MIJIN BUZUWA complete Hausa Novels.txt

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   92 / 144

273K to 276K   out of 431K words

Sai maganan Laraba da nake son yi yanzu kin san kwanaki mun taba magana kanta cewa kin gaji da zama da ita kina son a kawo maki yarinya har karo biyu kina min wanan korafin akan laraba ina baki hakkuri.
To yau Allah ya kawo iyakar zaman ku da Laraba don kin san Laraba yar uwatace ta jini bazan cire ta a cikin jini ba kamar yadda nasha fada maki haka ita din jinina ne ita din.
Don haka yanzu zaman laraba zai koma Abuja wurin khadija ke kuma sai ki dauko wanan yarinyar da kika ce an maki magana a kanta.
Shiru tayi sai can tace amma hajiya da an fada min a shirya su ko yanzu gaskiya basu da shiri don ko wanki ban masu ba.
Shirmay banza ke nan ai in don wanki ne idan kin yi tunda Yusuf yana hanya ko yaushe sai ya kai masu .
Laraba aka kira hajiyan ta sheda mata zancen zuwan ta a gaban mu tace tau hajiya can kuma Allah ya maida zama na tace eh don ita din can yanzu tana da bukatan mai taimaka mata da wasu abubuwan gama kin ga yanzu gashi azumi ne tafe kuma ga yara zata dasu.
Kinga zaki dan rage mata wani abin a can tace hajiya banda zabi duk yadda kuka ce haka za ayi yanzu zan dan je in kwaso komatse na sai nazo mu tafi sai dai zan bar sauran kayana sai a aika dasu gida daga nan wurin ki.
Tashi tayi zuwa shiri inda ta bar anty fati zaune bata ce komai ba sai zuwa can ta mike tana fadin zata je ta hado kayan yaran.
A gaskiya banji dasin yadda akai mata din ba sai dai babu halin magana a wurin don ba wurin magana bane.
Amma a gaskiya ta yaya ta zaune da ita kalau yanzu kuma a dawo ace ta koma gurin kishiyar ta ke nan nima watarana za a iya rabata da wurina din don bata yin kanta sai yadda aka juya ta ke nan.
Muryan hajiya ne ya katse min tunane na tana fadin kada ki damu dama zaman Laraba da Fati ya ishe ita Fati din don tasha min korafi yar uwata ce Laraba ta gurin uwa kin ga ita din jini na ce sosai.
Ba zanso kaita inda baza a kula min da ita ba yadda ya kamata ba dai sai na fada maki komai ba a yanzu zaki komai a gurin Laraban.
A raina nace ai kaji matsalan nikan an barni a ciki dana sani in dauko a bangare na kamar yadda ya bukata inyi tun farko.
Mikewa hajiya mama tayi ta samay shi a falon Abba tana mashi bayanin halin da ake ciki na zancen tafiyan da ta tsara yanzu.
Ba wanda ya musa mata don bayanin da tai masu akan haka sai Allah tsare hanya da Abban yayiwa jikokin nasa a lokacin.
Fati bata aiko wa yaran da wani kayan kirki ba hajiyan ta fara fada ina shigowa daga dakin mommy dana fito wurin ya Amina da ta shigo nace ai babu komai Allah dai ya kaimu lafiya.
Tunda muka fara hanya ba wanda yai magana a motar sai da mukai nisa ne daddy yace zai sha ruwa na dauko goran swarm na bude na bashi ya soma barci.
Allah ya sauke mu lafiya duk da gajiya muka fito daga motar tundai ni dana jirkita irin na ranan da muka je kaduna wanan dalilin yasa yai min magana ya sauke fushin da yake dani akan kin amsar girki a kaduna da banyi ba.
Muna shigowa na bude part dina muka shiga kafin kace may labari ya samu Nafisa na dawowan mu gidan har da yara muka dawo da wata mace.
Tace what in dai ba Fati bace tazo wa zaizo gurina da yara kuma mun shiga inda na barsu zaune a falo ban daki na fada sai da na amaye dan abinda ke cikina na karin safe danayi na samu sa,ida a raina.
Duk da yamma yayi sosai a gagauce nayi sallah na fito daga dakon na samay su har laraban zaune a takure falo.
Nace don Allah mama kuyi hakkuri na dan shiga ciki rage lalura ne ku taso muje daki ina kokarin shiga dayan dakin da kayan ta.
