MIJIN BUZUWA complete Hausa Novels.txt

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   75 / 144

222K to 225K   out of 431K words

nan duk wanda yace zai rabani dashi ai ya samu mai shi.
Dan zaman weekend din nan da mukayi a tare na fahinci AA mutum ne mai saukin kai sosai ashe yana da addini sabanin yadda na dauke shi lokacin sallah nayi bai bari ya wuce mu.
Nafisa ko tun lokacin da suka gama rikici ta dauki motar ta zuwa gidan madam uwar daba mai arna ta samay ta da wasu kawayen su biyu suna hiran nasu kishiyoyin sai gata.
Yanayin ta kawai madam ta kalla ta fahinci tana cikin wani yanayi ta ta fahinci sunyo tsiyan a gidan ta tare ta da fadin yau mutumiyar da wace aka tashi kuma.
Don yanzu gidan ki ya zama gidan danja kulun fitina ne ba daga kafa zama tayi tana jan tsuki tare da fadin ba dole ba wanan matsiyaciyar yarinyar kamar mai ira,izai da ke ture min shiri na.
Au har kin manta da abinda na Mando ya fada muna ranan cewa tana da masu kariya sai munyi da gaske a kanta.
Naga alama tace wai duk kudin dana kashe akan yar iska abin bai yi ba na tura yanyala ta turara yar iska ta baya sai gashi ita ta fito ta gaba tana turarani a gidan.
Ddon iskancin yanyala kuma a gaban idon su Ihisan taje yin abu sai gata wai taji kamar tafiya a bayan ta taje waigawa ta fadi duk ta kuje kanta ta kone.
Dariya sosai suka dauka ita ko tasha toka don bata ga abin dariya ba anan taci gaba da fadiin na nuna mata na gane turaren da take yi sai gashi ya fito kamar zaki yana tambaya shi a dole mai lalashin ta kada ta gudu.
Ba sai ga ihisan ta fito tana fada ma uban abin da Yanyala taje yi ba ta fadi yau ai ba karamin rikici muka kwasa dashi ba a gidan.
Sai dana murje mai ido kada inji kunya na dinga zabga masifan karya sanan ya rabu dani ai da ban san inda rikicin zai tsaya ba.
Dayar matar dake zaune hamshakiya ne ta karbe maganan da fadin kin ga irin abinda yasa ban tura kowa yai min aiki ni nake abina da kaina ba tare dana saka wani ba yaje yai min shirmay.
Tace ai dan ba kari mutanen banza ne wallahi ace dan karamin aiki haka sai mutum yayi shirmay a cikin sa wai fa yau sai kusan goma suka fito daga kwana.
Matar guda dake ta faman kada kafan ta tana jin mulki ta amshe da fadin wuri kika basu wallahi ni akawi yar iskan kishiyar da zata kai ko biyar na safe da miji a daki.
Ai da ranan sai tasan ta shiga hurumin da ba nata ba a gidan nan sai na saba mata kamar yadda ta saba min sai dai suyi tsiyar can a sace ban gani ba.
Ke in fada maki ma fa dayar ma sai idan bani gari yake samun sakewa da ita idan ko ina nan basu isa ba wallahi har shi din.
Hankalin Nafisa ya koma wurin mai maganan taji kamar ace itace ta samu irin wanan irin mulki tace haka nake so wallahi yar uwa.
Tace a mai za a fasa mutuwa ko hisabi ni ban daukan raini ga kishiya wallahi balle su duka ukun na girmay masu ga shekaru mijin ma kanshi na girmay shi balle su.
Kina nufin dama sune a gaban ki ta tambaya cikin son karin bayani gare ta tace wlh in fada maki ina ganin shi yai min kawai na aure shi duk da shima yana da abin hannun shi do ya fini nisa ba kusa ba gaskiya.
Badai haihuwa yanzu nake nema ba sai rufin asirin don haka nake juya su yadda raina ke so a gidan ba wace ta isa ta mai tak a cikin su tayi waje road.
Don wace nake bi har ta gwada min iya shege nasa miji ya yanka mata jan kati sai gidan su sani Allah sani Annabi ta samu ta dawo cikin yayan ta.
