MIJIN BUZUWA complete Hausa Novels.txt

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   87 / 144

258K to 261K   out of 431K words

abinda kika ci idan zan dawo zanzo maki da maganin ulcer din kisha mu gani nace nagode .
Yace Ok bye bye take care nace nagode I will ya kashe wayan maryam tana zaune ta kafa min ido sai da naje wayan tace dani.
Karfa kisha magani khadija azo ana magani daban ciwo daban nace yau na fara wanan kuma maryam don Allah bari zancen nan inani ina ciki yanzu ai abin zai min yawa.
Ok kina planing ke nan nace akan may zanyi planing maryam don cikin wai na masan ba zan yi shi a yanzu ba tace ok tana dan murmushi.
Kafin ya dawo yai min kira yakai uku tare da tambayan har yanzun maryam din tana tare dake dai ko nace eh ai anan zata kwana.
Warin tafarnuwa nake ji har cikin part dina da ake girki dashi a part din nafisa yake shigo min a part dina sai ya saka zuciyana wani irin tashi dole na mike ina cewa maryam don Allah mu shiga daga ciki.
Sai dai ban fada mata may nake ji ba wanka nayi nayi sallah ina sallamay wa na haye gado na kwanta abina.
Bai shigo ba sai nine na dare ya shigo dagani ko part din shi bai je ba a dakin ina kwance maryam zaune tana karatu ya shigo..
Gaisuwa sukayi da maryam din tare da tambayan ta jikina tace da sauki ulcern ai ya fada mata tun dazu barci tace tanaji yanzu.
Wurin gadin ya nufo maryam ta mike ta fita daga dakin kafa na ya ja na falka firgigit ina kallon shi sai kuma na dan sake murmushi tare da fadin sannu da dawowa.
Zama yayi yana fadin ya jikin naki naji sauki na bashi amsa yakai hannun shi saman wuyana yana dan tabawa tare da miko min maganin ulcer masu tsada a leda na karba ina fadin nagode.
May kikaci yanzu ya tambaye ni nace tea nasha da cake wani kallo yai min yace may zakuci a samo maki yanzu nace sai dai maryam amma ni na koshi.
No yace yana mikewa tare da fadin barin fita yanzu idan nayi wanka kada ku rufe ku jirani in dawo nace a dawo lafiya ya fita.
Falon na tashi na dawo na samu maryam din bata nan ashe tana dayan dakin ta kwanta nan na samay ta kwanta na shigo na samay ta na zauna.
Hiran anty salbiya muka dauko take fadin naji maganar mamaki yau ai watau dai ita mace da bauta aka santa a rayuwanta.
Da zaran an daura ma aure baka da wani lokacin kan ka isashe a gidan ka saina bautan miji ke nan wallahi khadija ina fanin kokarin ki sosai.
Ni dake tare dake kadai nasan wanan amma gaskiya kina kokari sosai don ba za a dauke a karamar jaruma ba kan don ko zama gidan nan ai sai mutum ya shirya.
Amma ke gani zaune ba abinda ya damay ki murmushi nayi nace to maryam yaya zanyi abinda yafi karfin ka ai sai ido.
Tace hakane mun kai kusan awa biyu da wani abu ya shigo dauke da ledoji a hannun shi ya miko min tare da fadin.
Kici kisha magani don Allah maryam ki tabbatar da ta sha maganin nan kafin ta kwanta don nasan ta da tsoron shan magani .
Tace zata sha ya dan lakato min hanci na tare da fadin raguwa kawai ji yadda kika fada yau kawai da dan ciwon nan .
Nace yau dai ka sani amma ni na dade yana damu na ai yace to asibiti zan kaiki gobe idan Allah ya kai mu ko yanzun ma don dare yayi ne da munje.
Ya fita yana muna sai da safe muka karba da Allah ya bamu alheri na mike nabi bayan shi don rufo kofa maryam ta nufi kitchen bai fita dakin ba sai da ya dan matseni a jikin shi na zille da dabar na samu ya fita na rufe kofan ina dariya.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Tunda ta shigo gidan ta dan zauna falo tare da tambayan su abubuwa na gidan kamar yadda take masu dan kwana bibiyu .
Hankalin ta ne ya koma kan abinda take son yi tsam ta mike zuwa dakin ta ta barsu a gurin tana fadin zan shiga ciki in huta ban son damuwa yau.
