Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MIJIN Buzuwa Complete Complete Hausa Novel by Nil

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   130 / 144

387K to 390K   out of 431K words

ku yau au har kirga kwanaki kika tsaya yi ke nan ?
Ban gane ba idan nayi hakan kuma laifi ne komay nace dashi a dan hasale don wani irin mamakin shi nake ji lokacin.
Dan kallona yayi kamar zaiyi magana sai kuma ya basar yace bashi na tambaye ki ba abinci nace ki kawo min dan Allah.
Nace ba laifin ka bane kuma banyi mamaki da ganin haka ko jin haka a gare ka ba yanzu don nasan inda ka fito ai.
Ina fadin haka na sa kai na fita daga dakin jikin shi ne yayi sanyi don yasan ban nuna kishi ba ga dawowan nasu tunda har nazo na tare shi da dawowa.
Amma shi bai san dalilin daya sa tun kan ya tafi baya kaunar gani na ba yanzu yasan ina iya kokarina amma shiya rasa laifin da nai mashi din yake jin haka akaina.
Ina komawa ina jin zuciyana yana min kuna na aje yaron na hada mai abincin nakai na aje mai nafito don yana daki har lokacin bai fito ba.
Na dawo part dina ban zauna falo ba na shige daki na da yasha gyara na alfarma wani iri nake ji kamar zuciyana zai fashe duk karfin halin da naso yi in dake a lokacin na kasa.
Zuciyana ta kasa daina tuna irin kallon tsanar da yake min tun kan yayi tafiya har zuwa yanzu da naje gaida shi din ya na min wanan kallon na rainin hankali.
Tambayan kaina nakeyi may nayi masa wanda ban sani ba may yasa bai min adalci ne idan halin shi na wulakanci ya tashi akaina ya kamata yai min uzuri ko don wani abu.
Hawaye naji yana silalo min a fuskana nace a hankali a fili may nayi ma AA yake son ya tsiro da abinda zai kawo fitina a tsakanin mu .
Why why duk hakkuri na da dauriya baka gani a idon ka ne share hawayen nayi da sauri na jawo waya ina neman layin tsoho bado in fada mai.
Sai da ya gama sauraro na yace kasa hadizatu kada ki damu da wanan don ba haka aka so ba a tsakanin ku kibi komai a sannu da yarda Allah duk wanan abinda yake ji a kanki zai daina jin shi.
Bafa karamin aiki akayi maku a gidan nan ba don har jaki baki da bakar akuya masu rai aka birne don ku aka hada fatar kura dana kare dana bakin maciji akai asiri dashi duk akan ku.
Ni kaina da nayi aikin cire kafin nan ba karanin wahala nasha ba a jikina don bakin Aljannin da aka turo yana maku aiki a gida.
Komai ya wuce da yardan Allah don ba karamin kwaran muka kwasa dasu ba a cikin daren nan danayi aikin a gidan naku.
Ki saki ranki ga kowa kada ki bari kowa ya fahinci kariyan ki har mijin naku da sauran wa yanda ke gidan kafin aikin mu ya shiga kansa.
Jin shiru ga almuru ya yayi sosai a lokacin ya fito a dininng din ya samu na jera mashi komai yadda ya kamata ya bude yaga sakwara ne a ciki.
Sai kulan miyan da ke dauke da dan ganye akushi yafi yawa sai nama dake ciki manyan yanka dasu sai kamshi ke tashi daya buda zama yayi ya fara diba yana zubawa a plate.
Ya fara ci a hankali yaji dadin girkin har cikin ranshi ya lumshe ido a hankali yaci gaba da ci ya kusa gamawa ne sai ga Nafisa ta shigo part din batayi wanka ba har lokacin balle ta canza suturan jikinta daya sha hanya.
Samad kai ka samu abinda kaci mu har yanzu bamu samu komai munci a cikin mu ba yunwa muke ji sosai wallahi.
Kallon ta yayi yace ba abin dafawa a shiyan ki ne yanzu tace da wanan gajiyan hanyar da muka kwaso zamu tsaya dafa abinci yanzu ?
Yanzu kai baga shi ka samu abinda kaci ba har don bamu da gata mu an barmu a zube hakana ni da tan uwa na.
Ya isa dan Allah ban son tsiro da fitina tun yanzu don Allah idan da tasan kina ci may zai hana ta baku tunda ta dafa abincin.
