MIJIN BUZUWA complete Hausa Novels.txt

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   16 / 144

45K to 48K   out of 431K words

ruda shi.
Da na dan shiga rudanin wanan abin amma yanzu maganan nan da kikayi yasani a hanya watau a takaice aboki na yana rudewa idan yaga khadija sai take mashi zubin yan ruwa idan ya kalle ta.
Tayi saurin fadin ya gano sirin da Allah ya boye ne anan ai khadija matar manya ce wallahi duk namijin da yai saa ta kalleshi da manyan idanun nan nata yakan shiga rudu ne ya rasa inda yake ina ga shiya take tsoron fita wallahi.
Don Allah malam idan kun gama kaja mota kakai mu inda zamu ko ka mayar damu inda ka dauko mu zaifi ya fada batare da ya juyo gare shi ba
Yi hakkuri malam abinda na gani na fada yasin khadija ta hadu ba karya a gurin nan kai mai dani inda ka dauko ni ya fada a dake.
Nidai nayi kamar badani suke yi ba kaina yana duke ina danna wayana dake hannu na muna charting da zarah.
Yusuf yace karkai fushi dani abokina gaskiya muka fada anan take a deep breath and confess khadija ta fi matan da kake gani haduwa.
Bude baki yayi ya zaro ido yana kallon yusuf da mamaki kalaman shi dayaji na bazata yasan Yusuf ne kadai duk duniya yake iya fahintar shi lokaci daya.
Yusuf ya sake kallo shi ya dan lagabe kai tare da girgiza mashi kai yace dont give me that look just say yes to your mind she is realy beautiful as you see.
Take ya daure fuskan shi tamau tankar bai taba dariya ba yace Yusuf kayi kuskuren furtan hakan a gare ni don kafi kowa sanin banda lokacin yin hakan .
Nace kunyi babban kuskure Yusuf da kuke son kamanta da wanan mutum matsoraci ko kuna zaton sakewan da nayi daku kun dauke shi da wani manufane ?
Ba so ko wani abu makamancin haka cikin zuciyana don ban taba daukan haka ba a tsakanina dakai sai mutunci da niyar taimakon ka a zuciyata don rayuwan ka na bukatan taimako da agaji ga wanda yasan shi.
Tsakanina daku kuma sai dangantarkar irin na zumunci na an fito wuri daya da biye min da kukeyi da kyautatawa .
Da ka sani da baka dauki haka ba da zafi don zuciyar ka ta baka ba daidai ba me yasa zakayi zaton soyayye zai yuyu a tsakanin mu don kana kyakyawa mai kudi maiji da ilimi da wayewa ko may ?
To ni duk wanan nasaban naka baya burge ni don ni ina fatan samun miji ne wanda yasan kanshi yake iya mulkata ba in mulkeshi ba ko wata tana mulkanshi.
Barin fada maka ban taba jin son ka wallahi a raina don halinka bai mun ba bai kuma taba burgeni ba tausayi ne da fatan alheri ka shirya da iyayyen ka takowani hali .
Don halinka da dabiar ka yanayin rayuwan da ka shiga da komai naka yana bukatan gyara a yanzu.
Ya isa yace da karfi ya fada cikin kuna rai, yayin da maryam tunda na fara magana take rufe min baki waina bar maganan .
Idon shi yayi mai jawur hankalin shi yana neman barin jikin shi zuciyar shi yana son tarwatse mai yace ba laifin ki ba ne.
Yaja wani irin huci ya furzar a bakin shi yace Yusuf ka juya mu sauke su inda ka dauko su don Allah.
Bana son inkara ganin fuskan yarinyar nan na tsane ta wallahi bana son kara haduwa da ita a rayuwa na .
Shiko Yusuf a ranshi ya gigice da fadan mu sosai yana rayawa yaushe ne zai samu cin ma manufar shi a kan mu yaushe zasu bar wanan halin may yasa Samad ke biye mata suna haka kamar wasu yara kanana.
Ya zama mai dole ya shiri mu tun yanzu tun kan mu rabu a hakan ba wani ci gaba gashi ya fara ganin hasken alamarin tun ba a je ko ina ba.
Ya zama dole ya gyara wanan abin tun anan don ba zai yarda abokin nashi yaci gaba da zama haka ba yanzu in ya bari muka watse a hakan abin bayi ba wallahi.
Naji Yusuf din yace Khadija ba nufin abokina ke nan ba baki fahince shi bane tun farko kin san tun jiya fa yana da haushin ki a ranshi don haka don Allah bashi hakkuri ya huce dake haka please.
