Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MIJIN Buzuwa Complete Complete Hausa Novel by Nil

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   134 / 144

399K to 402K   out of 431K words

key din sashen ka ka karbe min na wurina.
Gyaran part din kike ko may iyakan ki kizo ki kwanta ki tashi ki barshi a haka na ko so kike in bar maki key din ki kwashe min duk wani abin kwarai kiyi gaba dashi.
Iyakar ki min sata ko bincike ki samu abinda na aje ki gaba dashi wani kallo tayi mai kamar zatayi magana sai kuma tayi shiru don babu abin fada.
Yanzu sherin da zakai min ke nan yace may ye sheri a cikin wanan maganan ba gaskiya na fada ba ko kina tunanen ni mahaukaci ne da zan bar maki key dina yanzu ?
Ke nan itace mai gaskiya a gare ka don baka san barnan da take maka ba a boye yace ban taba gani ba ko ji ke ko fa na gani kuma na sani.
Dama tunda an riga da an gama dakai yanzu ai baka ganin laifin ta tunda ta asirce ka ta gama.
Wai ke may kika gane da zancen asirin nan ne baki da tawakkali ga Allah sai zancen asiri may asirin naki ya tsinana maki a rayuwa ki wai ?
Ki yarda da Allah shine mai yin yadda yaso ba wani can ba wanan ma abin kunya ne kina fadan haka a bainan jama,a ke baki jin nauyin haka ko kunya ?
Kunya may zanji ga abinda nasan kinayi ina yi duk akan mutum guda kuma muke tin shi nace kike dai yi don ni banda lokacin haka ga Allah na dogara da al,amarina .
Karya kike yar iska muna fuka karuwan cikin gida mai kwatar mazan mutane nace ikon Allah ai kwace miji ke aka sani da wanan.
Ke da kika raba miji da matar shi har da uwar shi da iyayyen shi Allah bai yarda ba yanzu kike ganin baki na kan hakan.
Ke kana jin abinda take fadi banyi mamaki ba don ke kin fada tunda dama haka ake fadi nace ba gaskiya aka fada ba yanzu mai kika zo yi nan din ?
Ke karamar yar iska dake da wa yanda suka turo ki kimin fitsara duk maganin ku zanyi a gidan nan mu zuba dani daku a gani.
Nace muga alheri gida dai na shigo shi ba fita sai dai ki mutu akan kishi ba abinda za a fasa kuma tace.
Wallahi karya kikeyi sai kin bar gidan nan koda tsiya anga wuein ci an lake kamar kaska ko to fita kamar gobe ne wallahi don, , , , .
Ke dan Allah ya isa haka ban son wanan shirmay tunda kin fadi abinda ya kawo ki kuma kinji amsan ki.
Ki fice min daga shiya tun kan ranki ya baci a gisan nan tace bayi kan ka bane don kai min haka a yanzu zaka dawo a hannuna mu zuba dani daku a ga wanda zai fasa.
Ta juya ta fita daga part din ya juyo yana kallo na ina zaune na harde hannaye na saman kirji na nima ido na zuba mai yace ke ma na lura kun zama daya da ita yanzu.
Nace yar rainin hankali ce bata tashi fitinan ta sai ranan da tasan nice da girki na dade da fahintar haka a gare ta dama.
Ke din yanzu rai kike gyara min da kike guduns komay ni ba gudun ka nake ba kaucewa nayi ma abinda nasan zai iya jawo muna matsala ai.
Yace oh tunanen ki ke nan ashe nace haka shine mafita ba tare da samun sabani a tsakanin mu ba tunda ka hau a lokacin.
Na tura mai plate din abincin da na zuba a gaban shi nace amma bai dace kace tana maka sata haka a gaba na ba ya ja plate din dakyau a gaban shi tare da fadin ke daban ne a gare mu ai gara kiji ki san may ke gudana don ki kula.
Lokacin da ta yaye ni ta tafi dashi ai kina gidan nan amma baki sani ba don haka kina gama abinda kike yi ki dinga rufe min kofa na don Allah.
Haba sai kace ba matan ka ba dai ai yanzu ba zata kara ba tunda tasan ka gane hakan har ka dauki mataki yace baki san halin Nafisa bane.