Yana fadin haka ya mike ya shige dakinshi ya barta a gurin abincin ta bude don yunwan da take ji gashi abincin yana daukan hankalin ta andade ba a gamu ba ta zauna ta cinye sauran daya raga tas har miyar bata bar komai ba.
Ta na isa dakin ta ta samu na aiko masu da nasu tace su samiha suci su kwaso mata naman ciki su saka guda guda a nasu suci ta zauna ta kara azawa a wanda taci din a wurin shi.
Sai da ta koshi nak tasha ruwa ta getse tace koma da ta zuba muna wani abu ba zai taba kama mu ba don don mun fi karfinta wallahi.
Yar wahala ina jira in huta ne in karbe yarinya na a gurin ta munafukar banza da wofi kawai wai ita uwar kinibibi da kissa itace gwanar rike mashi yara idan an barsu.
Yanyala tace ai Ihisan ta ban mamaki ji yadda ta nuna kamar ma bata san mu ba a gidan nan hankalin ta duk yana can gurin ta.
Ran Nafisa yai mugun baci tace ashe kuma kun lura da hakan nasan wani sheri tayi ma yaran ta raba ni dasu don ta gaje min su .
Idan da wanan Aljannar ce sadiya kawai ko kallon ta ba zanyi ba taje taita kayan wahala dama ni ban sata a jerin diyana ba can, don taulalin wahala ne kawai.
Yana zaune dakin bayan ya gama salolin shi ya dan duba laptop din shi ya koma saman gadon shi ya kwanta a rigingine yana kallon agogo.
Ba wanda ya shigo dakin a cikin mu har wanan lokacin wani zafi yaji a ranshi ita Deedar tunda ta fice bata shigo ba haka kuma Nafisa bata zo ba har lokacin.
May ye na fushi ga dan maganan nan yace to shima may yasa ya fada min wanan maganan ne don bai kamata ya nuna min hakan ba don ai kulawa dashi na nuna a fili.
Ya dan juya tare da jan tsuki yana ci gaba da tunanen shi sai ga Nagisa ta shigo dakin yana cikin yanayin jin komai bai mashi dadi.
Ya dan juyo ya kalle ta har lokacin ba wani wankan da tayi a jikin ta don yanayin ta kawai ya isa mutum ya gane hakan.
Zama tayi a bakin gadon tana fadin na dauka gajiya yasa ka barci ai ya katseta da fafin may ya hanaki wanka tun dazun da muka dawo har wanan lokacin ?
Ta kai hannun ta saman jikin shi da zuman taba shi ya gwauce yace cikin dakewa tashi ki shiga ki watsa ruwa tace bazan iya wanka yanzu ba don gudun daukan mura.
Kyaleta yayi dole suka kwanta haka na badon yaso ba sai dan tsamin daudan da takeyi sama sama don yanzu ya saba da shakan kamshi ga jikin mace.
Nikan tunda na koma part dina mukayi magana da tsoho bado naji wani kwarin gwiwa yazo min na fito nace akai masu abinci don nasan dare yayi ba zasu girka ba.
Tunda laraba takai mata abincin ta dawo nasa ta rufe part din namu bankara fitowa ba sai washe gari na shirya tsab na nufi part din nafisa na samay su kaca kaca a zaune.
Sai hira suke zubawa a cikin yare suna dariya nayi sallama na shiga gaban Nafisa ne ya fadi don gaba daya na sauya mata na koma mata wata hamshakiya dani a idon ta.
Sannun ku da zuwa nace mata tare da tambayan mutanen gida magana nake tana kallona a cikin mamakin sauyi na da yanayin magana na.
Na juya cikin wani tako da take ganin yanga da sallo nake mata na fice abina ta dade a zaune kafin ta sake wani irin ajiyan zuciya.
Tace duniya ku tabani idan ba mafalki nake yi ba don Allah yaushe nayi sake yarinyar nan ta zama haka a dan lokaci kadan a dan watan nin da nayi bana gidan nan.
Yanyala tace ashe bake kadai kikaga hakan ba nima mamakin sauyawan ta nake a raina gaba daya ta koma wata babban mace da ita.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/15/21, 8:23 AM - Fatima Amarya: Yayi mamaki da yafito ya samu breakfast din shi a dininng na aje mai komai na tafi koda ya sauko zuwa part dina ya samu duk mun fice a gidan kofa a rufe.