Yadan juyo yana kashe min ido sai na gane manufarshi da sauri sai da na hade wani bakin ciki na iya furta to kayi hakkuri don Allah ban fahince ka bane na fada a sanyaye.
Da kyau Khadija matar na tuba ko bata laifi komai rintsi ya juya gurin shi yace kayi tsamanin jin hakan daga bakin ta yanzu a yadda tahau din nan.
Wani iri yaji yace a ranshi may yasa na kasa fahintar wanan yarinyar ne wai me yasa na fadi wanan maganganun masu zafi gareta yanzu bayan nasan gaskiya Yusuf suka fada.
Halinta daban ne da na sauran matan dake bina suna ribibin in so su kai tsaye zata iya fada ma gaskiya batare da tsoron komai ba kuma ya amfane ka.
A sanyaye yace Yusuf ban san may yasa take son bata min rai ko da yaushe muka hadu ba zan bata dama taci gaba da min yadda take so ko yaushe.
Motar ta tsaya a bakin wani plaza babba ba wanda yayi magana Yusuf ne yace bissimila mun iso mu shiga mu fito tukun.
Fita mukayi a motan har lokacin jikina a sanyaye nake jin shi don abinda ya faru a motan Yusuf ne yazo daidai inda nake yace khadija na gode da kika fahince ni ba komai nace dashi cikin yake.
Muna shiga shi yana bayan mu yana tako a cikin izza da kamala maryam tazo daidai kunne na tace dan dakata mai ku jera mana.
Hara na aika mata nace sai dai ya mutu idan sai na jera dashi din ya dai ci albarkacin Yusuf da kuma na iyayye wallahi.
Ban garen kayan yara muka nufa inda maryam ta fara duba kayan ina tayata har lokacin ban sake ba nan muka shiga jidan ma yaran kayan sawa da sauran abubwan yara.
Mu koma bangaren takalma da dasu sauran abin bukatan yara harda su tawul da sabule da su kulan zuwa school muka hado dashi a hankali na taka wurin kayan mata na zaba ma anty fati kusan kala goma masu kyau da tsada.
Su dai ido kawai suka saka min har lokacin da muka gama Yusuf yace mu zabi abinda muke so ni wani jakka da takalma kawai na dauka maryam kuma ta dauki wani dogon riga da jakka.
Munje gun biya muka da ja baya naga ya ciro katin shi na bakin ya basu suka debe kudin su suka miko mai mun shiga motar mun zauna.
Yace kina ganin mun sai komai da zasu buta nace insha Allahu har maman su ma da sauri ya juyo yadan kalle ni kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa yusuf yaja motan muka tafi.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Hutun sati uku kacal muka samu wanan karshen zangon don haka naji dadi sosai da bai kasance dogon hutu bane don zan samu zama a minna tare da iyayyena in yi hutu.
Wanda rabo da in samu kasancewa dasu haka a wadace har na manta yanzun haka na fito daga zana jerabawan karshe na wanan zangon da mukayi da yazo min da rikicin haduwa da Abdulsamad da abokin shi Yusuf.
Ba ranan zan tafi ba sai washe gari don haka maryam ta tsaya jirana don taso muje gidan yayar ta na nuna mata ban son zuwa can din.
Komai na gama shiryawa a dakin sai kayan da zan saka ne da katifa ban samu daga wa sama ba don kwantawa da zanyi na yau kawai da safe in dage shi sama in tafi gida.
Bayan mun rabu dasu yusuf ya kirani yana tanbaya na ya muka isa hostel din mu tare da kara yi min godiya .
Bayan mun kashe wayan gidan Abdulsamad suka nufa sun kusa shiga gidan ne Abdulsamad din yace dashi idan sun tafi kada a sauke kaya da aka sayo a gidan shi abar kayan acikin mota kawai idan sun isa Yusuf yagane manufan shi na fadin haka.
Sai dai bai ma abokin nashi magana ba gamay da abinda ya fahinta na son kada a sauke kayan dayace kada ayi har lokacin gidan ba dadi tsakanin su da Nafisa.
Wanka ya fito yana goge ruwa akanshi ta shigo dakin har lokacin tana nan cikin fushinta da shi zuwa tayi tambayan shi kudin da tayi requesting wana zata yi tafiya zuwa gida.
