MIJIN BUZUWA complete Hausa Novels.txt

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   84 / 144

249K to 252K   out of 431K words

dade a gurin zaune ina tunanen kalaman anty a raina lalai ya zama dole gare ni na gyara komai nawa kamar yadda anty tace min ga magani a gonar yaro baisan kan sa ba ke nan.
Shigowan shi ke nan ya nufi gurin nafisa ya dubata yayo dakina daga can daga ida nake zaune a kasa saman center carpet na mike kafafuwa.
Jin an turo kofan ne yasani daga kai na kalle shi sannu da zuwa nai mai tare da fadin ka dawo ?
Na dawo khadija yau ban tsaya kusa ba munyi balaguro ne zuwa keffi acan muka bata lokacin mu yanzu sai wanka ke nan tunda ka kwaso wanan gajiya.
Kinyi tunane mai kyau gaskiya barin dan watsa ruwa in fito kafin nan nasan abinci na ya kammala.
Insha Allahu na bashi amsa ina kokarin mikewa daga inda nake zaune dukawa yayi ya debi corn din danake ci a gefe na.
Har ya kai kofa ya juyo yana fadin hajiyan mu tace a fada maki za a kawo lefen zainab a karshen satin nan insha Allahu.
Da murna na dago ina fadin masha Allah gaskiya nayi murnan jin hakan wallahi ashe zainab ta kusa bin layin mu bada jimawa tunda har lefe zaizo.
Baki ya tabe mi yace kinji dadi ke nan za ai mata yadda akai maki koda yake kawaye kuke waya sani ko matsin ku yasa akai maku hakama.
Wani kallo na watsa mai tare da fadin kana da gaskiyan ka tunda ka tauye ni.
Dariya ya wuce yanayi har ya fita kitchen na shiga na hada mai abincin shi na tsaya na gyara komai yadda ya kamata in yi na fita zuwa wurin shi.
Sai da na aje abincin na shiga daki wurin shi tsaye na samay shi yana juya kwalban da wasu abubuwan da na tsinto a karkashin gadon shi.
Yana ganin na shigo ya juyo gare ni yana fadin wanan may ye kuma haka Deedar ?
A karkashin gadon ka na jawo shi dazu nan dai na fada mai yadda akayi tun dawowana gidan ni da maryam.
Kai kai yace yana zama saman gadon tare da fadin wanan abin wai da may yayi kama haka nace waya kawo shi nan to ?
Yace wa zai kawo kuwa banda daya daga cikin ku tunda daga ni sai kune keda alhakin bude dakin nan yanzu.
Allah ya kyauta nace na dago ina fadin kayi wankan ne yace shi zan shiga ai naga wanan abin a kofa nace nina aje don kazo ka gani da idon ka.
Ya juya ya samu leda ya saka tare da adana abin jirani in fito dakin ki zamu koma sai nayi bincike akan wanan abin.
Yana shiga ban dakin ban zauna a gadon ba na juya inda na hada kayan abincin dana shigo mai dasu a cikin basket.
Ya fito a gurguje ya shirya muka bar dakin zuwa nawa ranan a can muka kwana wanda ina jin dadin hakan don ina sakewa sosai idan yana dakin nawa.
Asuban farko dukan kofan nafisa ne ya falkar damu cikin sababi take fadin iya shegen da kake yi a gidan nan yayi yawa.
Samad kaine ma mai biyo mace dakin ta ka kwana yana son fita na girgiza mai kai nace dashi kyale ta please.
Ya koma ya kwanta sai da akai kiran sallah muka tashi a dakin shima yayi sallah bai fito daga dakin ba sai bakwai da rabi.
Ashe tana falo zaune zaman jiran shi yana fitowa ta fara mai ihu da sowa wai yaji kunya gotaigotai dashi yana bin karamar yarinya dakin ta yana kwana.
Nafisa kina da hankali kuwa ke ba dakin ki nake binki ba yanzu tace idan ka bini ai da amfanina ko dan yanzu da nake cikin wanan halin.
Ita bata da amfanine gareni tace ina taga amfani banda ci takai masai mai take tsinana maka kai nafa san komai na fada ma duk wanan rufa rufan da kakeyi nasani.
Ashe dai har yanzu ke nan labe kike muna kenan tunda har kin san haka gashi yanzu ma alama ya nuna kan shi tunda har kin san a dakin ta nake kwance.
