MIJIN BUZUWA complete Hausa Novels.txt

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   47 / 144

138K to 141K   out of 431K words

san kadan ne daga cikin sherin Nafisa ko ba yarinya a tsakanin su haka take masu idan zai kwana a dakin Fati din tace bata da lafiya karshe a dakin ta zai kwana.
Do haka ta juya abinta taje ta kwanta bata kara ganin shi ba har rana breakfast din da ta hada mai baci ba wani aka kawo masu daga gidan Auta amiyar Nafisa din.
Haka fati tayi ta hadiyan bakin ciki da wanan zuwan nasu ita da ganin miji sai dare idan zai kwanta zai lalabo ya dawo dakin ya kwanta da safe ya fice kuma ranan nafisa tace itace zatai girki .
Dole Fati ta kyaleta tayi yadda ranta ke so tunda har mijin ma ya biye mata ita yanzu burin ta shine ta zauna a cikin yaranta kawai su girma a tare da ita.
Nafisa bata shiga gaida sarakkanta ba balle suga yar jikan tasu data haifa da dan su sau daya ta shiga gaidasu ana gobe zata koma bata ba kowa yar ta ba suma basu taya zasu dauka ba.
Sai kuma abin ya bata mata rai don yadda ta shirya bata samu yi ba sai taji haushin basar da ita da sukayi takoma fadin wai yanzu har kiyayyan da suke mata ya shafi yar ta jikan su.
Haka ya sa AA yaji haushin abinda sukai mata a ranshi har ya kira mommy yana fada mata abinda sukaiwa Nafisa da yar shi baiji dadin hakan ba.
Don ba halin ya kira mahaifiyar shi ya fada mata yasan kwanan wasa yanzu za a jisu da ita idan ta fara mai fada yasa shi kiran mommy.
Mommy tace dashi babangida kasan halin matar ka fa ta make yarta a jikin ta bata ba kowa ba mune zamu karba tai muna wullakanci amma munyi kuskure gaba zamu gyara insha Allahu.
Bayan kwana hudu suka nada suka koma abuja tun da suka kama hanya ta washe ranta da ya rasa gane mata da suke a kadunan.
Yanzu ko kamar ba ita ba sai hira take jan shi a motar tana faman dariya tana kuma wasa da yar dake zaune a cinyar baban ta din.
Tunda ya dawo ta samu kansa da kyau sai dai abinda bata sani ba yanzu asiri bai faye tasiri ya dauki lokaci a jikin shi don maganin tsarin da malam na zaria ya bashi.
Kuma abokin shi Yusuf bai zauna ba akan shi yana tsaye da alamarin shi haka ma mahaifan shi suna tsaye da mashi addua sosai yanzu.

Yau tunda na dawo daga islamiya nake kwance ba wai don banda lafiya ba sai dai ina jin jikina ba dadi ne ko aikin gida da nake taya mama ban iya tayata yi ba.
Barci nayi sosai a ranan can zuwa rana yaro ya shigo yana fadin ana sallama dani a waje mama ta shigo ta tadani tana fadin min wai ina da bako a waje.
Mikewa nayi da kyar don barcin dake idona na ban tsaya gyara fuskana ba na fita daga gidan haka na mamud ne zaune a motar shi da yaran shi biyu.
Na iso inda suke ina gaida shi bayan motan na bude inda yaran suke zauna kafa na suna waje ina gaidasu tare da tambaya su yaya makaranta.
Kafin yaran su bani amsa ya jefo min tambaya yaya naga fuskan ki haka kuma ko baki da lafiya ne ya tambaya ?
Nace daga barci na tashi yanzu ba tare dana kalle shi ba hannu na mika wa yar karamar yarinya dake saye a cikin uniform din shekk lemo sai yarinyar ta noke taki zuwa.
Tambayar ta nayi yaya sunan ta yace sadika dayan kuma nasir ina taba kafar yarinyar nace zakici biscut ta daga min kai nace to sai kinzo wurina sai ta kara makewa.
Ina zuwa nace dashi cikina koma na hado masu kayan kwalama na yara wanda na dawo dashi muna ci da kanne na nafito rike da leda a hannuna namikawa yaran.
Da sauri suka karba nan dai muka taba dan hira yace zai maida yaran gida daga islamiya ya dauko su mukai sallama ya tafi.
