Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MIJIN Buzuwa Complete Complete Hausa Novel by Nil

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   108 / 144

321K to 324K   out of 431K words

na rama ace ba haka ba.
Sai daya dan kada kai ya murmusa yace ke na kun zama daya yanzu da ita don may ba zaki fita batun ta yadda Fati take fita batun ta ba idan tanayi.
Ban yi magana ba sai runtse idona danayi ina jin kuna a cikin zuciya na naji yana fadin ban son irin wanan fitinar kinji na fada maki gaskiya.
Ido na bude nace ita ma ka fada mata ta daina shiga harkata tunda ban shiga nata ba ni kin shiga kan tunda kin auri mijin ta yace.
Nace ba sai in bar mata mijin ba indai shine zaman lafiyan ku tunda na fito na ganta a wurin nasan tsiya take ji yau a gidan nan.
Yace tunda har kin fahinci hakan mai zai sa ki biye mata ku zama daya da ita kuna saida hali a gaban yara suna kallon ku.
Juyawa nayi na kyale shi naji ya fita daga dakin can ya dan jima da fita wayana yai kara ya Adam ne na dauka yana fada min gashi a kofan gida mu.
Nace to yaya barin fada mai kazo yanzu namike zuwa fada mai dakin shi na samay shi yana duba abu a cikin computer shi jin na shigo ya dab dago yana kallo na nace ya Adam ne yazo yana waje wai yace kice ya shigo mana ki bashi wuri kafin in fito.
Har waje na leka na samay shi zaune a motar shi muka gaisa na fada mai ya shigo tare muka shigo gidan dashi dama kafin in fita na fada masu bako zai shigo falon.
Nan anty fati ta mike kafin in dawo tare da yaran ta sai nafisa muka shigo muka sama zaune lokacin shima yana saukowa ke nan.
Tun bai karaso ba yake fadin bata fada maku akwai bako zai shigo bane batai mai magana ba kuma bata tashi daga inda take zaune ba.
Ya sauko yana fadin baki jini bane tace gani nayi itama ai bata shige ba ko yace you're very stupid Nafisa ina magana kina yi.
Yadda ya hasala yasa ta mike kitchen na koma na hado kayan taron bako na kawo mai tare da dan zama muka kara gaisawa daga nan na shige ciki.
Sai lokacin ya kalli ya Adam yace bissimillah mana ga ruwa nan kasha yayi godiya tare da balle marfin drinks din ya dan tsiyayya yace kai hakkuri fa kasan matsalan mata yadda yake haka muke fama dasu.
Yace a, a ba matsala ko mu masu daya ma wani lokaci ai sai hakkuri su haka Allah yai halin su da karamin tunane.
Tsuki yaja yana fadin wanan nasu yafi na kowa ba a haduwa wuri daya bai jidali ba kowa na jirace da dan uwan shi.
Allah ya sauwaka yace yana gyara zama tare da fadin ta fada min abinda ke nan sai dai da farko zanso inji alakan ku da wanan mutumin dan shiru yaya Adam yayi yana aje cup din da ya kurba drink's a cikin shi.
Can Yace a gaskiya zan iya kiran shi da uban gidana da kuma mijin yar uwata da tarasu shekarun baya auren mu bai dade da ita yar khadija din ba a lokacin.
Ta rasu ta barshi da yaran su guda biyar a tsakanin shi da ita sai daga bayane ya auri wata yar kasar su yanzun haka ita ke gidan zaune dashi da yaran.
Kuma zan iya cewa yanzu dai shine jigon da muke dashi duk da ba yar uwana a gidan yana taimaka min sosai ta fannin aikina don shine ma ya samo min wanan aikin Nepa da nakeyi yanzu.
AA yace madalla na fahinci abinda nake son ji daga gare ka sai dai banji dadin ta yadda ka biyo min ta hanyar ita deedar din ba gaskiya.
Yanzu ai mun zama daya koma may ye zaka iya tunkara na gaba da gaba kai min magana don ni ban faye son abi ta gurin iyalina ba kamar yadda kukai min.
Ba zan boye ma ba ita Deedar ta cancanci in mata alfarma ko wani iri tazo dashi don tsawon zama na da ita bata taba rokona wani abu a duniya na rayuwan ta ba.