Na sani samad don na damu dakai ne nake haka yace ban saki damuwa dani ba tunda kin san bake kadai ke dani ba.
Wallahi baka isa ba samad sai ka dawo kana fadi da bakin ka a tsakar gidan nan ka kwaso mai farar kafa mara moriya a gare ka.
Yace ban yi mamaki ba don kin san sheri da kika kula zaki ko sha kunya a gidan nan wallahi don babu ida zata tafi.
Banyi mamaki ba don jikar mayu ka aura ta kama ma kurwa baka ganin laifinta a yanzu do an gama dakai ko.
Yace ke mahaukaciya ce kula ki ma hasara ne kiji da hakin da kike ciki zai fi maki alheri sakarai kawai ya shige .
Cikin daga murya take fadin zaka gane baka da wayau samda karka manta a tadin hannuna kake wallahi bai kula ta ba ya shige abinshi ya barta a wurin.
Ranshi a bace har ya karasa shirin shi ya zo ya karya bai kara bi ta kanta ba don ya gane idan ya biye mata zasu sai da haline kawai a gurin.
Koda muka fito yau a tare muka jero dashi don fita zuwa school shi kuma zai shige office abinsa nafisa da tawagan ta suna zaune falon nan ta dasa sabon balai kamar yadda bai kulata ba ni haka nazo cikin shiri na wuce su a inda suke zaune suna banbami.
Tunda muka shiga motar takaici da haushin tozarcin da tai mai ya hana shi magana nima ban bi ta kansu ba hankali na na mayar a wayana.
Mun isa suka sauke ni a kasalance yai magana da cewa yau ma ina ganin keffi zamu je wani aiki da wuya in dawo gida yau.
Allah ya tsare hanya nai mai da a dawo lafiya ina kokarin bude mota naji ya rike ni tare da fadin wai fushi kike ko may ?
Kallon shi nayi tare da dan murmusawa nace fushi akan may ? may ya hadani da maganar ku da zanyi fushi kuma?
No khadija idan ya kira full name dina nasan magana ce ta serious zai yi don haka na mayar da hankali a gare shi ina sauraren shi.
Kada kiji wanan yar fitinar na fadin wai ina kwana a dakin ta ki dauke shi wani abu wallahi banyi hakan don wani manufa ba.
Sai don tsaron lafiyan abinda ke cikin ta kawai nayi haka don hawa saman ta sauko zai iya jawo mata wani matsala again.
Don wanan tunanen yasa, , , , haba dai ni fa wanan ba matsalata bace asalima ban san da wanan zancen ba a rayuwa na.
Tunda ba hakkina ka dauka ka kai mata ba ban damu da duk wani rayuwan da kuke yi a cikin gidan nan ba idan ba wanda ya shafi bangarena bane.
Murmushi yayi yana hade wani kololon bakin ciki tare da fadin take care tunda ya kula ban son maganar da ya dauko min din nace dashi insha Allah.
Na sauka daga motar ya ja suka wuce ni kuma na shige ciki duk da nayi kokarin wanan maganan amma sai naji wani bangaren zuciyana yana kokarin kishin hakan ga Nafisa.
Da sauri na kawar da wanan zancen a bangare nace damuwa na may tunda ba hakkina yakai mata ba alhalin kuma gashi yanzun ma ya fadi dalilin shi na yin haka gare ta.
Ni komai nene suje suyi tayi ai tare na gansu na kuma san gidan da na shigo dole ne sai na yaki zuciyana daga wasu abubu na kawar da kaina gare su .
Muddin ina son kwanciyar hankali a tare dani da salama yawan sa rai ga zamantakewar kishiya da miji da saka ido ga abinda sukeyi shike kawo rashin kwancinyar a zukatan kishiyoyi.
Kamar yadda ita take yawan saka ido akan duk wani motsi nawa shine silar hanata samun salama a zuciyar ta.
Idan na biye ma wanan halin nata nace zan dau fansa a gare ta nice zan sha wahalan haka tunda ance wanda ya rigaka kwanci yana riga ka tashi .
Da wanan shawaran na shiga ciki na kama normal life dina na school mun dauki lectures muna fito wa sallah muka nufi gidan wanan matar da anty hawau ta hadani da ita.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Akwai mata duniya don gaskiya nayi mamakin ganin wanan matar da anty hauwa ta turani gidan ta daukan darasin rayuwa a gurin ta.
