shi ta wuce don wani dalili nata na banza.
Allah yaso Deedar yana son ta har cikin ranshi haka ma hajiyan mu tana son ta da na nuna mata nafita tsiya wallahi.
Guntun tsuki yaja a fili har Yusuf ya dan juyo yana fadin yaya akayi ne mutumina ?
Wallahi Yusuf yarinyar nan nake tunane a raina ban san ya akayi ta samu waje haka a zuciya na ba har batinta gidan ya sa nake jin gidan kamar ba kowa a cikin sa.
Yusuf yace ba sake kayi ba halin khadija ne ya ja mata haka yanzu in ka bibiya ko su Altine kamar su kama da wuta suke don rashin ta a gidan.
Ai mutum mai mutunci haka yake idan yabar guri sai kowa yaji daban a gidan yace na yarda da dan ko sadiya da take yarinya tasan khadija bata gidan.
Yau din nan Altine ke fada min ta daina karban abinci ko wani abu idan an bata sai fitina take masu kaga ko yaro yasan mai kyauta mai ashe inji Yusuf.
Ban san kunyi haka ba wallahi da na fada ma hakan da zakai mata ba daidai bane ko don kyau cika alkawarin da ka daukawa iyayyen ta kafin ai aure.
Bai iya magana ba sai dafe kanshi da yayi da hannun shi daya yana ci gaba da tunane a ranshi don baiji irin haka da Nafisa ta tafi ba in ba jin da yayi a lokaci daya yana son ya dawo da ita gidan ba..
Na yarda gyara na wurin yan hausa don ni kaina ina jin canji a jikina don irin shaye shayen da akai ta dura min nasu da suke amfani dashi na gida wanda suka sani sukan san ingamcin sa.
Bawai abinda basu san komai aka hada dashi ba wanda suke amfani tun iyayye da kakanni wanda duk wata mace a can ba abin kunya bane a gare ta amfani dashi.
Wancan ta kawo wanan ta kawo duk kuma kakana tana tsare ni sai nayi amfani dasu ba wani zancen boka da malam ko yawan cushe cushe a gaba da zaija wa mutum illa.
Wanan sai ma ya gyara ma jiki fata yai haske ka kara dan magurjin jiki daidaiwa daita da mata biyu zamuyi tafiyan sune zasuyi min rakiya sai wani yayan mu na miji da zamu tafi dashi.
Tun da safe muka dauki hanya har da kuka na na barin su da zanyi don ina jin wani iri a raina ba dadi a lokacin.
Mun sha tafiya sosai sai karfe biyar muka shigo garin har zuwan mu gidan kafin shida na yamma mun shiga gidan.
Da murna su Altine suka tare ni tare da baki na suka bani abinci kamar sun san da zuwan mu a ranan.
Sai tambayan mutanen gida sukeyi ina fadin suna lafiya a yadda na fahinta a cikin hiran mu dasu basu gane yaji nayi ba don shi abinda ya fada masu daban.
Naji dadin boye min sirina da yayi sai naji mutuncin shi ya darsu a zuciyana koba komai ya rufa min wanan asirin dama ina tunanen da wani ido zan kalle su.
Kafin wani lokaci Laraba ta gyara min dakina tsab da dakin da baki na zasu sauka Altine ta gyara yaran sun goya su bai shigo gidan ba sai bayan sallah ishai ya shigo.
Suna falo ana fira yayi muna sannu da zuwa tare da tambayan su mutanen gida sukace suna gaida shi.
Daki ya shiga wurina ina waya da maryam sai kyalkyatan dariya nake ni kadai a dakin kamshin turaren shi ne ya ziyarci hanci na na dago kai ina kallon shi.
Tare da fadin maryam sai anjima na kashe wayan ido ya kura min na dan wani lokaci cikin dakiya nace wanan kallon fa yace ai nasan baki da kunya.
Duk iya gudun naki bagashi yanzu kin dawo ba nace an dai dawo dani indon ta nice ai natafi ke nan ban dawowa wanan gidan da ba a san darajan mace ba.
Maimakon inga ranshi ya baci sai naga yayi murmushi yace goya ki kike son in dinga yi ke nan a bayana ina yawo dake ina fadin ga matar so na komay ?