Idan na bata ta gode idan kuma ban bata ba koda tana da bukatan wanan abin bazata taba min magana da tana son abin ba.
Ya Adam yace alhamdullahi naji dadi kwarai da ta samu wanan shedan daga gare ta don kusan sai ince haka halin su yake daga ita har yan uwan ta .
Wanan halin ne yasa kaga ban kyashin in mata in ma yan uwanta daidai gwargwadin halina yanzu kuma kaima gashi ka shedi khadija da wanan halin wanda na san tarbiyan da suka samu ne daga iyayyen su haka.
AA Yace to yanzu dai maganan shi AS kamar an gama ne sai dai zan so in zauna dashi muyi magana tsakani na dashi kan fili.
Sai kuma kai naka da nake son ka bar aikin nan in da halin bari in sama ma kwangila wanda zai tallafa maka ka gina kan ka dashi da iyalin ka don nima ina son in rama alherin da kukai min dakai da iyalin ka wanda ban manta dashi ba kuma ina afahari dashi yanzu.
Godiya ya Adam yai mai inda bai tashi ba sai da suka aje lokaci a tsakanin su akan ya samay shi idan ya koma Abuja.
Suka rabu da farinciki da jin dasin juna ya adam ya koma gida yana sheda ma Ya Amina yadda zaman nasu ya kasan ce a tsakanin su

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: A dadafe mukai kwana goma sha daya kwatsam da yamma ya shigo yana fadin gobe jirgin bakwai na safe zamu bi zuwa Abuja.
Da mamaki na kalle shi nace gobe goben nan kuma yaya yace eh halama zaman kd din ya maki dadi haka nace wallahi.
Da dai kun tafi kun barni nan har hutuna ya kare sai in samay ku daga baya don nan din mutum yafi sakewa ga yan uwa kuma kana gani.
Baki da hankali Deedar kina ganin zan wuce in barki garin nan ne komai karfin tafiyan goben ma donki zanyi shi ai don ina son muje asibiti idan mun koma.
Baga asibiti masu kyau anan din ba ku tafi kawai zanje ni da ya Amina na cikin magana mai kamar fada yace tunda Amina ke auren min ke.
Har ya fara tafiya ya juyo yace wai may kike tsunta a garin nan da baki son komawa Abuja naga idan na biye maki garin nan zaki dawo dani baki daya da zama.
Nace a yadda muke full house din nan yana min dadi ne don ba wani zaman part ga mutum yana yadda yaso a cikin gida.
Yace can din wa yahana maki yin hakan nace kaima kasan inda matsala take ai don yanzu muna komawa angayan buzaye ka zasu cika muna gida ne.
Wani kallo yai min baiyi magana ba ya juya ya fita dakatar dashi nayi cikin dan gudu ina fadin yaya sai ya juyo nace don Allah zan shiga wurin ya Amina da cikin gida in masu sallama kada in girshe su kuma.
Ya kalli agogon hannun shi tare da fadin a wanan lokacin zaki fita nace please yace shirya in sauke ki idan kin gama ki kirani in dauko ki kuma.
Nidai na juya da sauri hijjab kawai na zura a kaina na jawo kofan dakina na rufe a falo na samu Nafisa zaune da wanan yar uwar tashi suna kus kus fitowa suka zuba min ido.
Ban tanka su ba na fice ina jin Nafisa na jan tsuki a waje Affan ya tare ni yana fadin anty zan biki nace gidan hajiya zan tafi affan yace eh zanje.
Na kama hannun shi muka nufi wurin mota shi ya dakatar damu da fadin ina kuma zaki dashi haka nace cewa yayi zai bini.
Common shige ciki ya dakawa yaron tsawa ya juya da sauri motar na bude na shiga ya tayar na dan kalle shi nace yaro ne fa kana masu haka basu jin dadin ka ai.
Yace kin sagarta yaran nan idan kin koma zasuji daban nace ba sai in koma dasu ba ko muje da maman su gaba dayan mu.
Da sauri ya juyo yana fuskantana tare da fadin ina nace can Abujan mana ko itama ba gidan mijin ta bane can.
Yace ke baki san komai ba da data dawo nan waya koro ta can ta zauna nan tunda haka taga yafi mata nace ai ba tanata za a bi ba yaran yakamata ka dubawa makomar su.
Yaro fa sai da tarbiyan uba a kusa sai dai idan ya rasa su ne ya dauki maraici hakana.