Bayan mun gaisa da matar take tambaya tare da maida hankalin ta a gare mu tana fadin daga cikin ku wacece mai daukan darasin nawa ?
Maryam ne ta bata amsa da fadin dukkan ne anty don duk muna da bukatan hakan dariya matar tayi cikin hausanta da bai biye ba tace wacece matar auren maryam ta nuna mata ni da hannu.
Ta kalle ni tare da fadin very nice ai dukkan ku kina da quality din da namiji zai so ku a take idan kin iya rike miji kwana nawa ne kin kama abinki ga hannu basai ki tsaya wanan hali na matan kasar nan ba bin bokaye da malamai bashine mafita ga mace ba.
Sai dai wa yanda suka yarda da wanan akidar a wurin su yake mafita gare su amma idan mace zata zauna tayi amfani da hikimar ta da basira da Allah yaba mata sai taga ta kama mijin ta da hannun ta a saukake.
Ba wani abu mu matan waje mukafiku dashi dan banbancin kadan ne a tsakanin mu daku ku matan nahiyar nan kunya ne ko girman kai yake yawan damun ku.
Zaki ga mace na jin nauyi ko shakkan idon jamma,a ba zata iya sauke nauyin da Allah ya dora mataa kan mijinta ba.
Unlike mu kinga ni nan ko a gaban iyayyena nake ban shakan sauke nauyi mijina a gaban su No bawai kinji nace haka ki tunanen ina nufin kiyi fitara a gaban mutane bane,
Abinda nake nufi shi namiji yana son a riritashi ako wani lokaci ko agaban waye amma sai kiga mace sam bata damu da jawo mijin ta a gareta ba irin haka ne mata da yawa suke samun matsala a gidajen su.
Sai kiga namiji yayi aure daga baya matar tazo tana mashi abinda ke kika yi sake dashi a baya can wanda hakan laifin ki ne.
Ki cire kunya da nauyi kowa a idon ki ki tuna kuma kisa a ranki bautar Allah kike a hakan don babu waani wanda zaki daraja bayan iyayyen ki sai mijin ki.
Aljannan ki fa akace yana ga tafin kafar mijin ki ashe ko bazaki bada karfin ki da lokacin ki wurin ganin kin gina aljannan ki da hannun ki ba.
Zama muka gyara tare da ajiyan zuciya muna sauratlren wanan matar mai bada nashina kamar lectures taci gaba da fadin.
Ke bazakiyi tunanen irin nasa nauyin da yake sauke wa kanshi na hakkin ba kiyi tunanen wani abu zaki masa kwatankwacin wanda shima yake masa ki farauta masa rai.
Ashe ko duk wani abinda muka san zai sasu farin ciki ya zama wajibi muyi shi namiji shine zai ciyar dake ya tufatar dake ya biya maki dukkan bukatun ki nayau da kulun naki dana yan uwan ki.
Ke har da rabo idan ya ratsa a tsakanin ku koda yake ke ina ganin amaryace yanzu ko muka amsa mata da eh.
Tace to Allah ya baku zuria dayyaba muka amsa da amin tace kada kiji na zake ina maki wanan nasiha haka ke da kika zo in koyar dake dabarun mata.
Na dauko maki tunatarwa ne daga farko ta yadda zaki iya fahintar abinda zan fada maki a gaba da fatan kun fahince ni maryam ne ta amsa da kwarai anty muna biye dake ai.
Tace Alhamdullahi tunda kun fahinci inda na dosa taci gaba da fadin shi namiji da kike gani da zaran aure ya kullu a tsakanin ku daga ranan an bude maki wani sabon babin rayuwa ke nan.
Don haka wani jiji dakai da ko musu da sauri fushi ya kare a gare ki daga wanan ranan dole ne ki zama mai biyayya a gareshi.
Duk wani abinda muka san zai saka zuciyar su a farin ciki ya zamo dole mace ta juri yi ma maji shi muddin abin bai kaucewa shari,a ba.
Maryam tace kwarai anty tace kin gane ke nan shin kun san abinda yasa mazan ku na wanan kasar suke son auren matan waje ko wata kabila ta daban da naku ?
Wanan abin yana daga cikin abinda suke kwadayi wanda akasarin matan su sun yarda shi saboda kunya da dahun kai kan aure .
Suna hangen kwaraiwan wasu da kwadayin halaiyarsu na iya tatalin mazajen su da kwantar da kai a gare su.