Tashi tayi ta biyo bayana inda na aje kayan tare da cewa sannu da shigowa sabon rayuwa mama ubangiji ya kawar da shedan a tsakanin mu ya bamu zaman lafiya da juna tace amin yar nan.
Kitchen na koma na dora girki a gagauce na hada muna abinci duk da dare ne bai hana in girka abinci mai inganci ba a lokacin.
Sai tara saura ya shigo dakin muna zaune a falona muna cin abinci a plate daya da yaran sai mama laraba dake gefe daya tanas cin nata ita kadai.
Wuri ya samu ya zauna saman kujera ya fara gaida mama laraban da gajiyan tafiya sai ya juyo gare ni yace ya jikin naki yanzu ?
Da sauki na bashi amsa ina ci gaba da cin abincin da nake wanda dama bawani ci nake ba tsakura nakeyi don ma in dan ci yasa na hada hannu da yaran muna ci.
Yace mama yau gaki Allah yai dawowan ki Abuja kuma da fatan za a zauna lafiya da kowa a cikin amana da yarda tace insha Allahu.
Ya mike bayan ya gama maganan da zai yi ya fita nayi mai saida safe nace yara suyi mai suma sukace mai saida safe Abba ya amsa ya fita.
Laraba dake gefe tace uhumm sai dai kin koya masu ai sannu a hankali zasu iya ai din babu wannan shakuwar a tsakanin su irin haka.
Murmushi nayi nace komai yanzu sai a hankali ai mama bamu jima ba muka shige kwana.
Washegari ko da na tashi jikina ya matukar mutuwa sosai yai min nauyi ga kasala da kyat na iya fitowa na hada masu abin karyawa suka karya nikan daki na koma na dunkule.
Barci nayi sosai a wurin har mama taiwa yaran wanka ta shirya su ban fito ba sai da AA ya shigo ne yana tambayan ina cikine mama ke fada mai ai tun safe na shige banjin dadin jikin ne take gani.
Dakin ya shigo tun daga kofa ya tsura ma yadda nake kwance ido har ya karaso gare ni inda nake kwance bargon dana rufa ya yaye na bude idona da yai min ja na sauke a kan shi.
Yace may ke damun kine Deedar nace a kasalance jikina dai ke ciwo na kwanta in huta yace oright idan dai wani abin kike ji ki fada min muje asibiti a duba ki nace lafiya ta kalau.
Mikewa yayi yana fadin yau bazaki shiga school ke nan ba nace sai dai gobe idan Allah ya kaimu gaskiya .
Ni zan fita yace idan akwai abinda kuke so sai ki kirani a waya nace idan zaka dawo dai ka riko muna pop corn wasu daddy da sauran abin yara dan Allah ?
Kallona yayi ya girgiza kai nace da kyat please don Allah kaga yau ni ban fita zanyi ba yace yaji Allah ya sauwaka ya fita.
Mikewa nayi na shiga ban daki na fito wayana yana kara na dauka maryam ce a layin ina dauka take fadin ke yar dadi miji yau ke nan ba zaki fito school ba ko ?
Wallahi maryam jikin nan nawa yau sai a hankali sai dai gobe idan Allah ya kaimu tace ai ganinan zuwa na dubaki idan mun fito sai kinzo nace na kashe wayan ina kallon lokaci.
Sha biyu da wani abu na rana nace kai ashe lokaci ya shige ne tashi nayi zuwa falo na samu su laraba da yaran a zaune ko tv basu kunna ba.
Gaida su nayi nace mama shine ba a tayar dani ba ga har rana yayi sosai kallon yaran nayi ina tambayan su may za a dafa masu abincin rana ne ?
Wanan yace indomie wanan yace taliya nace bari mu raba gardama yanzun barin maku taliya din gobe sai ayi indomie din.
Na juya wurin Laraba ina fadin mama ai zakici taliyan ko tace zanci mana uwar dakina may ye bamu ci acan mu.
Kitchen na shiga na hada kayan miya na jajjaga tare da dauko tukunya na zuba ruwa na dora kan gas din fridge na bude na dauko nama na yanyayanka na wanke na zuba a tukunyar tare da zuba gishiri na kawo
albaaa na yanka a sama
Haka dai har na hada abincin yadda nake so na rage gudun gas din nawa na fito falo wurin su na zauna muna hira dasu.