Sun san idan ta fadi haka tana son kebewa ne ita kadai shigan ta dakin ta daga gado ta jawo ruban da ta saka dan bakan da ta haka muna.
Yana nan yadda ta ajeshi sai dai yayi wani abu kamar hunhuna ya shamuke ya bushe sosai ba yadda ta saba ganin shi ba.
Ganin shi a hake yasa tasan daurin da tayi mai yana nan yana aiki a kan mu ke nan ta sauke wani shu,umin murmushi ita kadai a dakin.
Ta mayar dashi dakyau bayan ta kakabe abin yadda ta saba aje shi ta aje tana fadi a zuciyar ta shegiya dangin makwadaita a haka zaki kare a gadin don nafiku maita wallahi ga abinda nake so.
Ba zan zauna ina kallo kizo ki mun kutse a gida ba kiyi yarda kike so sai dai ki gaji ki bar min gida yar iska yarinya kawai.
Gyara kwanciya tayi tana jan tsuki duk da abinda samad din yake mata akan wanan yarinyar da take ji kamar ta shake yar banza ta huta da bakin nacin yarinyar.
Lalai ya zama dole yau su kasance tare da samad ba zata tsaya wani bin dokar likita ba can ita da ko haihuwa tayi da anyi suna take like da mijin ta yanzu za, a kawo mata wani sharudda a kafa mata.
In banda wanan yar banzar yarinyar da tai mata shigen bazata a rayuwan samad har ake wani wai raba kwana shi kuma ya biye mata ina zata iya hakkuri dashi haka, .
Yanzun ma tasan don yakan dayi wasanni da yarinyar ne amma ai ba dai a cikin wani gamsuwa ba tunda tasan ta gama daure shi ta ko ina.
Don har yanzu idan sunyi fada yakan dawo ya lalashe ta su koma daidai ta sauke murmushi tana gyara kwanciyar ta tasan babu wata mace da zata shiga rayuwan shi ya gamsu da ita idan ba ita dai Nafisan ba.
Itako indai tana jin dumus a hantu da account din ta ai komai zata iya yiwa samad din don a zauna lafiya bazata taba yarda wata ta kwace mata wanan dama nata ba har takai ga lasan zuman shi.
Haka ta wuni a kwance duk wani shiri tayi shi a gurin don daren yau tana son ta kasance tare da samad din tane saboda tayi kewan shi sosai.
Da dare bayan ya dawo ne yakai muna kaji da drinks da sauran tarkacen ciye ciye ciyen da ya sawo muna ya dawo falo ya dauki nata ya nufi dakin ta dashi.
A kwance ya samay ta tana waya a cikin yaren su ya fahinci da mutanen su ne take waya a lokacin wanda idan ta fara wayan ba kasafai take aje wayan ba.
Don haka ya a je mata ledojin yana shirin juyawa ya fita ta katse wayan tare da fadin ina kuma zaka again yace daki zan koma ga dan abin tabawa nan na shigo maki dasu ya sake juyawa kamar zai fita daga dakin.
Amma kasan a nan yau zaka kwana dai ko wani kallo yai mata kafin yace kin manta cewa kin kashe wanan ranan da na kwana a dakin Deedar don wani dalili.
May kake nufi da fadan haka amma kuma ni kasan dalilin kwanan ka anan yanzun ai akan matsalana ne ko ?
Wani matsala ina kin samu lafiyan da zaki iya hawa sama yanzu tunda har kina iya hawa ki tafi yin masifa sai zuwa kwana gurina ne zai gagare ki kuma ?
Ban gane inda maganar ka ya dosa ba fa kana nufin don na hau ranan shike nan ina da karfin hauwa ko yaushe.
Yace wanan maganan haka yake a zuciya na don ba zan zauna in tauyewa diyar mutane hakkin ta ba ko yaushe a kan ki ba.
Wani hakki take dashi a kanta idan ma kun kwana din wata tsiya take iya tsinana mata bayan bakar fitinar da ta shigo muna dashi gida tana kokarin mai dakai mace mara amfani ga mata.
Wani kallon mamaki yai mata ya bude baki zai yi magana sai kuma ya fasa fadan abinda zai fadi din yadan girkiza kai ya juya tace dakai fa nake magana.
Yace naji ki kuma naji abinda kika fada ai koma bata yi min komai amma ai dole in tsare mata hakkin ta ko.