Ka taba ganin wanda ke goya matar shi a baya ya nuna ma duniya don yana son ta sai dai ya nuna ma duniya kulawa da matan shi a fili.
Kai ya kada min kawai yana fadin wanan bakin mai farsan sa bata farshe da kyau ba gurin wanka.
Bayan fitan shine haniyan su ta kirani na dauka da kunya tare da gaida ita take ce min khadija ashe kun dawo yanzu yake fada min dawowan ku.
Nace eh mama mun dawo dazun tace daga yau na hane ki da barin gidan mijin ki idan ma wani abune ki kirani ko kizo nan wurin mu.
Nayi mamaki da kikai hakan khadija kin nuna min baki dauke ni uwa gare ki ba har yanzu da zaki sa kafa ki fita zuwa wurin yan uwan ki wani kasa.
Nace mama ba hakana bane ta tare ni da fadin kada dai ki sake yin wanan gangancin barin gida da yara haka koma may ye ki fada min ko ki zo wurina.
Nace na gode mama don Allah kiyi hakkuri tace ya wuce ki faki gaba mukai sallama na kashe wayan tare da fadi a fili nace ina zan iya haka mama ai abin kunya ne a gare ni in kai korafin dakin wurin ki ko yaushe.
Washe gari maryam tazo tunda safe ganin yan uwana ta dade dasu tana fira kafin mu koma dakina da ita.
Muna shiga tace min yar iskan mata kin sa mijin ku karamin haukacewa duk da boyen hakan da yake yi wa mutane amma kana ganin shi ko jin maganan shi zaka san baya cikin hankalin shi.
Gado na fada nace ai ke kan gulman ki yayi yawa wallahi duk kin rushe min plan dina naso sai ya wahala sosai kafin ya gane inda nake din.
Tace da ya kwanta asibiti ke kinga yadda ya tayar da hankalin shi ai Yusuf yace min kece maganin shi don ba a taba yi mai haka ba.
Nace maryam kin san da na yarda shike nan haka zai min sheri ya hanani karatuna na zauna nayi nazari sai na fahinci don ya hana Nafisa fita ne ya kirkiro da wanan dokan a kaina.
Tace shima dai wallahi ina zai hada ki da wanan jahilan zaman gida ba ilimi sai tarin jahilci ai karatun mace bawai don aiki kawai ake son tayi ba.
Yana taimakawa rayuwan yayan ta dana mijin ta da ma alumma baki daya karatu ga mace kamar ba gari tallafine.
Nace barshi kawai shi bai gane hakan gani yake kudi suna iya sayen komai da kowa ni bai san zuciya na bai mutu ga abun wani ba.
Wallahi maryam harga Allah ban so dawowana gidan nan ba don komai ya fita raina wallahi tace ke ki bari ko dai yar buzaye ta gama dake ne.
Kai na kada nace ba zan dauki alhakin ta ba koda tayi ban sheda ba kuma ni kin gani nan yanzu duk wani zancen wani asiri ya fita min a kai don Allah keyi ba mutum ba.
Kawai dai ni rayuwan tsarin gidan ne bai mun ba maryam ace mace bata da sani rana ga miji ko wani jin dadi sai idan miji yana da bukatan ta.
Maryam bai fa san damuwan mutum ba shi ko ka fada shi yana ganin kudi sune maganin ko wani matsala na mutum a gidan nan .
Maryam kin sanni kin san halina ni mace ce mai son a kulani amma shi sam rayuwan shi bai san ya lalashi mace ba ko a wuri bukata duk wani abinda ke fada da shawara da ake bani nayi maryam duk a banza.
Sai yanzu nake gane cewa haka yasaba dashi ga matan shi na farko bai da wani damuwa dasu sai ta kudi baida lokacin su ko na diyan su sai dai ya baka kudi kayi ko may nene .
Nasan akwai matan da haka rayuwan su take su dai bukatan su ga namiji shine kudi babu wani jin dadin rayuwa.
Kudi kan nasan akwai su don yanzun haka ina da kudi a dakin nan ni kaina ban san ko nawa bane haka kuma ga account dina don baida keta wurin kudi gaskiya to amma a baka kulawa mana.
Na nuna mashi ni kudi basu bane matsalata ba ranan da namiji zai ware ya baka kulawan shi sai kullun cikin uzuri dare ne kawai zaka kebe da mutun ko shi a uzurce ne.