Ladabi da biyayya ga miji tare da mutunta juna gami da sadaukar taimako tare da jajircewa a cikin zamantakewan aure.
Kun ga wanan abinda na lissafa maku bakomai bane auren facewa wanan gishin kin rayuwan da nai maganan su yanzu idan kin rike wayan takar kin rike kan maciji ne da hanuwan ki don ana son mace tazamo mai wanan halin a rayuwan ta.
Sai kiga ba mijin ba kadai da kowa nasa kin gama dasu a lokaci daya sai dai fa wani kari daya zuwa biyu dana manta ban fada maku ba sune.
Karbi, karbi ga dangin miji da abokai yana kara haska mace a gidan mijin ta sosai haka kuma godiya ga alheri zuwa ga miji yana daukaka darajan mace.
Sannan shi yawan bukata kullun ki ce saya min wancan babu wanan sai ta girgiza kai tare da fadin kin ga abu mai muni dake saurin durkushe mata yanzu.
Duban lokocin da maryam tayi a wayan ta yasa tace damu barin barku haka idan kun kara shigowa ma karasa sauran bayanin kafin mu kai ga darasin mu.
Amma kafin ki tafi yanzu barin baki wani abu don baji amaryan tana kamshi irin na rikakaun amare ba mikewa tayi tashiga daga ciki.
Maryam ta kalle ni tare da fadin kam uban nan duk wanan kamshin da kike zabgawa kinji matar nan wai bai yi ba nace maryam aini yau naji abu wallahi.
Fitowa tayi dauke da kwalayen a hannun ta tana kokarin sakawa a wani leda blue ta miko mun tace wanan idan kin karanta akwai sauran bayani a cikin sa kafin gobe ku shigo ko jibi.
Godiya mukai mata muka miki tsaye don barin gidan Nepep muka shiga muka koma school don acan za a zo a dauke ni.
Har naje gida maganganun ta suna min yawo a zuciyana da yake bai nan tun shigana na rufo part dina tunda nasan ba kara fita zanyi ba ranan.
Ban dade ba barci ya dauke ni a can cikin barcin nawa nai mafalki da Nafisa wai ina duke ban san da zuwan ta bayana ba tayi kokarin turani cikin wani rami Allah ya taimake ni na rike wani farin abu mai tsawo kafana yana daga cikin ramin ban riga da na fada ba.
Na dago na kalleta tare da fadin bazaki taba cin nasara akaina in Allah ya yarda sai ta kara yunkuri turani a ramin razana yasani ambata inna lillah da karfi.
Zubar na mike daga barcin ina yanka wani iri zufa a goshina tsoro ne matuka ya kama ni gashi ni kadai ke a dakin.
Wani irin tsoro nake ji yana rufe ni a lokacin addua na fara karantowa sai wajajen asuba barci ya dauke ni har nakai ga makara.
Wanan mafalkin ya tsaya min a rai sosai haka har na gama shirina na fito ranan nayi mamakin yadda ban samay su a falo ba kamar kullun.
Na isa school na samu an shiga sai dai malamin yana gab da shigowa a lokacin wuri na samu na zauna ina mai ci gaba da nazarin wanan mafalkin a raina.
Har malamin ya fito yayi abinda zai muna muka gama lectures ranan jikina banda wani kuzari sosai .
Haduwan mu da maryam yasa na dan sake kadai sai dai idan na tuna da mafalki nakan karatun Allahuma ajirni fi masibati wa,akalifli hairun min ha.
Bayan mun sallamay sallah da yake ban karya ba a lokacin sai nake jin kamar zan fadi don yunwa maryam ce ta sawo min lemon kwalba da snack na dan sha rabin goran na aje sai dai ko ina bai kai ba na amaye shi duk.
Kin san baki ci komai ba dole sai abu mai dan zafi ne zai zauna maki a ciki dole mikewa mukayi da jikina yadan sake muka nufi gidan anty Salbiya don karin ilimin da muke so na zaman duniya.
Bamu dauki lokaci ba muka isa gidan anty Salbiyan saida akai muna iso saboda tsaron da gidan ke dashi duk da gidan bai kokai rabin gidan AA tsaruwa ba da fasali.
Sai dai rashin tsari da yawan jamma,a da gidan namu ke dashi ya jawo baida wani tsari yanzu ga kowa.
Bamu dade zaune ba ta fito fuska

84 / 144

Chapters