ba yanzun wanan abin da kikayi yaya kike son diyan ki da mijin ki su dauke.
Kin wuce kin watsar da diyan ki gashi kin rufe kitchen kin barmu da yunwa in badon wanan baiwar Allah dake gidan nan mun samu ta bamu kulawa da yaya kike son muyi.
Tsawa ta daka ma Fatiya tace wanan ya isheki haka na gane idan na barki a gidan nan watarana zan dawo in samu kun dinke da wanan matar a gidan nan.
Kai ta gyada mata tace ba zan taba cin amanan kowa ba sai dai daga ke har ita zan fada ma duk wanda yayi ba daidai ba gaskiya.
Kiwa kanki fada ga wanan halin da kike yi don zai kaiki a inda baki tsamani ba don daukan alhakin yayi yawa.
Abu wasa wasa har dare suna wajen ganin bai dawo bane yasa suka yanke shawaran zuwa asibiti su duba idan yana can ita da yar uwarta dayan Fatiha tana ciki tana sallah a lokacin.
A asibitin ma sin sha bambam a can basu samu ganin shi ba sun dai duba yarinyar suka juyo zuwa gida sai dai sun samu ya koma gida.
Yana zuwa gida ya shiga gida tare da bada umurnin su rufe maigidan shi bai kara fita ba sai safe don ranan yana da bukatan hutu a tare dashi.
Nashiga gurin shi na samu har ya kwanta a lokacin na karasa yana kwance ya kifa ciki shi kadai a dakin na shigo zuwa bakin gadon na zauna.
Juyowa yayi da fuskan shi yana kallo na nace sannu da dawowa ashe anka maman Ihisan din yace ta dawo dai tunda ta gaba abinda taje yi.
Kallon shi nayi cikin dan mamaki nace wani abin taje yi ashe ina tambaya ina kallon fuskan shi yace idan ba wani abu ina zata tafi tabar yarta mai shan nono.
Ajiyan zuciya na sauke don banda abinda zance cikin fadan mijin da mata nace abinci fa naga har ka kwanta ko yace bar abincin nan bana jin yunwa.
Nace kada ka dinga sa zancen mata a rai ka jawa kanka matsala kuma ki hado min tea kawai zansha na daga har na kai kofa nace ka bada umurini ta shigo ko.
Kallo na yayi ya kawar da kai saina dan tsargu da kallon da yai min din na fice daga dakin zuwa dafa ruwan zafin.
Ban dauki lokaci ba na kawo mai sai da ya sha na kawar da kayan na sauko ba tare da na kara mai maganan komai ba shima dai din bai mun ba.
Ina sauka na shige muka rufe Altine ce take tambayana ko Nafisa din ta shigo gidan daya dawo nace ban sani ba amma ina tsamanin ta shigo ai.
Mikewa nayi zuwa ciki na dan kewa ya ban daki na fito na gyara jikina ban fita falo ba na shirin kwanciya sai ga laraba ta shigo da mami na karbeta na shayar da ita.
Bayan mun kwanta ne har barci ya fara dauka na sai ga Altine a dakin tana fada min ashe Nafisa ba shigo gidan ba.
Karshe ma maigida yace a rufe mai gidan shi tunda ya dawo ta na waje tana hauka da yar uwarta nace badai Fatiha ba tace dayan ai Fatiha ce tazo tana fadi wai ai maki magana ko zakiwa maigida magana don ance yana gidan nace mata kin kwanta tun dazun kin yi barci.
Yau ma Altine yana nufin matar nan awaje zai barta ta kwana ke nan ko may tace wa yaja Khadija itafa tajawa kanta komai Allah ke tambayan ta.
Tun da safe ina karyawa sai gashi a dakin yace zai fita asibiti ya duba su nace adawo lafiya yakai kofa ya juyo yana fadin jiya ya akayi kika shiga motar nan , ?
Baki shiga wanda na baki ba sai wanda aka baki kyauta kikai amfani dashi kin nuna min kin fi bukatan wanan din ke nan ko ?
Kaina na dan girgiza nace wanda na gani a kasa ai dashi zanyi amfani ko don har yau banga wanda ka bani din ba a gidan nan.
May maganan ki ke nufi ke nan ban baki shi a kasa din ba ke nan ko nace bance ba tambayana kayi ai na baka amsa ko ?