Zama nayi ina kallon shi tana cin abincin shi hankali kwance na tsiyaya mai ruwan zobin a kofi na mika mai ya ansa ya kurba tare da lumshe idon shi yace ke kika hada wanan din nace eh baiyi bane yace yayi mana sosai.
Akwai abinda zaki hada da hannun ki baiyi dadi bane ya karasa kurbe sauran dake cikin cup din ya aje min lokacin ne nace mai gidan SJJ sun aiko min da katin gaiyatan bukin gidan su wani sati.
Kamar baiji abinda nake fadi ba ganin ya gama ya turo min plate din a gabana na mike tare da fara tattara kayan abincin.
Kallona yake yana jin wani irin son kasancewa dani a lokacin wani abu yake ji yana fisgan shi na dago kai nace ka gama da wanan jug din ne in dauke.
Bar min zan kara anjima yace amma dai kin san babu inda zaki yanzo ko nace kamar ya ba abinci kace inzo in baka ba dama, na kuma baka.
Ke nan har yanzu baki hakkura ba daga gudurin ki na dauka wanan zancen ya wuce ai.
Dago kaina nayi na kalle shi da zuman in bashi amsa sai dai yadda ta tsure ni da idanuwan shi yasa nayi saurin dukar da idona kasa.
Ina sauraren ki idan hakkurin da mukaje har gafin ku muka baki bai maki ba yanzu sai ki fada min abinda kike son inyi kuma , ?
Deedar nasan wani lokaci ban kyauta maki amma kuma ni ina ganin duk abinda kikaga nayi da dalilin yin shi gare ki sai dai ke kin kasa fahinta na ne ko kadan kina ganin haka kamar tauye hakkin ki ne a gare ni.
Har cikin zuciya na na dauka ke kadai ce macen da zan iya sakata tayi abu tayi shi ba tare da korafi ba, ina alfahiri dake a ko ina Deedar bana son rashin fahinta haka yana shiga tsakanin mu akoda yaushe.
Ki tausaya min don ceto rayuwana daga halaka ke kadai ce kike iya tsayawa ki fada min gaskiya in fahinta ya zama min alheri kuma idan nabi shawaran ki.
Kada ki ruguje muna tubakin da muka fara dorawa dake a gidan nan wanda nake fanin zamu girbi alheri nan da dan lokaci kadan idan Allah ya yarda.
Ki daina fadin kalman banson ki khadija ina son ki ina matukar kaunar ki babu macen da keda kaso irin naki a zuciyana.
Na yarda dake dari bisa dari khadija ke din jaruma ce da bakowa ke gane hakan ba sai wanda ke tare dake yasan hakan ki yarda dani khadija don jiki nake kamar ba a matsyin matana kawai na dauke ki ba a matsayin yar uwa ta jini da zata share min hawaye.
Ban kara gaskanta hakan ba sai rike min wa tan nan yaran da kike ganin kamar na cuta maki ne ga yin hakan ni kadai nasan manufata nayin hakan danayi gare ki don ingancin tarbiyan da yaran nan zasu samu daga gare ki nake kwadayi wanda Alhamdullahi yanzu na fara ganin hasken hakan a gare su sosai.
Ajiyan zuciya na sauke daga inda nake zaune don jin yadda yake tsaro min magana daga bakin shi wanda ko wacece dole ta hakkura da wanan kalaman nashi.
Sai naji bazan iya fada mai komai ba a lokacin tunda har ya zauna yana fada min zuciyar shi haka yau ga kuma kalamin dana dade ina son ji a gare shi ya furta min da fatar bakin shi.
Sai naji bai kakata in rike shi haka yadda nayi niya ba a zuciya na don duk sai naji ya wanke laifin shi a gare ni ya zama dole gare ni in kara hajircewa gurin taimakashi a gidan.
Ba zan so in dawo da abinda ya wuce ba gare mu yanzu sai dai mu dora a inda muka tashi a faki gaba kuma don nasha alwashin ba zan sake kyale Nafisa tana juya mu yadda taga dama ba a gidan.
Ganin nayi nisa a tunane yasa ya dan rankwafo inda nake zaune tare da hura min iska yana fadin ko baki yarda da duk abinda na fada maki bane yanzu.
A sanyaye nace na fahinci manufar ka yaya AA insha Allahu ni kuma nayi maka alkawarin duk naga gyara a lamarin mu zan sanar dakai koda a cikin hikima ne da yardan Allah yadda zaka gane.