Tace ikon Allah wai ni khadija ban san halin ki ba wasu nacan suna neman hakan ke kuma ga kudin hakan bai maki ba koda yake banga laifin ki ba tunda ba auren kudi kikai mai ma ba.
Yanzun ai dole ya canza nace Allah yasa sun riga da sun koya mashi haka lokacun da mukaje kaduna sallah da yake dan zama a gida tare damu.
Da kunne na naji Fati tana gulmana wai ni kamar wata fitsarara banjin kunyan zama da miji ko yaushe ina makale dashi.
Maryam tace ke wani amsa kika bata nace bance mata komai ba don nafahinci bata san ciwon kanta ba ita.
Naso mu zauna mu fahinci juna amma hakan bai yuyuba a tsakanin mu don ita bata yarda da kowa ba.
Mun dade muna hiran matsalolina da maryam inda ta dan bani shawara sai dai ban fada mata komai ga irin abinda na fahinta dan zuwa garin mu danayi ba.
Bayan tafiyan maryam na fito wurin bakin na muka dan taba hira akai kiran sallah naje nayi la,asar na fito na shiga kitchen laraba ta biyo ni.
Nan muna aiki muna hira take banu labarin ai babu zaman lafiya tunda na tafi tsakanin shi da Nafisa kulun jidali ne akan yara da kuma zancen fita.
Yasa tsauraran matakai ashe akanta ranan da bakin ta take fadin wai ke ce kikai mata asiri dan kada ta zauna lafiya da mijin ta.
Nace kuma dai ita bata da aiki saina asirine a gidan nan wai wani riba ta samu akan hakane da har yanzu bata saduda ba.
Mun gama mun gyara part din na wuce zuwa part din shi na gyara ko ina banyi mamakin samun part din kamar tun gyaran karshe dana yi yake haka ba ba wani gyara a cikin shi.
Sai da na gyaro ko ina nasaka kamshi don har karni naji dakin yana min na rufo kofan ashe ban sani ba yanzu ni kadai ce keda key din dakin a hannu na.
Sai da na fito naji nafisa na fadin aiko a kwaita wato ni nawa key din ya karbe ya barwa wanan banza nata a hannun ta zai dawo ya fada min abunda yake nufi.
Kamar in wuce ta sai wata zuciya tace daina kyaleta na juyo nace ba komai yake nufi ba illa dai yarda ne ban taba daukan mashi komai a dakin ba kila ke bai yarda dake bace yasa ya karbe key din shi.
Kin san mutum shike sayawa kan shi mutunci idan bai sa ido ga abin wani ba waya sani ko kin masa halin bera ne a dakin.
Tashin hankali nan ko ta hau jidali zaginta dama irin na tab tasha ne daga zagin iyayye sai bakar ashar mai muni nace baki da maraba da yan tasha zama dake ma zunubi ne wallahi
Mace ba sanin Allah ba addini ba ilimi sai jahilci dake cin ki da bakin kishi ki koma ki san Allah zai fi maki ko dan tarbiyan yaran ki.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/19/21, 6:32 AM - Xxxxx: Bayan na gama tanadar komai dana san zaiyi amfani dashi har abinci na jera mashi saman d/table na dawo part dina na samu yan uwana bakina dasu Altine suna hira.
Zama nayi a wurin su kafin lokacin sallah ya karaso ban wani dade da zama ba time yayi na mike na shiga daki wanka bayi kafin alwala na fito.
Bayan na idar da har isha,i na zauna na gyara jikina tsab a cikin doguwar rigar mai kyau don sune kaya na in bada naje kebbi nake kokarin saka atamfa kulun ba a dan kwana goma sha danayi can.
Laraba ce ta kawo Al,amin wai yana rikici na karbe shi muka fito falon muka zauna muna dasa fira Altine tace yaron nan fa yanzu wayo yayi sosai don yasan yayi kwana biyu ba tare da mu ba.
Ina kokarin ciro nono in ba yaron nake fadin wai baba kayi wayo inji gwago kasan dangin uwar ka yanzu ko kabar su gwago.
Na dago kaina ina dariya a yadda Altine ta tsura min ido yasa na fasa dariyan ina kallon ta tace wanan tafiya kamar an canza ki ne baki daya.