Madam tace amma sai da kika bari kikai nazarin su kafin ki fara aiwatar da shirin ki ko tace sosai kuwa da farko ai da fuskan musulma nazo masu.
Nice son diyan su nice nuna masu ban damu da miji ba nama fisu son kan su da sauran abubuwa sai da na gama karance su tsab na fara fito masu da kalata.
Da uwargidan na fara don na jata a jikina sosai naji komai na gidan da yadda yake guda ai in fada maki akanta na fara ranan.
Ba baki don ta gama fada min duk sirin gidan na sani kuma tana jin kunyar aji a gurin ta naji komai dole sai lalabawa da biyayya gare ni.
Madam tace to abinda Nafisa bata iyawa ke nan na fada mata ta nasu ta gama fahintar ida suka dosa amma ta kasa hakan don kishi.
Ai in kina son ki san kan gida kafin ki fara aiki fara kama kan uwar gida je mata da fuskan musulma ki nuna kina ra,ayin ta kina tausayin ta yanzu zaki fahinci komai a wurin ta.
Don su gani suke cutar su miji ke yi ko yaushe yafi maida hankali ga amare basu san duk kanwar jace ba kishiya kishiya ce ba mai son taga yar uwa tafita ga miji.
Kai Nafisa ta gyada tare da fadin ni gaskiya ba zan iya jan kowa a jiki na ba duk daya na dauke su ai kafin in zauna da amaryan da uwargidan muka fara.
Wanan fa irin kishin kasar su tazo muna dashi nan bata san abin ba haka yake ba a nan sai ka hada da kissa da kisisina da kutungwila zaka ci riba.
Nafisa tace gaba daya nike masu bugun diyan kadanya don ban yarda da kowan su ba ni mijin nake son in kama ko ta halin kaka abin ya faskara gare ni kuma.
Sai naga kamar zan kama shi sai abu yazo ya jagwule min daga baya yanzu fa yan kwanakin nan samad bai jin kunyar fadin mu bar mashi gida dani da yan uwana.
Matar tace duk ke kikaja hakan tunda ya riga da ya fahince ki baki kaunar ko daya daga cikin su don may zai zauna zaman goyon bayan ki koda yaushe.
Bafa ko yaushe asiri ke tasirin akan mutum ba madam ta karbe da fadin shi nake fada mata ai bata gane ba.
Matar tace kamar ni nan ai da farko wani na samu na kamashi a hannu wani last done ne wallahi har ina ganin na kama shi ashe matar shi ta fini iya duniya.
In fada maki tana ji ba ai sati ba ta shiga ta fita sai batun kake ji yar iska ta kama abinta tamau ta rike ai ke madam kin san labarin don da ke mukai ta bugawa a lokacin.
Madam tace kwarai kuwa na sani Hauwa black yar jos ko kin san har yau kuwa a kule take damu ranan mun hadu a gidan buki baki ga yadda take wasa da naira ba tana muna hura kai.
Ba dole ba yar iskan mata miji ya rike mata kan maciji tana wasa da bindin shi duk tarin dukiyan shi fa ita kadai ce matar shi har yanzu gashi matashi mai ji da lokaci.
Kedai bari yar uwa yanzun ai ba a sanya don wace za ka sama sheri ke da zaki shigo kuma da naki shitin ba, a shiga hannu sake yanzu kowa tsaye yake kamar laya.
Tambayan Nafisa tayi may ye matsalan ta yanzu akan kishiyar tane sai da ta rufe ido ta bude kai tsaye tace wallahi hajiya ni gaba daya naki jin kishine a rayuwa.
Don na kasa tsayawa in fahinci takon yar iska ai in san ta inda zan fito mata don yarinyar gata karamace amma akwai bakin wayo gare ta.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Washe gari bai so in shiga school ba wai sai na karkare murmurewa in fara zuwa rokon shi nayi ya bari in shiga don muna da test washegari tuesday.
Bamu hadu da maryam ba sai da muka fito sallah a zahar muka hade a masallaci da ita kallona kawai tayi ta kwashe da dariya.
Oh kinga abin dariys a jikina ke nan na fada a hasale tace ban gani ba sai dai kina dashi ne khadi daga dan haduwa guda shine har kika wani fada haka.
Kallon jikina nayi na tabe baki nace dama haka kike son gani aka hada baki dake ai wlh ki san da sani konci bashin haka a gurina sai na rama nima.