Rungumini yayi zuwa jikin shi yana mai sauke nunfashi tare da matse ni sosai a jikin shi kamar wani zai kwace ni a jikin nasa.
Wani iri duniya muka lula naji tankar ace daga ni sai shine a wana rayuwan babu sauran wata a bayan mu in gwada mashi so na sahihi duk da ko a yanzu ma hakan bai baci ba ai don kowa gyara kansa yake a gurin miji tunda har na fara samun wanan yabo a bakin shi.
Sake ni yayi yana fadin kai kayan nan ki kara ba yara nono ki dawo daga kai nayi na kalle shi ido cikin ido wani irin abu naji a zuciyana nayi saurin dukar da kaina kasa.
Don nauyin shi da kunya daya kama ni a lokaci guda da kyar na iya bude bakina nace daka bari har yan uwan nan nawa su wuce zaifi.
Ummm, ummmu yace kada ki kawo wanan maganan yanzu ai sun san gidan ki suka zo kuma aure kike yi jin dadin hakan ne ma yasa kika gansu nan.
Nace to shike nan amma nima kayi hakkuri da abinda nai maka a baya ba daidai ba matsalan rashin fahintar junane na fada a cikin sanyin murya tare da dan marairaicewa.
Rungumo ni naji yayi cike da tausayin junan mu yana fadin ki yarda dani Deedar ban rike ki da wani manufa ba a raina idan kin ga haka ki fahinci inda na dosa kafin ki yanke hukunci ina sane da komai da ke faruwa a gidan nan.
Sai dai ban taba daukan zaki dauki hakan a cutarwa ba gare ki don haka don Allah ki gafarce don baki taba min musu irin haka ba har da guduna zuwa wata uwar duniyan.
I am so sorry ga abinda ya faru ba wai na fada don in hana ki karatu ki bane ya isa haka yaya AA na fahinci komai wallahi kaima don Allah ka yafe min .
Kai ya girgiza min yana murmushi yace khadija ke nan babu abinda kikai min na batanci da zaki ce in yafe maki komai kikai min kina da dalilin yin shi tunda ban fada maki manufana ba.
Idan ma kin man na yafe maki har ga Allah don ban taba rikeki da magana ba kara lafewa nayi a jikin shi ina sauke numfashi.
Can na sake shi nace zan duba yaran yaya kada suga na dade ban dawo ba yace ke dai kina gudun sherin mai shegen saka idon nan Altine.
Da kyat na samu na bar wurin shi zuwa kasa ya bini da kallo yana sauke murmushi a fuskan shi tare da kada kai yana fadin kai mata sai a hankali kamar ba ita bace ta so ta birkice min yanzu.
Koda na koma na samu ma yaran suna goye a bayan su don haka na shiga nayi wanka na kimtsa jikina dakyau naso in kara ba yaran nono amma sai Altine tace in wuce ai akwai madaran su yana nan idan sun tashi.
Koda na shiga motsin shi naji a bayi yasa nagane yana ciki wurin daya dan baci na kara gyarawa sai lokacin naga zoben shi dana tsunta a kasan gado danake shara yana fitowa da bathrobe a jikin shi sai dan karamin towal da yake tsane ruwan kan shi dashi yace har kin dawo ashe.
Nayi sauri nace mai sai yai saurin fadin bance ba don Allah a rufa min asiri kada asani kwana maraya kuma nace da momy da ranta da Abba zaka kwana maraya kuma .
Yace ai sin yayeni tuni yanzu sabbin uwaye na samu kuma wanan zoben naka ne na kawar da zancen da tambayan shi.
Kallo zoben yayi yana mamaki yace ina kikaga wanan zoben dana dade ina neman shi a dakin nan karkashin gado na gan shi dazun ina shara na bashi amsa.
Takowa yayi zuwa inda nake ya karba yana juya zoben yace nasan ba kowa yai min wanan aikin ba sai Nafisa zobe ne na tsari da aka bani ta sani takuma san amfanun shi sosai gare ni ya karba yana sa zoben a yatsan hannun shi naga yana wani addua lokacin da yake zura zoben.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/20/21, 6:35 AM - Xxxxx: Satin bakina daya suka koma gida da rarin abin arziki daga gare mu sai albarka suke saka muna mun rabu tare da kewan juna inda suke kara jadda min kula da zumunci.