Gaskiya ko ba komai ashe zama da mutum dadi gare shi ga yau kawai naji dadin kasancewa dasu a tare dani part din.
Da ko sai ni kadai zan zauna idan ba waya ba ko tv banda abokin fira a a part din shigowan maryam yasa muka mayar da hankali a gare ta tace ke shegun buzayen nan su tare ni waje sai tambayoyi suke min wai may na dauko a jakata sai na bude masu sun gani don basu yarda dani ba.
Nace ga yan wulakanci zanyi maganin shegu kuwa tace bakiga yadda suke wani zare min ido ba wallahi har tsoro ne ya kamani.
Mikewa nayi na fita zuwa wurin su a bakin get din ko hijab ban tsaya sawa ba a jikina tun daga nesa nake kwala ma wanda nagani a kofar kira ya wani nuna kan shi wai shi.
Zuwa nayi a bakin get din nace wa ya baku ikon bakona idan zai shigo gidan nan sai kun caje min shi yace hajja dokane muka samu yin hakan daga sama.
Wayan dake hannuna na kira AA dashi suna kallo na nace da ya dauka kai kaba wa yan nan buzayen dake get din gidan ka doka idan bakuwa tazo wurina su caje ta don yanzun haka sukai ma maryam har da so taba jikin ta.
Yace what wa ya basu wanan dokan haka gurin bakin ki nace haka sukace ina juyawa ciki bayan na gama masu masifa da warning din su don nasan inda dokan ya fito yanzu.
Ina shiga rike da hannun daddy dayan su shima ya shigo ya nufi gurin nafisa dake zaune falo yanzu cikin jikin ta ya girma sosai.
Na barshi nan ya duka yana fada mata sai gashi wai ta aiko in je kin zuwa nayi don nasan maganan banza zanji idan naje din abinci na juyo muna na na kawo falo.
Mun baje muna cikin cin abinci sai gata ta shigo falon da kanta ba sallama kamar kulun na dauki wanan dabianta ne haka ta saba shiga guri tunda har mijin ta naji yana korafin hakan.
Zata fara magana na dakatar da ita da fadin malama may ye haka kamar wace ta shiga church babu sallama kuma.
Tunda zuwan ki nan ba alheri bane ki fice min daga shiya don bakiga kafana a gurin ki ba ke fitsarariyar mara kunya nace dakata may kika gani anan yara ko.
Don Allah kada ki bata ma yaran nan tarbiya da halin nan naki mara kyau kamar yadda kika bata wa naki tarbiya kallo takai ga yaran da laraba tace aikin banza sai kuma ta fasa fadan daya kawo ta tace.
Idan mutum ya isa ai ya haifi nasa ya daina karice karicen diyan mutane a furin shi a haka dai zaki kara da kalar diya a shiya badai ki haihu ba.
Nace idan na haihu tunda kece Allah sai ki kashe diyan mu gani gaki bakar manya kike kiran wani maye ashe tunda har kin san gaibu.
Ta hayyako na mike tsaye ina fadin Maryam rufo min kofa nan don Allah yau in koya ma matar nan hankali a gidan nan .
Jin haka yasa ta fara ja da baya baya tana fadin dama an fada min haka kuke yan cin mazan mutane idan kunga anfi karfin ku sai ku nuna karfin doya ga mutum.
Har ta fice da wayo tabar dakin dariya muka sa maryam tace shegiya yau kin gano takon yar iska a gidan nan ai ashe dama tana da tsoro haka take iskanci.
Laraba tace ina ina za a hada girman jikin su ba daya ba idan uwar dakina ta danke ta aisai buzunta dama haka hajiya uwar yaran nan ke tsayawa ta kwaci yancin ta ai da abin bakai haka ba.
Amma yadda kika san uwa da yar ta haka muka zauna a gidan nan a baya lokacin ba a nan muke ba dawowan munan kuma abin ya kara lalacewa tsakanin su da maigidan.
Maryam tace ai ma kasa ki yarda ki hada jiki da yar iska don ance tsiya yake kawo wa a gida fada kana hada jiki da kishiya haka.
Nace nima ai hauka nai mata ina zan fara taba ta da wanan tsohon ciki haka a samu na bin gari dani ana nayi kashin kai.