Ya tsaya yana mamaki inda mukaje haka ya kira waya bai shiga ba ya kira na Altine ya shiga yace Altine ina kuka ke kuka rufe gidan.
Tace muna nan makarantar su khadija suna wani taro ya kashe wayan tare da kutawa a fili ya koma part din Nafisa a falo inda laraba ta aje Sadiya tana gurin tana ta tsala ihu har zuwa wanan lokacin.
Daukan yarinyar yayi ya nufi cikin dakin nafisa dake kwance tana ramuwar barcin ta hankali kwance ya bita da kallon takaici tare da bugun ta yayi a hasale ta falka a gigice tana kallon shi.
Yace yanzu kin kyauta ke nan kina nan kina barci kin bar Sadiya ita kadai a falo tana ta faman tsala kuka baki damu da damuwanta ba.
Tace Sadiya may ye hadina da ita a yanzu ai na riga na mayar da ita hannun uwarta na ainihi ke nan idan ba diyar ta bace ta yaya zata rike min ita haka kawai.
Wa kallo yai mata na takaici yace Nafisa kina da hankali kuwa wai wanan haukan da kike yi a ina kika taba jin anyi haka ko duk jahilcin ne wannan ina laifin yarinyar nan khadija da ta sa hannu ta rungumay maki diya abayan ki tsakani da Allah.
Wani dariya ne ta sake tare da fadin kai may ka sani ta dai rike yar ta amma wanan mai zubin yan ruwan kan na yafe mata ita harga Allah.
Yace idan kin ce haka zaki yi kuwa ba sadiya ba har ihisan din duk a wurin khadija zasu zauna su biyu tunda ke baki da hankali nagane yana fadin haka ya fita dauke da yarinyar a kafadan shi yana lalashin ta zuwa part din shi.
Bamu dawo gidan ba sai after two ina saye da rigan mu na lauyoyi a jikina na tsayar da mota yana tsaye suna magana da Yusuf su Altine suka fito suna dauke da yarana.
Fuskan shi a kaina har na fito daga motar gaida su nima nayi kamar yadda su Altine suka gaida su sai dai ban tsaya ba Yusuf ne yace yau kin fara fitowa lauyan ki na ainihi ke nan nace wallahi kasan muna gab da gamawa yanzu ba hutu a gare mu.
Daga haka na shige abina Yusuf ya karbi mami hannun Altine mun shiga da gajiya a falo muka ya da zango dukkan mu.
Abinci muke ci ya shigo part din dauke da Sadiya ban dago na kalle shi ba yace tun dazun yar nan tana gurina da kyat na samu ta dan ja fida kadan.
Altine ku karbe ta ku bata wani abu taci don nasan yunwa take ji ga bata abinci da wahala Altine tace ba uwarta ta dawo ba ai an kaita da safe da zamu fita.
Fuska ya bata tare da fadin Altine ku barta a nan gurin ku don Allah fadin hakan da yayi yasa na dago kai da sauri ina kallon shi tare da fadin ta zauna a nan kuma bayan uwarta ta dawo.
Ina don uwar bata nan ne muka rike ta anan din yace kin ji magana na ai nan nake bukatan su zauna dukan su su biyun yanzu yana fadin haka ya juya ya fita daga dakin.
Bin bayan shi da kallon mamaki nayi tare da sauke ajiyan zuciya sai laraba ne tayi magana take fadin ina ganin dai wani abin ne ya faru akan yaran kun san ba kirki ne da ita ba.
To amma mama an taba yin haka don Allah ina don uwar bata nan ne na rike su a nan wurina yanzu kuma zai zo da wanan maganan haka.
Altine tace maganan Laraba ne dai dole akwai abin da ya faru nace ni gaskiya Anty matsalan gidan nan ya isheni haka wallahi.
Hakkuri suka shiga bani tare da fadin don yaga kina rika masa ne a gurin ki ne kadai yake ganin yaran zasu ji dadi kuma su samu tarbiya ni dai shi nake gani kamar hakan ne.
Shiru nayi na kasa ci gaba da cin anincin dake gaba na duk da yunwar da na kwaso a lokacin na mike zuwa dakina wanka na shiga na fito na gyara jikina tare da saka bubu a jikina redmade mai laushi daidai zaman gida.