Bukin gidan SJJ ya tashi ban dauka yana tune da zancen ba sai ana gobe yake ce min daya shigo part dina da dare, kin fasa zuwa yiwa Adam din ne kara ?
Ni na dauka baka barni bane ai yace ai ba zan hanaki zuwa rama abinda akai maki ba kema sai dai kin san dole zaki kai abin buki ko ?
Nace ai shine kuma don dai kasan wanan ba taran kudi suke nema gudun mawa ba yanzu yace idan kinyi tunane sai ki fada min.
Abinda zaki kai godiya nayi mai ya fita tun wanan lokacin nake shawaran abinda zan kai wa amarya gudun mawa idan zan tafi.
Altine da nake fadaw tace shine matsalan mu yanzu sai mutum yace sai ya rama alherin da akai mai nace ba wanan a tsari na abu dai wanda ba zasu zata ba nake tunane komai kankantan shi.
Karshe dai mun yi shawara na hada kaya masu kyau irin na Anty Salbiya sai wani sarkan gold mai kyau da tsada da awarwaro a cikin kit din su da zan ba amarya gudun mawa.
Maryam ta shigo washe gari muka shirya har laraba da Altine zuwa gidan bukin mun samu taron sosai wurin hajiyan gidan.
Ban dade ba muka mika abinda muka zo dashi tare da fadin zamu tafi tace haba tun yanzu jana tayi har dakin ta dani da maryam tare da su Altine.
Muka zauna tace naga kamar wanan sakon naki mai muhinmanci ne a gare mu tana magana tana bude ledan ta ga abinda ke ciki.
Ikon Allah duk wanan abin haka kin ga mutane basu fahinci hakan ba don ba wanda ya maida hankali gurin gyara min kawan tawa.
Don Allah kiyi hakkuri ki dan muna bayanin komai kafin ki tafi na fara mata bayani a cikin kunya tana fahinta na sai godiya take min kan hakan.
Ta bude ledan da akai wraping din sarka da awarwaro a cikin sa sai naga ta bude ido tana fadin wanan ma ya isa khadija ki koma da sarkan nan ko ni ban saya mata shi ba don mijin ta ya saka mata su a laife sosai.
Anty ai wanan nawa ne don ta na kawo shi tayi dan shiru kamar za tai magana sai kuma taja baki tayi shiru ta mike ta fita dan jima kadan sai gata ta dawo dakin tare da amaryam da wasu dauke da kayan motsa baki a cikin tire.
Bayan sun fitane tace da amaryam na kira kine kiwa anty khadija godiya kinga abinda ta kawo maki tana nuna mata kayan.
Murmushi tayi tana zama sai da ta shafa sarkan ta dago tace kai anty nagode sosai wallahi wanan yana da kyau matuka.
Ta shiga godiya kayan ne hajiyan ta fara mata bayani tana sune kai don kunya ta kara fadin anty nagode.
Bamu taba komai ba daga cikin abinda suka kawo muna a dakin nace zamu tafi tace haba wai kodai har yanzu baki sake damu bane a yan uwa muka dauke ki fa gidan nan.
Nace ba haka bane anty a koshe dai muke shiysa tace to tunda ankawo saidai ku tafi dashi ranan jumma,a akwai walima da yinin buki don Allah kuzo khadija don ranan zan hada ki da Alhaji ku gaisa.
Don bai sanki ba sai dai yana jin labarin ki a gurina nace Allah ya kaimu mukai mata sallama muka tafi tana muna godiya.
Maryam ce ke jan mu a motar sai da muka dauki hanya tace humm,umm masu kudi suna inda suke wallahi duk wanan gidan ita kadai ke mulkansa.
Altine tace nima abinda nake ta tunane a raina ke nan tun dazu don Allah ji daki kamar wani shagon sai da kaya.
Ni ba abinda ya ban mamaki sai yadda suke ta yaba kyautan ki gare su nace nima maryam shine ke bani mamaki ai.
Muna shiga gidan buzuwa ta fito zasu fita ita da wata maryam tace wanan ashe ta fara fita bakar yawon nata ko nace dama ina zai iya tsare ta a gida ko yaushe tunda ta riga ta saba da fita kullun.
Ranan Jumma,a bamu je gidan SJJ da wuri ba sai bayan azahar muka isa gidan yau ma kamar ranan haka aka tare mu tana

134 / 144

Chapters