Yarinya ai sai dai ki ramay wurin ramawa nikan ai ba zanyi wanan rakin irin naki ba kin sani mun dauki lokaci a gurin kafin mu koma ciki.
Biyar da rabi muna fitowa motar shi na iso wa don haka ban samu kara kebewa da maryam din ba na wuce .
Tunda na shiga motar naga shi rai bace ban damu in tambaye shi ba don ba abinda ya shafi gida bane kila.
Mun dan taba tafiya kadan ne naji muryan shi yana tambaya maganan da ya daure min kai dagowa nayi ina kallon fuskan shi ya kara maimaita tambayan shi gare ni.
Nace ina kika je a Napep ke da maryam da bana gari shuru na dan karayi sai kuma nace ban je ko ina ba sai wurin gyaran kai dakuma shago na sawo kayan bukatana don banda mai sawo min.
Khadija kin ko san darajan ki a yanzu garin nan da zaki je shiga Napep da mutuncin ki da kimar ki na matar aure matar ma tawa .
Wai kin san wanda kike aure kuwa khadija idan ma baki sani ba bari yau in fada maki ni ko waye don ki sani.
Wanan aikin da kikaga ina yin shi nake don cika gurin iyayyena a yadda suke so suka kuma gina ni akai ina kokarin ganin akoda yaushe na farantawa iyayyena ransu.
Idan ba haka ba ba abinda zanyi da wanan aikin da kike gani inayi anan kin san wasan polo ko wasan kwalon doki da akeyi .
Kai na gyada alaman na sani yace to ina daga cikin wanda duniya ke alfahari dashi a wanan wasan kin san jackpot na girgiza mai kai yayi dan murmushi yace ki bincika don yafi komai kawowa rayuwana kudi sai dai banson yi idan ba yama min dole ba wanda idan na buga kusan duk abokan karawan nawa sai na doke su.
Ni business man ne ina shigo da karafuna da part na motoci a kasan nan sai dai duk inayin wanan ne a cikin boyen kurwa don idon jamma,a akaina.
Don Allah don Annabi for god sake mai zai sa kije shiga motar haya bayan na aje maki daya daga cikkin motocin shiga na a dinga kai ki duk inda kike so.
Ba wai naki saya maki mota bane tun kafin muyi aure ko mota nawa kike so a gare ni zan iya saya maki Deedar sai dai ina duban abinda haka zai jawo maki ne a gida da idon jamma,a.
Ranan da Nafisa tayi maki gori naji zafin abin don har barci abin ya hana ni samu issashe saboda raina da ya baci da zancen.
Don Allah may yasa kikayi min haka har yaron wajen aikin mu dashi da matar shi suka rage maku hanya yau yake fada min banji dadin jin haka ba wallahi.
Gyalen kaina na gyara tare da gyara zamana ina fadin ni kada kaga laifina akan hakan fa.
Yace a harzuke don may ba zanga laifin ki ba Deedar sunana kike son batawa a bugani a jarida anga matana a motar haya a garin nan.
Ko Fati da take cen duk inda zata da motar hajiyan mu take tafita na kuma kyaleta ne ban sai mata wani ba saboda careless din ta dayai yawa.
Don Allah ka daina zargi kan haka don ko ba laifina ba ka tambayi driver ka ko maryam zasu fada ma idan nice mai matsalan.
Motar da tun ranan da ka tafi iyakar mu da ita kenan a gidan ka ban kara ganin driver ba sai yau da muka fito din nan naganshi a waje yana noke kai.
A dai yi min munafunci ne don ba,a son aga kwanciyar hankalin mu tare da kai shiyasa ban bi ta kan motar ba na ci gaba da tsagogina.
Da ina da power a gidan ka ba za a hanani shiga motar ka ko taba kayan ka ba a gidan nan.
Shiru yayi yana saurarena har na gama san nan yace kina nufin hana mashi umurnin da na bashi akayi komay nace ai ka tambaye shi kaji daga bakin shi ko kuma idan baka yarda ba zaka iya tambayar maryam yanzu ma ba sai gobe ba.
Shiru yayi bai sake magana ba har muka isa gidan ban tsaya ba na kwashi takarduna zuwa ciki na barshi a motar ya biyo ni da kallo.