Tace Samad kwanaki na ta matsowa har yanzu bakai magana kan abinda na bukaci ka bani ba wanda zan je gida dashi indan zan tafi sai in wuce dashi.
Yadda take magana bai sa ya daga kai ya kalle ta ba Samad dakai fa nake magana ya dan wuce ta zuwa bakin gado ya zauna .
Ta juyo gareshi tace magana fa nakeyi maka kana ji kuma ta fadi a hasale sai lokacin ya dago yace kada ki kara yi min maganan nan.
Don bashi ke gaba na ba gobe kaduna zan tafi in daba iyayye da iyali na wani irin gumzi tayi tayo kan shi tana fadin wallahi baka isa ba.
Ba kuma inda zaka kaje na fada ma don baka fada min zancen tafiya ka ba don haka ban shirya ma tafiyan ka yanzu.
Murmushi yayi yace kice ma mai shirya min tafiyan don kece zaki sallamay ke nan ko ?
May kake nufi da wanan maganan haka ban ci na sani bane idan za kai tafiya yanzu koma ko da da kake fada min ni nake sa ka fada min .
Yace shine kuskuren da na aikata a baya yanzun kuma a shirye nake da na gyara komai da ya faru ido ta zuba mai cikin firgici take.
Ganin zata damay shi yasa ya fice ya bar mata dakin don da dakin yaso ya gyara kafin ya kwanta don ya kwana biyu ba samu tsayawa ya gyara ba.
Don yanzu gyaran dakin kwanan nashi ya dawo kan shi saboda indan yan uwan nata sun mashi gyara sai abubuwan da dama suyi ta bacewa a dakin.
Wanan yasa ya daina bari su shiga mai daki suyi mashi gyara sai shi ya ke gyaran dakin nashi da kanshi ya don yafi mai sauki idan bai gyara ba ita bata da lokacin gyaran .
Haka kuma zata shigo ta kwanta a cikin dakin ba kunya ba tsoron Allah haka dai ake rayuwan a dunkule ba wani jin dadin irin na aure tsakanin mata da miji.
Laptop din shi ya dauko ya na dubawa sai dai tunane ya hana shi yin wani aiki a ciki bakomai yake tunane ba sai irin maganan da nake fada mai, mai kama da shagube yana jin haushi na ashe gaskiya nake fada mashi.
Yaushe rabon shi da yaran shi suzo kusa dashi su zauna a matsayin shi na mahaifin su suji dadi babu.
Ya tanbatar da ya tafka babban kuskure da Allah zai iya kama shi da laifin da ba zai iya amsawa ba gobe kiyama.
Khadija khadija ya furta a hankali kin taimake kin ceci rayuwana ta yadda ban taba zato ba wanan wace irin yarinya ce mai hikimà da basira.
Ya dade a wurin zaune har ya kai kwance sai da wayan shi yayi ringing ya daga wani yaron shi na wurin aiki ke gaya mai an samu wasu filaye ns gwaunati a gwagwalada da wasu mutane ke son ci.
Yace da yaron nashi ya bari sai next week za a duba case din idan Allah ya kaimu sun gama waya kiran Yusuf ya sake shigo mai inda yake fada mai gashi a kofan gidan shi sin dawo da motaci an gama duba su .
Yace gaya nan fito mikewa yayi ya zura santala santalan kafan shi cikin wasu budaddun takalma ya sauko zuwa kasa inda ya samu falon cike da yan uwan Nafisa kamar suna shawara.
Ganin yadda ya fito yasa ta dago kai tana kallon shi ya fito ya samu Yusuf din zaune a saman dan wani dakali yana jiran fitowan shi.
Ya fito ya fara mai baiyanin komai basuyi aune ba sai ganin Nafisa sukayi a gaban su tana huci ba bata lokaci ta shiga dura ma Yusuf din zagi tana ai banta shi.
Bai tanka ta ba sai faman kururuwa take masu a kai tana kiran da munafuki dan bakin ciki ko bai so sai ya gansu da Samad agidan shi.
Dama tasan duk wani munafuncin da ga wurin shi yake fitowa daga shi har samad din sai ta dauki mataki a kansu.
Amma dai karki manta bakece Allah ba ko don haka babu wani abin da zaki iya muna sai Allah don in da sabo ya saba da wanan halin na Nafisa.
Sau da yawa idan sun kwaso rikici da mijin ta a kanshi take saukewa don tana ganin shine mai zuga shi sai taga ta kamo shi da kyau dan lokaci kadan kuma sai abin ya juye mata.