Haka ake son mutum yaje gida aga canji a tare da shi ba irin zuwa gidan buzuwa ba dariya zancen ta ya bani nace kai anty ho.
Bamu dade da zama a gurin ba Altine na cikin magana sai ya shigo part din namu gaida baki na tare da tambayan su ba dai wani matsala ko ? .
Bayan sun gaisa ne ya juya ya fita mukaci gaba da hiran mu bai dauki wani lokaci ba mai tsawo da fita sai fa kiran shi ya shigo min a lokacin kira uku gana hudu na daga kiran da sallama.
Yace ki zo ki bani abinci mana sai ya kashe wayan ina shirin fadin ai abinci da duk wani abinda zaka bukata yana nan na aji mashi su sai naji ya kashe wayan nan take ban samu bakin magana ba.
Sai da ba dan bata lokaci wurin har na dan ci abinci na mike zuwa bedroom dina dogon rigan jikina na shafa ma oud kala kala sai body spray dana fesa a gabobin jikina dakyau.
Na fito na nufi wurin shi inda na samu yana waya na juya zan wuce bayan na dan tsaya bai gama wayan ba.
Muryan shi naji yana fadin ina kuma zaki je bayan nace ki kawo min abinci in ci abinci na d/table tundazun na fada a wani irin yanayi.
Yace ba gani ki zuba min mana na fice daga dakin na barshi a ciki ban dade a gurin ba sai gashi ya fito daga dakin .
Ya abincin baci gaba da zuba mai na gama tare da hada sauran kayan a guri daya sai jug din zobo dana sabo garin mu dana hada mai na matsa mai dashi a gaban shi.
Ya kalli jug din tare da fadin wanan may ye a cikin nan din zan bashi amsa sai ga Nafisa ta fado gurin kamar an jefo ta dakin tace Samad gurin ku nazo dama dakai da wanan yarinyar.
Don ke baki iya sallama bane idan zaki shiga wuri ko may ye hakan kikayi yanzu tace ba a koya min ba don bashi ta kawo ni nan ba yanzu.
Nace amma dai ke jan a binciki addinin ki don ragage ne kin ga don Allah malama ki bar nan don na gane manufar ki da kike muna hakan a ranan girkina ne kadai kike muna wanan dabian haka.
Do kawai kiga kin birkita muna farin cikin mu zuwa bacin rai saboda haka yau dai baki zo a sa,a don nariga da na gane nufinki a hakan
Ji wanan dama har wani farin ciki kike dashi a gidan nan miji dai kike kokarin cusa kanki a gare shi kuma baya yi dake yar iska.
Dani dake yanzu ai ansa wa miji ya daina yayi a gidan nan don ko makaho ta laluba yasan gwanatin ki ta kife a gidan nan sai yan dabaru kuma.
Oh dama burin ki ke nan wallahi komai asirin ki dole ki barni don na damaki na shanye yarinya na juya gurin shi nace kaji ke nan da kunnen ka har tana ikirarin da asiri a gaban kowa haka ?
Yace ke ku rabani da wanan shirmay haka Nafisa bar nan don Allah don ba lokacin ki bane yanzu tace nasan ba lokacina bane amma kasan ina da daman shigowa nan duk lokacin da na ga dama.
Wallahi karya ne baki isa ba idan kuma kin ce karya ne ki kara muna haka kiga abinda zan maki a gidan nan.
Kin mata kike kika saka wanan dokan a gidan nan kuma dayake nasan gaskiyan hakan na tsare wanan dokan don may ke ko yaushe kike karya wanan dokan.
Lalai wuyan ki yayi kauri a gidan nan har ni zaki kafa ma dokan ganin mijina komay kai wanan matar da abin dariya kike mijin ki ko mijin mu dai miji kan ai ya tashi a naki sai dai a jam,i don mata uku cur take mallaka daidai kuma kike da kimar kowa a cikin mu har ma mun daraki a wani fannin a gurin shi.
Wani irin bakin ciki da takaicina ya rufe ta a lokaci daya nan ta fara irin zaginta na yan iska zagin banza da baida dadin saurara ko fada.
Ke ya ishe ki kifice nan ai gaskiya khadija ta fada kin zo nan don ki bata muna farin cikin mu ne kawai tace zuwa nayi don in ji dalilin da zaka bar mata