Part dina na bude na shiga har kullun baki na dauke da addua don nema tsari ga Allah har nayi sallah la,asar na idar part din shi na je na gyara na saka kamshi ko ina tare da wanke unders din shi na shanya mai ta bayan benen shi na fito zuwa nawa dakin na dora girkin abinda zamu ci da dare.
Ban sa lallai dole zaici abincin ba sai dai na girka dashine kawai don nice mai alhakin bashi abinci a ranan duk da ba wani girki mai yawa nakeyi ba.
Na gama na shiga wanka lokacin har magarina ya dan gwauta na fito na tayar da sallah bayan na gama ne na zauna na gyara jikina tare da hayewa saman gadona na kwanta.
Tara saura ya shigo part din nawa daga shi sai wandon crazy fari da farar riga armless ajikin shi sai kamshi yake zubawa haka yasa na fahinci yayi wanka ko a lokacin.
Ban daga daga inda nake ba ina kwance a yadda nake sallama ma dayayi ciki ciki na karba mashi ya iso bakin gadon ya zauna yana fuskanta na tare da cire min handout din da nike karantawa da na dora saman cikina ya dan duba.
Ba tare da ya kalle ni ba idon shi na kan takarda naji yace dani wai fushi kike dani akan maganar da nayi maki dazun ko may ?
Na dan juyo tare da fadin wa ni don may zanyi fushi tunda ina da gaskiya na akan may zan dauki zafi dakai kuma hutawa dai nake kawai.
Murmushi naji yayi tare da fadin ba gaskiya bane idan da baki fushi may ya hanaki zuwa wurina ki dubani ko ki kawo min abincina a can ko baki girka abincin bane ?.
Na girka mana nace dashi tare da kokarin mikewa zaune sai naji ya mayar dani a yadda nake kwance da ya shigo.
Ido na kafa mai shima haka sai nayi saurin jaye nawa idon daga nasa ina sauraren shi inji abinda zai fadi fuskan shi ya sauko zuwa kasa yana nufan nawa dashi.
Kokarin kawar da kaina nayi gefe sai dai ya riga kai fuskan shi din a nawa yana neman bakina ya hade da nasa ban samu kaucewa ba har ya kawo bakin sa a gare ni ya shiga tsotse ni tun ban biye mai har na fara biye mashi na fara mayar mashi da martanin abinda yake min din.
Mun dauki lokaci a hakan kafin ya sake ni ya mirgina gefena yana sauke numfashi a hankali dan gyarawa nayi tare da kokarin tashi saman gadon naji ya rike min hannu na.
Dole na juyo ina dan kallon shi kafin yace ina kuma zaki yanzu nace abinci zanje na hada maka kafin ka fito ko a nan zakaci yace dani duk inda kika bani a shirye nake inci banda matsala ga hakan.
Mikewa nayi zuwa hada mashi abincin a nan falona muka zauna mukaci tare dashi ina jiran ya kara min maganan shiga motar sai naga ya sake yana ta wayan shi ina zaune gefe ina kallon shi har lokacin da ya gama ya mike yana fadin bari in dan leka dakina sai kin shigo.
Don Allah dai ka barni in kwana a dakina mana tunda ka jagule ni ya juyo yana fadin wayo kima zaki min Deedar shiyasa kika taimaka min.
Nace na taimaka ka da may kadai jagule ni kaimin wayon manya kuma kace sai nazo dakin ka may nayi maki ai hakkurine wanan na soma baki don naga kina son fushi dani.
Sai da na karasa hada komai na bar dakin nawa na kashe wuta na fito tare da rufe part din na nufi wurin shi.
Koda na shiga dakin yana zaune a bakin gadon shi ya tasa laptop din shi a gaba yana aiki a cikin sa jin sallamana ne ya dan dago yana amsa min.
Dan zama nayi a gefen shi shiru banyi magana na sai ji nayi yace ina son shiga kaduna wanan satin in Allah ya kaimu.
Da sauri na nuna mashi farin cikina nace Allah sarki ashe anty Fati na da bako ranan don Allah idan an masu AFFAN hutu azo min dasu.
Yace idan nazo dasu ni yaya zakiyi dani ina

75 / 144

Chapters