Bayan sun isa ma sai da ya kirani muka taba hira ya kashe wayan tare da fadin zai zo amsa gudane wurina nace na hutar dakai kada ka wahal da kan ka.
Yace to zamuyi waya nace sai najika aiki gida na taya mama ta koma folo tana kallo sai dana gama zuwa dare na shiga daki na samu wayan mamud har six miscall ya kira ban dauka ba.
Kiran layin shi nayi aka dauka ban tsaya sauraren ba nace ina waje ne ina aiki banga kiran ka ba.
Ban karasa magana na ba naji muryan mace tana fadin ke wacece da zaki kira lamban mijina kin san ko waye mamud kuwa ?
To bari kiji daga yau kada ki sake shiga harkan mijina in ba haka ba zan sa ayi maganin ki a garin nan shiru nayi ina sauraren ta sai da ta gama nace.
Ke kuma wacecd a guri mamud din bari ki ji ki sani ba don ki ke kadai akayi shi ba daga yau ki gyara kalamin ki inzaki magana akan shi ki dinga cewa mijin mu.
Ina fadin haka ban tsaya jin haukanta ba na kashe wayan ina dariya nace banza mahaukaciya ni mijin ki bai a gaba na yanzu da kin ga tsiya wallahi.
Bai kirani ba nima ban kirashi ba sai bayan kwana biyu sai gashi ya aiko kirana wai ace mamud ne mace ace ban samun fitowa aiki nake yi.
Mamace ta samin baki dole na fita naci karo da dan aiken ya dawo wai yace don Allah inyi hakkuri minti biyu kawai zanyi.
Tare muka koma da dan sakon na samay shi zaune a cikin motar shi yana duban wayan shi karasowa na ya fito yana washe baki.
Fuska na a daure na gaida shi magana yake na kyale shi sai ko umm ko ummumm nake bashi amsa dashi kaina a kasa ina dakilan wayana.
Muryan shi naji yana fadin yau gimbiya may ya faru ne naga an fito min haka a daure nace wani abu ka gani halan ?
Yadan motsa kafan shi kadan yana murmushi tare da harde hannayen shi guri daya yace ko gimbiyar tawa mulki take jine haka ?
Sai da nayi mashi wani irin kallo shekeke nace mulki ai mulki yana gidan ka don ko wayan ka sai an baka izinin dauka kake dauka ko zuwa gurina yanzu waya sani ko santan hanya kayi kada matan ka su gani.
A cikin rashin kuzariya dago kai yana kallona yace wanan wani irin magana ne haka khadija kikeyi kai tsaye ba tare da tunane ba.
Nace irin wamda matar ka tayi min jiya daga kiran wayan ka ta dauka tana zagina a wayan ta daukar min waya fa kikace nace ka duba nan ga kirana a wayana kana gani katuna ina kaje jiya a daidai wanan lokacin ?
Look mamud na fada ma soyayya dakai a yanzu akwai matsala ka nace akan sai munyi gashi tin ba a je ko ina ba an fara kirana ana zagina daga gidan ka har da yimin iyaka dakai.
Ya kai duban shi gare ni tare da sake dan murmushi yace mai shi tayi nasara gare ki ke nan tunda gashi har kin karaya zaki bar mata ni.
Haka muka kasance dashi muna musayan maganan karshe dai yaban hakkuri nace ya wuce amma ya daina zuwa wurina.
Yace ba da sanin shi ba amaryan shi ce ta dauka daya shiga wanka kuma da ya fito bata nuna mashi akwai wani matsala ba.
Nace wanan kai ta shafa ni dai na gama magana kuma.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Kawar da kaina nayi gefe kamar ban ganshi ba ko ban san shi ba karfin gudun ya rage ya dinga sarsarfa zuwa wurina yayin da ni kuma nake sauri in shige get din gidan Ya Amina din.
Ke ji mana yace bai juyo ba sai saurin da nakeyi na kara harda dan gudu nashige ciki tsayawa yayi ya rike west din shi da hannun shi biyu yana dan murmushi.
Yadda na shigo gidan kamar wacce aka koro yasa Ya Amina fadin ke lafiyan ki kuwa nace ina waigen kofan shigowa lafiya sauri nake na bar wayana daki.
Ajiyan zuciya ta sauke ta kalli kofan sai ta juyo ta kalli inda na shiga ta tabe baki na dade a ciki zaune kafin in fito danaji shiru.