Yaushe ma kika iya tuki haka ne ban sani ba nace ni tun ina kaduna nake driving motar ya Adam ai ko don bamu da mota gidan mu kake mamaki haka ?
Wanan kuma maganar kine don zance na bai kai can ba kuma yanzun na fahince ki ai daga zancen ki yana fadin haka ya fita nabi bayan shi da kallo.
Nace a fili tunda ina yar tallaka kana mamakin tukina ko ai samu yafi iyawa yanzu baga iyawan yai min dadi ba.
Matar ka daka wayar kamai da ita mutum a cikin mutane bakai mamakin iyawan ta ba sai nawa ai itace maganin ka a gidan nan.
Tayi yadda take so kuma a zauna lafiya yanzu ai zanga matakin da zaka dauka akan ta gidan nan don wallahi ba yarda zanyi ba.
Yana fita daga gidan asibiti ya nufa sai da ya duba yarinyar ya fito ya leka office bai dade da zuwa office din ba security din gidan ya kira shi.
Kan Nafisa tazo gidan da tashin hankali sai ta shiga gidan fita yayi zuwa gidan inda ya samay a cikin tashin hankali sosai da masu tsaron get din.
Yana bude kofa yace ke wata irin mace ce mara hankali zaki zo ki tara min jama,a a kofar gida na haka ne.
Tace don may zaka hanani shiga gida na don wani dalili naka can yace gidan ki fa kika ce tace idan nan ba gida bane ina kake son in tafi ?
Ida kika fito yace ke ni dai na auro ki ko to kije na sake ki saki daya yau ban son komai naki a gidan nan ki tatara ki kwashe awa daya na baki ki barmin gidana.
Ya juya gurin security din yace kada ku bari ta tafi min da diyana ko ina Nafisa da tayi mutuwar tsaye tun lokacin da ya furta ya sake ta sai da taji yace diya ta iya magana.
Tace diya kan nagama tafiya da abina bandaki wanan musakan zan iya barma ba yace mu zuba ni dake ki gani a garin nan.
Ya shiga motar shi ya tafi ya barta a gurin a cikin tashin hankali ina daki zaune naji hayani ashe itace ta kuma dora laifin a kaina.
Falo na fito na ce ma su Altine don Allah su kyale ta kada su tanka ta abokin mutuwa take nema sai lokacin Altine ke fada min wai ai ya sake tane a gaban kowa.
Da sauri nace subbahanallahi shiko yaya don may zai yi haka da hankalin shi kuma Altine tace ke kan ban san irin zuciyar ki ba wallahi.
Altine ba hakana bane nace wanan abin bashi ya dace da ita ba ai ba a yanke hukunci haka a cikin fushi sakin aure fa ba dadi ne gare shi ba.
Tace ke ai farin ciki yakamata ace kinyi nace saboda an sake ta din tace kwarai kuwa an huta da bakar daga a cikin mu.
Nace Altine ke fa mace ce bai dace ki farin ciki don aure ya mutu ba ko ta bar gidan nan bashi zai sa ta gyara halin ta ba sai ma ta nusa ga halinta mara kyau.
Kin ga kuma ga haihuwa a tsakanin su dole dai ko yaya ta koma a kira ta da uwar yayan shi a garin nan amma in yayi hakkuri ya ladabtata a cikin gidan shi kila idan tana da rabo sai ta gyara halin ta.
Amma saki baida wani alfanu ga namiji zuwa ga mace yanzu ma ko nayi murna ta tafi ai wata zai kara kwasowa gidan nan ko don haka banga abin farin ciki a wanan ba gaskiya.
Laraba tace gakiya ne uwar dakina na gamsu da maganar ki don baka san kalar da za a kwaso maka ba kuma don mazan nan da zaran sun dadana zama da mace fiye da daya a gida ba fasa aure zasuyi ba.
Gara wace ko ka santa kasan halin ta yafi ace a auro maka watacan daban sai dai ita din ce ba abin a tausaya mata ba ko kadan saboda halin tan nan duk da abinda ya faru da ita din.
Altine da magana na bai gamshe ta kitchen ta shige ta barmu a gurin muna magana da laraba ina gurin zaune ina jimamay sai ga Fatiha ta shigo part din.
Bayan mun gaisa take fadin nazo ne ki taimaka min da daysn layin mijin ku don wancen dana sani baya zuwa na ba wanda zata iya samun shi taimin godiya zata fita.