Kofan gidan ya Amina ya tsayar da mota yace idan kin fito ki kirani nace to na fita ya wuce.
Ina shiga yaran ta suka tare ni da murnan su mun gaisa na shiga dasu ciki tace daga ina haka da yamman nan da cikin ki tsoho nace daga gida zuwa gidan yar uwata mana.
Baki san ba a son mai ciki tana fitar yamma haka ba nace daurowa fitan nawa yayi nazo maki sallama ne na fadi ina zama.
Yaushe zaku koma nace wai fa yanzu yazo yana fadin gobe goben nan da bakwai na safe in Allah ya kaimu.
Shiko may yasa yake hakane nace haka yasaba dashi yanzu shirin da zan maki ina zan samu yinsa da yamma haka nace nidai idan na samu yaji ya wadatar dani kibar ssuran shirin ai ba zamu dade ba zamu dawo bukin zainab don kafin sallah babbane akace bukin.
Wayana yai kara na dauka maryam ne akan layin take fadin wai yaushe zaku dawo ne kin barni nan abubuwa na son cabe min nace kaji ki da wani zance kamar may shirin aure.
Tace don Allah yaushe zaku dawo wallahi ina bukatan ki khadija sosai nace ke gidan mijina fa nake dariya tayi sosai tace ana muna kuri da auren nan muma dai mun kusa bin layin ku ai muhuta gorin auren nan hakana.
Kiyi yau idan kinyi fushi mana tace banyi yau amma zan baki mamaki don sai kin sha mamaki na.
Dariya ta bani nace gobe idan Allah ya kaimu muna nan tafe korafi ya kare ni kina ban mamaki mace da mijin ta kuma a dinga damuwan ta wai ta dawo .
Ko kun hada baki ne da buzuwa wai tace shegiyar tana ina ne wai nace kd mana muna nan tare da ita.
What naji tace wai mijin nan naku wani irin sokon mijine shi maryam mijin nawa ne soko na katse ta tace hannu a kunne na madam kada a yankani .
Yau kuma AA ake shigar ma fada nace ya son ranki yar mata tace daina rage min aji kice KARAMAR BAZAWARA.
Dariya mukayi sosai da ita tace sai dai kinzo don akwai labari gaskiya nace kamar yau ne insha Allahu tara ina dakina da yardan Allah.
Mun gama waya da ita ya Amina ta kalle ni tace aure zatayi ne nace bar ta da shimay ta ba aure zatayi ba so take dai in koma mu shiririce can da ita.
Ina gidan ya Amina anan nayi sallah sai baya magariba na bar gidan nida ya Amina muka shiga cikin gida.
Mun gaida Anty amarya dake farko shigowa sai umma da ke kusa da part din Abba su hajiya mama da mommy sune daga ciki part din su yana kallon juna.
Wurin mommy muka shiga nan take jun zancen tafiyan mu tace waishi babangida wani irin bahagon mutum ne haka bai fadin abu sai a kuraren lokaci.
Ya Amina tace shi nake fada mata yanzu ai wai yaji take so ni kuma ban riga da na aika ba ai mata mai hadin nan.
Mommu tace in don yaji ne akwashi nan gurin a koba na sadiyan shehu ba tace shi take so wai taci shi ranan tace dandanon yai mata.
Mikewa nayi nace barin gaida mama tace yakamata kada taji kin shigo tun dazun baki lekata ba kuma.
Tana zaune tana lazumi na shiga dakin ganin tana lazimi na shige wurin su Binta a kwace na samu zainab gaisawa mukayi dasu Binta tace daga ina haka da daren nan nace gida nazo sallaman ku ne.
What don Allah har zaku koma ke nan nace wallahi haka yace dazun da yamman nan sai lokacin zainab tace yanzu nima yaya ya ke fada min amma yace ku jirgi zaku bi ai nace eh tafiya safe zamuyi shine nazo sallama don goben nasan a gurguje zamu shigo.
Zainab yakama ta fa ki koyi sakewa da mutane hakan wanan shirun baiyi maki a wanan zamanin don ni naga ranan bakina nace na juya ina kallon ta.
Murmushi tayi tace kaji ki da wani zance haka halina fa yake Binta tace tana sin komawa anty fati ne kila nace Allah rabaki da halin anty Fati .
