shi a falo na wuce su suna hira na hau sama wurin shi da abincin.
Kallon mamaki ta bini dashi har na shige waya ta dauka ta kira Sabuwa tana fada mata cin fuskan da yake shirin mata don ita a zaton ta har da kwanan ta ya bani duka.
Ki bishi a sanun mu gane mai yake nufi da dakatar dake da yayi a girki tunda bamu san manufar shi ba kan hakan yanzu.
Kuka ta saka mata tana fadin sabuwa Samad ya cuce ni idan yace haka zai min yanzu kan wanan yarinyar baya ganin kowa da mutumci sai ita kadai a gidan nan ga laifin nawa har yana son shafuwar ya ta yanzu don har ihisan haushin ta yake ji gaba dayan mu yanzu.
Ke ma kin san wanan aikin asiri ne idan tace tanan harda yara zata hada sai muma mu koma kanta da yaran ta ga baki daya mu zuba mu gani.
Sai dai ke ma kina da laifi Nafisa don may zaki haifi ya kuma ki nuna mai kina kyamatan ta haka a fili ko Allah zai iya jarabtan ki kan wulakanta wanan yar da kika yi ai.
Sabuwa na kasa saka yarinyar a raina don zuciyata ta kasa hakkura da ita a matsayin ya ta ki duba yadda yaran nan nata yanzu suke tasowa a gidan nan kamar wasu diyan turawa dasu .
Shegu ko kaine wa bakai masu kallo daya ka kawar da kan ka garesu saboda shiga rai da yaran ke dashi farat daya na rasa gane wa suka biyu da wanan kyau din cikin uwar da uban.
Nakasa shegu zamuyi su koma abin kyamata suma ga jama, a ba tana sallo ta haifi na miji ba mu kai dan banza a sakar mashi illa a rayuwan shi.
Yadda uban ma zaiji dan ya fita rashin gaba daya kinga dake da ita mai kurin tana da namiji kun zama daya ke nan sai dai idan samad ya mutu a yanzu kan dan ko mun nakasa shi tafiki kaso a gidan.
Nan dai sukai ta kula sheri wanda kullun cikin kulawa suke basu ganin alfanun shi kuma bai sa sun daina abinda sukeyi din ba.
Tunda na shiga falon na aje mai abincin tare da gaida shi da wuni na juya zan koma part dina naji ya ce dani dawo ki zauna har in gama ki tafi.
Wani kallo nayi mai a cikin mamaki ya sake fadin ki zauna nace in gama ko nace amma kasan in munyi haka mun wuce gona da iri don ba hakki na bane yin hakan.
Babu ruwan ki umurni na baki ba neman ba,asi ba ko wani dogon bayani ya fada don katse wani zance daga gurina din .
Don dole na ja kujara na zauna ina fuskantar shi yana cin abincin ba tare da wani yayi magana a cikin mu ba.
Na yanke zan tambaye shi may ye dalilin sakani yin hakan bayan ya san banice da alhakin kulawa dashi ba ranan ina yi ina dan satan kallon kofan

136 / 144

Chapters