Saita juyo take ce min kin dai ji abin daya ke faru damu ko a gidan nan koda yake banga laifin mijin ku ba gaskiya.
Don yayi iya hakkurin da ake son namiji dashi don haka tsuntsun da yaja ruwa shi ruwa ka doka nace naji zaman jimamay nake a nan din kika samay ni yanzu.
Nayi iya kokari na tun jiya yai min iyaka da zancen su yasa kikaga na sa masu ido tana murshi tace ai ba komai don kinyi yadda duk akeyi don nasan da itace ba zataiwa naki yadda kikai muna ba.
Allah dai ya kyauta har abada ba zan taba goyon bayan karya ba nawa bai kona ni ba nawani kuma ba zai kona ni ba har ga Allah.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/4/21, 9:38 PM - Xxxxx: Ban san ya sukayi da shida Fatiha ba na dai gan su a gidan bayan wasu awowi gaba dayan su sai shige da fice sukeyi a gidan.
Ranan dai gidan ya koma na buzaye kowa ka gani fuska babu walwala a cikin su alamun bacin rai a tare dasu ba sai an tsaya fadi ba.
Shikuma tun da abin ya faru ya tafi bai dawo gidan ba har wanan lokacin magana nayi wa su Altine akan su fita batun su su daina zirga zirgan da suke a wajen gidan ma.
Don kada su dauka ko muna farin ciki da hakan ne gare su Altine tace kai ni kina ban mamaki akan wanan buzuwa ta dauka haka din ne mana.
Idan kece haka ya cika da ke tausaya maki zatayi akan hakan ba nan falon zata fito tana darawa ba murmushi nayi tare da fadin aimu ba ita bace sai mu nuna mata mu din masu tarbiya ne ko.
Baki ta tabe tamike zuwa ciki tana fadin ko dai duk tsoron nata ne haka daga ke har mijin ku shima tunda wanan abin ya faru ya bar gidan nan bai leko ba.
Nace ai kin fi kowa sanin ba matsoraci bane yanzu tunda ya nuna maki namiji yake dake da kawar ki buzuwa ta shige tana dariya ciki.
Mun yi saurin rufe part dina ranan don haka bamu san halin da suke ciki ba sai da safe ne naji ana buga kofan part dina da karfi ina zaune ina karyawa Altine ce taje ta bude kofan.
Shine a tsaye zata jashi da wasan ba,a tace ina khadija tana ciki ta bashi amsa ya wuce ta ya turo kofan ina kafa kai a cup din da nake shan kunun da Laraba ta dama min.
Ina kwana na fara mai yace Deedar waya balla min dayan dakin nan ya shiga nace tunda na haihu ban taba zuwa gyaran wanan dakin ba asalima ai bakaji na karbi key din ba da sunan zan gyara shi.
Wani iri yanayin fuskan shi yayi a lokaci guda ya furta Nafisa nafiki iskanci wallahi ya juya ya fita da sauri dakin.
Mikewa nayi na fito falo motsin da naji a kitchen na leka inga wace ke ciki Altine ce a kitchen din itama ganina ta juyo tana fadin mijin ki lafiya yake kuwa naga ya shigo a fusace yau ya kuma fita a hakan.
Nace shine nima abinda ya fito dani yanzu don ina ganin anmai barna a dakin shi da yake aje kayan sirin shi ne tace dan gado baya barin gado.
Wa zai mai inba wanan matar tashi ba suna fita a gida haka banza ne dama ai sai sun samu barnan da sukayiwa miji suke tafiya.
Tun jiya naso ince mu saka ido akan komai sai kuma maganan da kikaimuna ya sare min kafa da zancen nace yanzu ai ya fita.
Sanan may zaki iyayi akai Altine wanan tsakanin su ne don yafi kowan mu sanin halin matar shi ai .
Tunda ya fita da safen nan sai daya ya dawo yana shigowa muna falo zaune sai wayan shi yai kara ya daga kafin ya amsa muna gaisuwa.
Naji yana fadin OK ok yayi kyau an karbo yarinyar da kayan ko ya tsaya saurara sai yace No yarinyar dai da kayan zaku karbo min ku barsu su tafi su.