Tace tunda kai ka zama dan son ba mace dadi ta ko wani hanya ko to wanan dai ka sani bazaka taba jin dandanon ta ba har ta gaji ta fice don nan ba gidan zaman ta bane.
Yace da kyau kinyi kokari kin san sheri da kikayi ke nan shiya sa kike fadar haka ko wani lokaci ashe , ?
To koma may ye haka naganta nake son zama da ita ko da ko bazan taba more mata din ba balle ma ina morewa a wanin fannin.
May kake nufi ta waro ido waje yace kwana da ita da nake yi ina jin kamshi don ta iya gyaran jikin ta a gurin miji ba sai zata fita take gyara ba.
Ga kuma girki da ladabi da nake samu a gurin ta ga natsuwa da sanin ya kamata da wanan halin kike son in barta haka ba tare da kulawa ba.
Ai kema ki mata adalci mana wanda ke baka wanan abin ai bai kamata ka wofunta shi ba Nafisa .
Kema da zaki daure ku hada kai ku shirya da ita nasan da kin karu da wasu daga cikin ni,imomin ta ai.
Samad ta kira sunan shi da karfi tana fadin agabana kake lissafo min wai abinda kake ji a kishiya ta .
Wallahi maganan nan naka yanzu yasa nake jin kamar in shake yar iskar yar banzan yarinyar nan ta mutu kowa ma ya huta shegiya diyan makwaidaita kawai.
Wani murmushi yayi yana fadin dama na fada maki kadan daga abinda nake samu a wurin ta ne don ki ji haushi kema ki gyara halin ki.
Don duk waban abinda na lissafo Deedar dashi Nafisa baki da ko daya a gurina da sunan kinayi miji yaji dadi.
Filo ta dauka ta jefa mai ya cabe tana dube duben wani abin ta jefa mai ya fice dakin yana dariya samun sa,anta da yayi har taji haushi.
Muryan ta yaji tana fadin zanzo dakin in samay ka ai yanzu kafin da safe ita kuma yar banza in san abinyi akan shegiya.
Kafin tazo ta hanashi hutawa ma ya sa ma kofar shi key ya rufe ya zauna yaci dan abinda ya riko ma kanshi ya kwanta tunda ba girki take mai ba sai sa,a .
Kuma ko tayi ba iya ci yake yi ba don abincin baya gamsuwar shi a bakin shi yasa kullun gikin ta dole sai ya samu wa kansa dan abinda zai ci.
Taje dakin nashi kamar yadda tace ta samu kuma arufe ta soma buga kofan da karfi tana kiran sunan shi ta yarda kowa zai iya jin ta.
Da fushi ya zo ya bude mata dakin ta shiga tana huce ta fara fada dashi akan may zai rufe mata kofa tunda yasan zata shigo.
Ko don yaki kwana a dakin ta kuma bai barta da takaicin hakan ba ya fada mata magana son ranshi ya fito yana zaton zata kyale shine wanan karuwan gidan nashi ta shigo inda yake.
Dariya maganan yaso bashi yace yanzu dai ba kinzo ba may ye kuma nasai kin zagi diyar mutane a cikin maganan mu.
Hararan shi tayi tana kaiwa kwance tace idan ba ka sallami wanan yar banzan ba kaima kasan ba zaka taba samun kwanciyar hankali a gurina ba ai.
Don na tsani na bode ido naga wanan yarinyar a gidan nan kuma kasan ba haka mukai alkawari da kai ba tun farko.
Yace da na aure ki munyi rijejeniyar ban kara aure ne ko may ko yanzu wata zan karo idan naga wace tai min ita ma na fada mata hakan ta kuma sani.
Aure fa kace zaka kara again yace kwarai kuwa Nafisa ina son in gado mahaifina kuma inyi koyi da sunnan ma,aikina ne.
Tofar da yawun ka akan wanan magana ko wanan kul ba dade kul ba jima sai ta fita gidan nan ina fada maka kana dauka wasa ne.
Yace ki tabbatar da ranan tare zaku fita da ita don son ta nake na auro ta haka kema so da tausayin ki ne yasa na aure ki ai.
Shiru tayi ta bashi baya tana tunane a ranta ya dauka ma tayi barci ne sai can yaji tace wai samad may kake nema ne a gurin wasu matan wanda ni banda shi a tare dani .