Ashe tana fita ta kirashi ta kwashi karya da gaskiya ta fada mai sai gashi ya kirani yana fada da daukan wayana babu ko sallama sai fadin Deedar kina haukane da zaki biyewa Nafisa da tsohon cikin ta ki nakasata ki mai da ni baya.
Duk abinda tai maki bazaki jira in dawo gida ba sai ki far mata da fada har kina shirin dukan ta a wanan yanayin da take ciki haka.
Sannu mai mata nace mai tare da fadin ai bansan mijin tace kake ba sai ka nuna min yau na kashe wayan abina.
Maryam tace wa mama laraba kin gani ko kirashin fa tayi yanzu ta kwashi karya da gaskiya ta fada mai shi kuma ya hau ke nan.
Nace idan ma ya hau ai sauka zaiyi don ba zan yarda da rainin wayon kowa ba a cikin su yai min kira yafi a girga naki daukan wayan ina gani ban daga ba.
Muna gidan da maryam sai bayan magariba ta bar gidan zuwa gidan anty ta tace acan zata kwana don yanzu zaman hostel din bai mata dadi da ban nan.
Sai dare kamar yadda ya saba shigowa ya dawo gidan sai da ya watsa ruwa ya sa jallabiya ya shigo dakin namu rike da ledan popcorn daya sayo yana shigowa ya mikawa yaran sun karba babu godiya nace baku godewa Abba mana ko ya karbe abinshi ne sukace sun gode suna hada baki wurin fada.
Gaida laraba yayi ya juya ya na fadin kai min abinci nace naji ya juya ya fita daga dakin nawa sai da ya dan jima na mike na shirya bayan nace mama ta rufe ta ciki idan na dawo zan kwankwasa sau biyu tace to.
Na riga da nayi warning din yaran da kada su fita ko ina idan ba dani ba koda wani na fice zuwa wurin shi kai mashi abincin.
Yana zaune a d/table din na shigo da sallama ya amsa min ciki ciki na isa na fara jerawa baiyi magana ba sai dana gama na juya nima ba tare da na yi mashi magana ba naji yace.
Ina zaki na juyo nace mai daki zan tafi yace dawo ki zuba min ina zubawa har na kusa gamawa yace don may nake kiranki baki daga waya ba.
Ban kusane ina kitchen na bashi amsa yace da kikazo kikaga miscall dina fa shiru nayi mai ban tanka shi ba.
Ya ja plate ya fara kai abincin sakwara ne da miyar agushi maryam ta taimaka mukayi tunda nafisa tai maganan doya muka sha dariya.
Shiru wurin ya dauka ba wanda yai magana a cikin mu wurin sai da ya kusa gamawa ya dago kai yace nice mijin tace ko ?
Nace in ba haka ba daga jin magana ta bangare daya zaka hauni da bugu don ni naza juyan da take fada min ko may ?
Haka kawai zan zauna ta shigo min har part dina da cin mutunci amma naka laifinta ba sai ni da ta sama din tunda ni ban san daukan ciki ba ko ?
Kinga bashi na kiraki nan ki min ba yanzu sai dai abinda nake son ki dashi shine ki kula da halin da take ciki yanzu da hankalin ki zaki far mata da duka.
Au ka dai yarda da dukan ta nayi niyar yi ke nan daga haka naja bakina nayi shiru yana gamawa na kwashe kayan zuwa kasa na barshi a gurin zaune.
Koda na koma dakina ban fito ba na zauna muna hira da laraba har sai da yara sukai barci na kaisu daki bayan na saka sunyi fitsari daki na koma don in shirya na samu waya na ruri.
Dauka nayi na duba shine a layin ban daga ba sai da na gama shirina tsab na fito naiwa laraba sai da safe nace ta rufe kofa tayi addua kuma ta kashe wutan dakin .
Ina shiga yana zaune a bakin gadon shi ya tasa laptop din shi gaba sai dai ba dakila yake yi ba har na aje jakkan hijab da zanin sallah na na kwanta bance dashi komai ba.
Jin sauka hannun shi nayi bayan ya hawo gadon ya kwanta ba kula shiba yai abinda zai yi ya tashi kamar yana taba dutse.
Shima bai min magana ba ya mike zuwa ban daki yana fitowa nima

92 / 144

Chapters