Wanan kaaton da soja yaje daya fi mai yya more karfin shi a can nace ina dagawa wanka nayi na fito na shirya na fito falo.
Na samu yaAmina bata falon sai gata ta fito daga uwar dakin ta tana fadin zan dan shiga gidan su mommy akwai aikin da zamuyi da safe nan kin san ance ka rama alheri ga mai maka.
Dana haifi Na,ima mutanen nan baki ga irin alheri da sukai min ba wallahi banda abin basu in ba ta haka zan maryar masu da alherin su ba gare ni.
Adawo lafiya nace mata ina lafewa saman kujera tare da danna wayana ta juyo tana fadin idan ban fito da wuri ba sai ki dora girkin abinda zamuci da rana kada bakuwan ki tazo ta samu ba abinci.
A kwai komai a kitchen da zaki buka wanda babu ki buga min waya ko ki fita ki samu nan bakin layi sai kin dawo nace da ita tafice daga gidan.
Ban dade ba barci mai nauyi ya dauke ni a guri firgigit na tashi daga zaune don mafalkin hajiya mama da nayi ta sani gaba tana min murmushi.
Firgigita na falka daidai lokacin da ta mika hannu zata share min hawayen dake bin fuska na ina mamakin wanan mafalkin da nake yi tsakanin jiya da yau.
Na dade zaune a gurin kafin in mike in shiga kitchen ban ankara ba ashe har shadayan rana ya gwauta ban sani ba a gurguje na dora muna girki ina yi ina duban time.
Wayana naji yana ruri daga falon inda nasa chagi da sauri na nufi gurin maryam ne a layin na dauka ba ko sallama naji tana fadin wani unguwa zan ce a kawo ni nace GRA na fada mata sunan layin mu.
Isowan ta yayi daidai da gama girki na na fito na tare ta a waje muka rungumay juna muna dariya tare da shigewa ciki sai bin gidan takeyi da kallo.
Falo muka shiga na karbi jakkanta nakai dakina da na gyara na dawo falin ina dariya tambaya na tayi ina ya Amina nace humm kin san sune kan buki tun safe ta shiga wai aiki a family house din su AA.
Nikan na matsu in san wanan uwar gidan nashi abin tausayi na kallo ta nace may abin tausayi a ciki an fada maki tana cikin wani hali ne ?
Khadija labarin dasu Binta suka bamu nata ne ai matar abin tausayi ne wallahi malama kice dama gulma ya kawo ki ba taya zainab murna ba.
Sannan ita fa Fatin nan halin tane haka shiyasa mutane suke mata kallon abin tausayi tana da sanyi hali da rashin nuna kulawa ga abu shiyasa mutane ke fadi haka.
Amma ni ina ganin lafiya kalau take da mijin ta yanzu don ban kara jin wani maganan haushi ya faru ba koda yake idan ma ya faru ni ina zan sani.
Mikewa nayi na shiga kitchen na fito mata da abinda zata ci mun dade muna hira har bayan azahar muka mike zuwa sallah.
Ina idarwa wayana na karan kira ya shigo min na dauka da sauri Zainab ce a layin gaisawa mukayi take fadin khady har yanzu baki shigo ba mana bamu shirya komai ba fa ke ake jira.
Nace gani nan da maryam ta iso dazun tana hutawa ne amma mai zai sa sai nazo kuyi duk abinda kuka ga ya dace mana zainab.
Look indan ba zaki zo ba ni ganin nan zuwa dayani in gaida maryam da zuwa don binta sun fita sai kin zo din nace Allah ya gani yanzu kunyan shiga gidan su nakeyi.
Ba a dauki lokaci mai tsawo ba sai gasu tare da Binta sun shigo da murna suna taron maryam din nace ga gandoki muje buki ta iso daga ina fata mata kawai tace gata nan zuwa ai.
Wayan zainab ne yayi kara ta dauka da murmushi tana mikewa wurin da muke din Binta tace ango yayi kira ke nan dariya nayi nace au shine ake gudun muji yadda ake soyewan ta dan waigo tana fadin wallahi yayana ne ai ba wani soyewan da muke yi ke dai.
Munafuncin banza sai ki fada masu su da basu sani ba nikan nasan komai ai yanzun tana dauka yake tambayan ta tana inane haka waya ke ta ringing bata dauka ba?