Falon na fito don kada damuwa ya damay ni ni kadai ban dade da zama ba sai ga text ya shigo min shine ya turo min wai in mashi list din abinda muke bukata a gidan.
Share zancen nayi naci gaba da abinda nake yi nace Anty yau naga kun wahala ina ga zan bar fita yanzu da yaran nan a gida zan dinga barin ku tunda sunyi wayo ko ?
Altine tace wa yan nan diyan nawa dake da yawan tsotso haka zasu yarda su zauna a gida nace idan sun samu madara zasu zauna sai mu gwada a satin nan mu gani.
Tacevto shike nan idai mahaifin su ba zai yi fada akan haka ba nace satin nan ba zamu zauna a cikin makaranta ba don zamu shiga kotu muyi aiki ne a can kin ga ko fita dasu ba zai yuyu gare ni ba ai ke nan.
Laraba ne da gulma yaci ta shigo take fadin ina ganin da mutum biyu kawai aka dawo Altine tace ni tun da suka dawo ban ga ko dayan su ba har ita uwar gayyan tasu.
Ihisan ce ta shigo part din namu da kukan ta sai ga uban ya shigo shima yana zare mata ido yace idan na sake ganin kafan ki gurin su saina balbala ki a gidan nan.
Yana fita sai ga Nafisa a part din nawa ta shigo da zuman masifa sai kuma taja tayi tsaye tana bin part din da kallon mamaki can sai ta basar tace Ihisan fito muje.
Ba zaki zauna gurin wanan matsafiyar ba ya dai bar wanan data sauya ta karasata a nan idan ta iya tayi gunduwa gunduwa da namar ta kafin gobe.
Sai yarinyar ta make hannu taki zuwa tana matsowa da zumar janta ta yanka wani ihu ta nufo gurina tana kuka tsayawa tayi tana kallon mu nace Ihisan jeki gun uwar ki kin ji.
Aiko baki fada ba zata zo ne tunda bake kika haifar min ita ba nace ina yanzu gorin haihuwan nan ya wuce a gurin ki tunda kin tabbatar ni din ba juya bace.
Ina magana kamar banbson yi tare da ahafan kan yarinyar dake kwance a jikina tana kuka au don wa yan nan diyan da kike ganin kin haifa mai masu zubin diyan ke tare wa ya sani ko wani bayahuden kika je yai maki cikin su.
Nayi murmushi nace ba wani baya hude yai min cikin su ba wanan dai da kike hauka a kansa ne yai min.
Wata kila baki iya kwancin bane yasa kika haifo naki a haka don haka ki fice min daga shiya kafin ranki ya baci yanzu a gidan nan don zan maki abinda sai kinyi jinyar jikin ki.
Ya dai ba taki bace tawa ce kuma dole ki bani abina nace diyan ki dai don naji kina magana akan Ihisan kadai kwashi tarkacilen diyan ki ku tafi don Allah banson yawan hayaniyar nan naki a nan kina daman min yara dake barci.
Haushi da takaicin magana na ya kamata a wurin tace don wayan nan diyan da kike ganin kin haifa kibar daga kai a kansu kibari kiga girman su.
Ta Allah ba taki ba in sha Allah idan da rai da lafiya kamar gobe ne kin gani sha kurumin yadda kowa ya girma su ma girman zasuyi da yan uwan su gidan nan.
Ta rasa may zatace ta fice daga part din Altine tace dama na fada maki akwai wata a kasa kyalesu muga iya gudun su gidan nan.
Ko yanzu ki gode ma Allah don ta wullakanta ai ga saki ga yaranta kiri kiri miji ya hanasu zama a gurin ta ko haka ai ci gaba ne a gare ki don ya yaba da ke ke nan.
Wanan yabon kan ai da wahala Anty ace an dauki taulalin yara an dora ma sai sun girma su kama uwar su.
Tace ke dai din ce ba mai son hayaniya ba amma sai naga ko sanan riba ce a gare ki ai tunda duk wani kudin lalurar su yana a hannun su.
Murmushin takaici na sauke nace wanan bai a gaba na sam don ni ga Allah na dogara da lamarina idan rabona ya koka a wurin shi ko bai da niyar bani sai ya bani.
Shiru falon yayi na dan wani lokaci na mike ina fadin bari na

130 / 144

Chapters