Mutum bai iya maida hatsi sufe kullun jiya ayau ita kodan kiza kizan na fa batayi na mata hajiya mama ce ta bude labulen dakin take fadin.
Khadija kece da daren nan nace eh mama nazo in sallamaku ne yace gobe zamu koma wai tace ikon Allah gobe goben nan kuma nace haka yace mama kuma tafiyan safe zamuyi .
Nace aiko kuna nan har bukin zainab tunda ba nisa nace nima naso haka mama tunda muna hutu ne yanzu amma yace a, a.
Daga inda zainab take tace hajiyan ki tuna mata zancen set din kada ki manta Binta tace mara kunya zancen kayan ma ke ce mai tuni ashe ba a ko bari mu, mu tuna.
Nace kunyawa zata ji kan abinda take so kuma kece dai mara kunya ai da kika sa baki a zancen manya dariya ta kwashe dashi lokacin da taga na dafe baki tace ai kin gama.
Kunyar may zakiji dama in ina fadin kina da baki sai tace wai kazafi nake maki yanzu ai gaki kin gani hajiya da idon ki.
Murnushi hajiya tayi tana fita tace in kin gama ina falo nace to hajiya tana fita na mike Binta tace ina kuma zaki nace wurin hajiya mana ko so kike in zama mai zunubi kuma na fice.
Zama nayi kasa daga gefen ta na fara gaida ita bayan gama gausuwan mu ne tace dama akan kayan zainab ne wanda aka saya tace bata son irin sa .
Nace ta fadawa dan uwan ta wai ita kunya take ji nikuma magana irin haka baya hadamu dashi don zaiga kamar umurni ne nake bashi akan dole.
Shiyasa nake son kuyi magana dashi udan da hali sai ya kara mata wani su zama biyu dana alhaji din dayai mata.
Zanyi magana wayana yai kara na dauka shine a layin yace kina ina baya na dauka nace gani wurin hajiya yace ok ya kashe waya.
Nace mama ina ganin in anyi mai magana ai ba zai ki ba zai canza mata din tunda dai bata son wancan din da akai mata hajiya tace matsalan ai Abban ku yabawa kudin komai a hannun sa.
Sallaman dayayine ya katse mu ya shigo dakin yadda ya samay mu a zaune ya fahinci wani magana muke yace karana takawo ko ?
Yana zama yake fadin haka hajiyatace kai mata wani abin ke nan ko tana kallona nace shawara muke na uwa da yar ta kawai ka tsargu.
Yace ashe nazo daidai sai ai shawaran dani ke nan tunda nazo murmushi hajiya tayi irin na manya da yake baiyana jin dadi a gare su.
Dama kazo a daidai magana muke kan zancen kayan zainab sai gaka yace ina mun gama maganan da Abba ko na bada duk wani abinda za a bukata ta bagaren shi.
Ka gama hajiya tace sai dai ita zainab din take korafin kayan yanzu yace hajiya mu yarinyar nan ta samu wuri korafi kuma kan kayan da Abba yasai mata ko may ?
Nace yaya ba haka ake nufi ba ana magana ne kan abinda ake yayi kasan shi Abba din bawai yasan kan kayan bane yace ke kikasan kan su ke nan ko ?
Ya fadi yana harara na hajiya tace kada kaga laifin yar mutane itama yanzu ta san da zancen kasan hajiya umma zai sata zabo ita kuma kasan sai ta samu riban sai ta zabo mata mai karamin kudi.
Yace kai umma tana nan da halin nan hajiya tace may za a fasa kadai san halin bakina suke son ji kawai akan zancen har alhajin.
Tunda ina yar tane baiba kowa ita yake ba dai tawo masu abinda ransu ke so mu kima kaga namu iya bi.
Yanzun ya kuke son ayi tunda an riga da ansaye din tace shine ka samu muna magana anan yazon shawaran da muke ke nan ai.
Nace ni sai naga a bar wancan din a matsayin na Alhaji sai ka saya mata wani mai kyau a matsayin naka ko na hajiya din.
Hajiya tace a dai barshi a matsayin nasa din zaifi yace idan mun koma sai taje ta duba mata komai acan a bata list din duk wani abinda za a bukata daga can din yana magana yana sa hannu aljihun shi hakan yasa nace mun

108 / 144

Chapters