Tace nazo wurin kawar mune Khadija da tazo nan makwabtan mu ba nisa damu murmushi yayi yace khadijan na kusa ne ki bata waya tace eh sai gata tazo tana miko min wayan.
Yayana ashe kwanan nan zakayi wuf da kawata gaskiya munyi murna sosai Allah ya sa albarka ga alamarin.
Ameen khadija Allah yasa ayi namu da naku a lokaci daya ya fadi da sauri nace dani dawa kuma ai ni ban ko tsayar da miji ba balle aje ga zancen aure .
A yadda muke magana dashi yasa dukan su zuba min ido a cikin tuhuma sai kuma ga maryam tace kice ina gaida shi ina taya shi murna.
Ga mayam tana tayaka murnan samun zukekiya kamar zainab na fada cikin zolaya yace haba yaushe tazo nace yau din nan ina fada mata jiya tace da ita za, ayi komai shine ta taso yau aba maryam din waya yace.
A lokacin da nake mika wa maryam waya binta tace wai tsaya nifa ban gane ba ?
Dama kun san shi ne ko may maryam ta karbi wayan tana fadin yaya Yusuf ashe wani abin arziki ya samu kuma munyi murana sosai wallahi.
Yace ya gode ta mika wa zainab wayan ta zainab din ta juya tana make murya muka sa mata dariya wai tsaya don Allah dama kun san yaya Yusuf ne khadija ?
Mun san shi mana farin sani kuwa kallon da tati min ne yasa na gyara zancen da fadin ai a sanadin ku ne muka san shi kin manta ne.
Zainab ne ta juyo tana fadin wai yana waje yana jiran mu mu fito gaskiya something is fishing here don ina mamaki har da gidan ku yaya Yusuf wai ya sani.
A yadda nasan yaya Yusuf bamai yawan magana ba ne da zai san ku haka farat daya dariyan da maryam keyi ne yasa ta mayar da hankalin ta gare ta.
Mikewa mukayi zuwa wajen inda yace yake a waje bakin get muka samay shi ya fito daga motar shi gaidashi muka fara yi muna tayashi murna.
Yace in Allah ya yarda khadija na fada maki da naku za ayi bukin mu nace don Allah yayana kabar zancen nan wai dawa zaka hada nine halan.
Koma da waye kin fi kowa sani don yanzu lokaci yayi da kowa zai sani na gaji da wanan wasan boyar naku maryam tace ashe ka gane su yaya ?
Maganan mu ya daure ma su Binta kai nace cikin daure fuska don Allah yayana abar zancen nan anan kada kasa in koma yau Abuja.
Yace an gama ama watarana ai dole kowa zai sani nace wai asan may da kake ta fadin haka yace ai na bar zancen tunda baki son matana ta sani ko ?
May kuka shirya zakuyi ne goben nayi saurin cewa ba wani bidia zamuyi mai yawa ba kawai dan get together zamu da kawayen mu su ma su sheda.
A ina zakuyi ke nan binta tayi tsagal tace yaya a kama muna holl a gamji kawai muje can mu cashe da sauri nace a, a wallahi nan dai kusa zamu samu wani gida muyi event din mu wanan ai kya jira har aure yazo.
Zainab tace ga gidan yayan mu nan ai ya ishe mu muyi komai don ko falon gidan kunga babba ne sai dai in ba zai bari ba kun san shi da rashin son hayaniya.
Cabdi akan may zai hanamu shi da matar shi tayi buki na banza ma a ranan fa Yusuf yace to shike nan kunji madam ta gama maga dole ko zai yarda da hakan.
Balle ma ai bazai hanaku yi ba a gidan sai ka fada mai da kanka Binta tace yace kedai ki bar zancen tunda kin ji khadija tayi magana ai an gama.
Yayi muna sallama yace zai tafi idan munyi list din abinda muke so sai mu turo mai amma ga wanan ya ciro kudi a motar shi yana miko min wai mu fara amfani dashi.
Kai na kada nace a a yayana kudin nan sunyi yawa wallahi bafa wani abu mai yawa zamuyi ba a wurin just friends din mune zamu hada su tayamu murna.
Binta tayi saurin mika hannu tana karban kudin wai din may zance sunyi yawa inda wani ma a karo.
Murmushi yayi yana

47 / 144

Chapters