Ina ita Sadiya bakina ya subuce ya tambaya sai da ya gama sauraron mai wayan yace min tana asibiti dasu momy yau za a sallamota dai.
Wanan bata da imani tafiya tayi tabar maka yar jaririyan anan ?
Zama yayi a daya daga kujerun falon yana cewa kudina dake gidan nan dawasu abin amfani na ta kwashe zata tafi dasu.
Haka suke ai dama inji Altine sai sunyiwa gida tas suke tafiya su tsiyata mutum gaba daya Allah ne ya taimake ka ai.
Hannun shi yakai a goshi yana fadin bari Altine yadda matan nan tasan ina aje abu haka a gurin nan yake ban mamaki kuma ba ita kadai ta budeshi ba dole da taimakon maza ta iya bude gurin nan.
Wanka yayi ya fita ya dauko su momy daga asibiti sai yarinyar ta baka tausayi sai gashi ya shigo dauke da kwalayen madara wanda za a dinga bawa yarinyar tasha.
Zuwa dare su Ihisan suka shigo gidan tare da Samira munyi mamakin ganin samira tare dasu shima yana fitowa yace yarinya daya ya ba da umurnin a dauko sukai mai bayanin taki bin uwar ne anyi rigima sosai tace bazata bi uwae ba suka tafi suka barta nan shine dalilin dauko ta.
Ni dai tunda yaran suka shigo banyi magana ba sai ma Ihisan datazo gurina ta kwanta ita kuma samira ta kwanta saman dogon kujera.
Tunane nake na abubuwa da dama a raina har dare yayi ina son kwantawa ga yaran banji yace wani abu a kan su ba.
Momy ne ta ce sani ki shige abinki ki kwanta bar mu dasu a nan har safe muji abinda ya yanke a kan su din.
Cikin dare ma banyi barci ba sai tunane nake barkatai sai wani lokaci na samu barci ya dauke ni a gurin.
Kukan yaran ne ya falkar dani daga barci na tashi na samu momy na rarashin su na zauna ba karbi yarinyar momy dake zaune a gefe na tace ni wanan matar alamarin ta ya daure min kai yafi karfin mamaki.
Anya barin yarinyar nan datayi ba da biyu tayishi ba don shu,umancin ta yawa ke gare shi nace momy ni abin ne ma na kasa fasarashi wallahi.
Nan ta fara bani labarin a cikin dare yanyala ta gudu ta falka ta nemay ta bata ganta ba a asibitin sai da safe ne da yaje yake fada mata abinda ke faruwa.
Nace raina ya bani zata dawo gidan ai tace nima dai haka nake tunane a raina tun dazun don dawowan yarinyar nan da biyu ne gaskiya.
Mun dauki lokaci a dakin muna maganan da momy kafin in koma barci ita kuma ta mike zuwa sallah.
Da safe ya shigo gaida su momy ne yake fada mata zai bayar da Samira a ranan abi uwarta da ita koda ma bata je gida bane a je mata ita can garin su don bai dauka gida ta tafi ba.
Don a maiduguri aka kama su aka karbo mai kayan shi da yarshi ya ce wanan matar ta fita raina kwata kwata momy don bata da dadi tako ina.
A raina nace yanzu ko lokacin da ake fada ma ai baka ganin laifin ta sai na masu fada ma gaskiya ni ko a jikina kan wanan zancen.
Muryan shi naji yana tambaya na jikin Sadiya din nace tana barci har wanan lokacin a daki sai bai kara magana ba.
Kamar yadda yace haka ya fita da Samira a gidan ashe tafiyan ke nan bai dawo ba sai dare momy ke tambayan shi yar yace yaba da kudin jirgi an kaita Niger ai.
Allah ya kyauta momy tace mai ya fice zuwa part din shi sai dana dan jima a zaune na mike tare da daukan kayan abincin shi na samay shi a dakin.
Na shigo yana amsa call dan haka na samu wuri na zauna a gefen shi ya dan dauki lokaci yana amsa wayan.
Ya gama ya juyo yana ce min na san kina da hankali Deedar zaki fahinci halin da nake ciki a yanzu ki taimaka ma momy ku rike min yaran nan a dan zaman da momy zatayi kafin ta wuce wani sati.
Zuwa lokacin na gama yanke shara akan yaran na samu wace zata rainan min su a gidan nan don banson inyi nisa da yara nan ko kadan.
Nace yara