Yace kina da komai na mata Nafisa amma kuma ai kin sa ra,ayin maza ne haka akwai wasu abubuwa da namiji kan hango gun mace yaji yana son kasancewa a gidan shi da ita.
Banga abinda wanan da ka kwaso zata nuna min ba yace a naki ganin ke nan amma tana da quality din da nake son mace ta kasance dashi.
Haushi maganan shi ke bata idan taji yana fadin magana a kaina don haka ta kyale shi ba tare da tai magana ba.
Kwanciya ya gyara ya kwanta sai saukan hannun shi yaji a ga jikin shi murmushi yayi tare da fadin kin san kina cikin dokan likita dai.
Tace likita shi Allah ne ko ubana ne da zai kafa min wani doka yau na fara cikin in kwana tare da kai ko mai.
Da zamu tsaya bin wani dokan shi can muki farautawa ran mu abinda muke so ni tsausayin ka naji tunda nasan kana bukatan hakan kaga nazo da ba haka ba sai in kyale ka da wacan mara moriyan inga iya gudun ka.
Sai dai ina gudun kaje wajen wata kayi abinda ka kasayi a gidane alhalin ina nan ina da abin a jikina nima.
Har suka gama abinda zasuyi yana mamakin karfin halin Nafisa da bata iya boye zuciyar ta ko kadan don ta fito fili karara ta nuna ita ke da hannu kuma bako shakkan fadin hakan da takeyi.
Yanzun ita a zaton ta ba abinda ke shiga tsakanin shi da Deedar yake zaune haka da ita don haukan ta da zafin kishi ya hana ta kwantar da hankalin ta ta fahinci komai akan haka.
KHADIJA
Mun tashi mun yin sallah akan lokaci sai dai bamu kara kwantawa ba don nemawa cikin mu abinda zamu ci.
Yau tunda na tashi da kewan yan uwa na da iyayyena na tashi har na kasa boyewa nayi wa maryam magana a kan su.
Tace ba kuna waya ba nace ba kullun ba don daddy ya kafa muna dokan kiran su ko yaushe yace idan suna son magana damu su zasu kira mu.
Maryam tace kai daddy ho wallahi da daddy ya fito cikin mutanen da, da yayi tsanani sosai nace ai ko yanzun ma akwai tsanani don duk da aure muke bai hana daddy kafa muna doka ba kuma dole mu bi.
Tace ina son irin su daddy masu tsayawa tsaye a kan iyalin su amma wanan mazan yanzu ai adaiyi dai ne wallahi.
Kamar kin sani abinda nake tunane ke nan irin du AA ai ko tarbiyan yaran su basu da lokacin bayarwa kullun ana gurin aiki.
Tace ashe kema kina wanan tunanen nace ba dole ba maryam tunda ruwa ya gaurayu da jini yanzu ke dai Allah ya shige muna gaba kawai.
Tace AA fa saukin kan shi ne yakai har wanan matar ta samu wuri haka wallahi irin su basu damu da matsa ma iyali ba komai akayi mai kyawo ne hali ne na rayuwan turai kowa na da independent din kan shi.
Nace halin banza ba maryam mutum ya yarda addinin shi da al,ada ya kama na wasu shi abin nasa ma har yai yawa wallahi.
Da na dauka diyan Fati kawai yake kin kulawa sai yanzu nake fahintar ko yar nafisan ma ba wani damuwa yayi da ita ba iyakan shi da ita ya dan kama mata hannun yai mata wasa a tsatsaye ya wuce.
Niko kin ga ba haka na saba dashi ba duk tsananin daddy da kike gani wallahi yana da lokacin iyalin shi maryam idan kin gan mu dashi zakice ba shi bane.
Sai dai idan kayi ba daidai ba yanzu zaka sha hukuncin da bakai tsammani ba a gurin shi komai girman ka kuwa.
Mun karya mun shirya har lokacin bai shigo dakin ba waya na dauka na buga mai ina sallama ya amsa min tare da fadin Deedar kun shirya ne ?
Na amsa da eh tun dazun kai muke jira wallahi yace sorry dear wallahi yau na dan makara ne amma gani nan fitowa ku bani minti goma.
Kallon wayan nayi na kashe maryam dake jin abinda ya fadi tace yau ko dai buzuwa ta murda kambun sarauta ne haka ?
Tsuki nayi ina saka wayan a cikin jakka na tare

87 / 144

Chapters