Wanda take ganin Yusuf din ne ke mata zagon kasa a hakan sai dai bai nasaran rabata da Yusuf din da yake son yi ko yaushe.
Da kyat yan uwanta suka samu takoma ciki bayan sun kare masu kallon banza suka shige da ita cikin gida tana ta haure hauren rashin mutunci.
Washe gari tun da safe ya shirya Yusuf yazo zasu tafi kamar yadda ya saba motoci uku zasuyi tafiyan da shi sai dai wanan karon tafiyan ya canza masu sallo.
Na farko su kadai ne ba tare da buzuwa ba na biyu kuma tare da a abin arzikin da bai saba tafiya dashi ba zasu dunfari gidan.
Ana kara gyara kaya kamar daga sama sai ganin ta sukayi a wurin motacin tana ganin kayan ta shiga tonawa har ta gano abinda ke cikin buhuhunan da akayi siling din su din.
Ranan sun ga masifa haka sukaja mota suka tafi ransu bace da halin da Nafisa ta nuna masu din sun isa a cikin lokaci gari bai je gidan ba sai da ya karasa gidan shi ya huta don sun iso kan shi yana mashi ciwo sosai saboda hayaniyar da baiso.
Tunda Yusuf ya sauke shi yanufo gidan nasu da abinda suka zo inda sai gani motane keyi anata shiga da kaya a cikin gidan ana jibgeasu a kofan hajiya mama kamar yadda ya umurce shi da yi.
Sun kasa boye mamakin su anty amarya ce ta fara tambaya anya wanan abin da Nafisa ko aka zo wanan karon dariya Yusuf yayi yace bada ita bace anty muka dai muka zo.
Mommu tace abin kan da mamaki gaskiya Allah yasa babangida ya canza daga wanan karon dariya Yusuf yayi yace insha Allahu mommy kudai taya mu da addua.
Ya shiga dakin hajiya mama don ya gai da ita ya samay ta da yan matan ta suna mamakin wanan sayyayan da suka gani haka wai daga gun Abdulsamad ya fito haka ?
Ya shiga dakin sai da ya zube kasa ya fara gaida ita sai faman murmushi take yi har lokacin ta kasa boye mamakin ta bayan sun gama gaisawa dakin take tambayan shi wanan sauyin yanan Abdul din data gani.
Yace hajiya adai taya mu da addua kusan kece sillar canzawan nan nashi lokacin fada maki komai baiyi ba amma nan gaba insha Allahu zan sanar dake komai so nake komai ya tafi haka yadda muke so dashi .
Don yanzu insha Allahu akwai canji sosai wallahi nan dai suka dan taba hira yace Abdulsamad na tafe zamuyi bayananin komai idan ya shigo.
Duk da zaman lafiyan da akeyi gidan bai hana a kebe gefe ba ana gulman wanan sabon yanayin da aka hango a gare shi.
Sai dai kowa ya matsu yaga abinda ke cikin buhuhunan wanda ba wanda ya iya gane komau ye a cikin su su indan gaiyan aikin nasu ya shigo.
Saida suka sauko sallah jumma a ya shiga gidan iyayyen nashi a falon Alhajin su ya fara shiga ya gaida shi da mashi yaya jiki ranan yaga sauyi sosai na sakin fuska a wurin mahaifin nashi wanda ya dade bai gani ba.
Bayan sun gama da mahaifin nashi ne ya shiga ciki ya fara gaida ummi sai mommy sai anty amarya ya wuce dakin hajiya mama wanda dama kullun itace karshen shiga da yafito kuma sai ya bar gidan.
Sun gaisa da ita acikin sakin fuska ya dubi Affan dake zaune gefenta yana cin abinci ya kira yaron saboda rashin sabon da basuyi ba dashi ya dago ya kalle shi kawai ya gaida shi.
Sai baiji dadin yadda yaron yayi mashi ba shiru ya dan biyo dakin take tambayan shi iyali ya amsa da duk sina lafiya hajiya tace dole ita da yan uwanta zamu tambaye ka don sune yanzu iyalin naka.
Babangida yanzu kana ganin abinda kakeyi kana aikata daidai a rayuwanka mutum ya watsar da iyalin shi ya rugumi wasu bare can.
Shiru yayi ya dukar da kanshi tace kaima kanka fada kada ka mutu a cikin wanan halin kasan Allah na zai barka ba Yusuf ne yace ayi hakkuri hajiya komai zai zo

16 / 144

Chapters