MIJIN BUZUWA complete Hausa Novels.txt

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   89 / 144

264K to 267K   out of 431K words

alheri idan mun dawo sai ki saya ma mutanen Niger nasu driver yakai masu can.
Shiru nayi nama kasa magana a lokacin sai can nace angode ubangiji ya kara ma arziki albarka yace amin mikewa nayi na fice daga dakin zuwa part dina.
Yinin ranan busy nake sai yamma na dawo a gajiye ga jikina banjin dadin shi amma haka na daure naiyi ta zirga zirgan tafiyan da zamu gobe.
Washegari na shirya tsab shi kawai nake jira sai da ya leka office din su ya dawo muka dauki hanyar kaduna wanda kafin mu tafi din sai da suka kwasa da nafisa a gidan.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Kamar kullun yau ma shigan dare mukayi garin inda kai tsaye gidan shi muka nufa da kyat naga mun kawo kaduna din don wani irin amai dake taso min a motar yayi magana na nuna mai kaina ke ciwo kawai.
Motar na tsayawa na fitaa da sauri na rigashi shiga gidan don jirin da nake ji a lokacin banyi tsammanin anty Fati tasan da zuwan mu ba
don yadda muka samay ta ba a cikin shiri ba.
Ganin mu yasa ta fara dan kamay kamay tana fadin ashe kuna hanya tafe ne yau nace eh ina zama saman kujera.
Dafe da hannu na akaina karshe ma kwantawa nayi don jirin ya sake ni shigowwaan shi gidan idon shi ya sauka a kaina.
Dashi da Yusuf suka shigo wanda ya wataa biyu bai abuja a lokacin yana waje wurin wani business da AA din ya tura shi yai masu.
Lafiya may ke faruwa yake tambayana cikin kura ma inda nake ido har suka kara so gare ni Fati tana mashi sannu da zuwa ya amsa mata sama sama.
Har ya iso inda nake kwance ya dan duka yana taba jikina tare da fadin may ke damun ki ne kuma ?
Yusuf ya tambaya dama banda lafiya ne da muka fito gida yace lafiya take sai dai ina ganin tun a motar ne bata jin dadi zuwa yanzu.
Yaran ne suka fito daga dakunan su ganin mu yasa su jin dadi sukazo wurin uwar su suka tsaya suna kallona suma.
Har lokacin ban iya daga kaina ba ina a yadda nake kwance ko muje asibiti ne Yusuf ya fada sai lokacin da naji ya ambaci asibiti na dago kaina da idanuna da suka kada sukai ja nace jiri nake gani kawai amma lafiya ta kalau.
Ok zai sake wani lokaci haka yakewa mutum ai idan ya kwana biyu baiyi tafiya ba ya hada min da fadin sannu na gyada mai kai.
Daga inda Fati take zaune ta jefo min sannu na amsa mata tare da karfin halin fadin Affan kuna lafiya ina mika masu hannu su zo gareni.
Affan kawai yazo shi karamin yaki zuwa inda nake din na rike hannun Affan din ina gaida shi sai yayi saurin fadin sannu anty ya jiki.
Murmushi nayi nace da sauki Affan kunyi hutu ne yaron ya gyada min kai tare da fadin eh munyi hutu last week.
Zama AA din yayi saman kujera ina jin ta kara gaida shi ya amsa gaisuwan nata ya kara maida haankalin shi a inda nake kwancen yace.
Ko ruwa baki samu kisha ba don gidan ba,a iya ba boko ruwa ba ki daure ki shiga ciki kidan watsa ruwa ko jikin naki zai sake maki.
Namike batare da bata lokaci ba na nufi hanyar hawa saman ida dakunan kwanan gidan suke tare da ciro key a cikin hand bag dina na bude dakina na shiga.
Dakin yana nan kamar yadda yake sai kura da yayi saboda rashin mutum a cikin sa na kwana biyu da ba a zauna ba na bi dakin da kallo na rasa ta ina zan fara da dakin.
Zanin dake saman gadon a shimfide ya yaye na jefa ga abin zuba wanki dake gefe daya aje a dakin na nufi ban dakin akwai ruwa kamar ko yaushe duk da yanayina sai dana wanke bandakin don in akwai abinda na tsana shine rashin gyara bandaki.
Na fito na dauki tsitsiyar dakin na share jakkana ba bude na fito da sabon zanin gado a ciki na shimfida na feshe dakin da room fresh ya dauki kamshi a lokaciya daya.
Ban daki na shiga a can na tube kayan jikina wanka nayi tare da dauro alwala na fito na tada sallah ina gamawa na haye gado na kwanta duk da yunwar da nake ji a lokacin.
Barci ne ke son dauka na naji an shigo dakin tun daga kofa ya fara magana yana fadin har kin kwanta ne ko ?
Kin ci wani abune da kika kwanta haka na da yunwa ?
Ko baki jin yunwa ne yanzu da kika kwanta hakana ?
Ya karaso bakin gadon tare da zama yana dan taba min jiki nace ai ba zazzabi nake yi ba gajiya ce dai kawai ya kama ni kamar yadda yayana Yusuf yace.
Har wani tafiya zakima gajiya haka kamar wace taje Egypt da kafan ta akawai dai wani abinda ke damun ki may be ulcer din kine ke son tashi maki kuma.
It may be don yanzu danayi some a hours banci abinci a kan lokaci ba haka yake min naji yace kai wanan ulcer da tonon asiri yake bai tashi kamaki ba sai yanzu da kike gida.
Ya sake kai hannun shi saman wuya na cikin dan shagaba nace dashi haba ya AA don Allah ka bari barci nake son yi fa yace ba zakiyi barci ba sai kin samu a binda kika sa a cikin ki tukun na.
Bari Yusuf ya dawo yanzun nan ya fita ya samo muna abinda mukaci nace laifin ka ne ai dabaka bugawa Anty Fati waya kana tafe ba yau da ta maka tanadin abinda zamuci.
Tsuki naji ya buga tare da dagawa daga rankwafen da yake a kaina yace wai ma ko kin sha ruwa da muka iso nace banjin kishin ruwa ai dana sha ko.
Fita yayi daga dakin sai gashi ya dawo dauke da goran ruwa da cup a hannun shi ya zauna a bakin gadon tare da fadin oya tashi kisha ruwa ko da kadan ne.
Cikin yanayin jin jiki nace har yanzu fa jiri nake dan ji ban son in daga sosai wallahi yai kamar ya tallaboni na mike da sauri tare da fadin kana son mushiga hakkin da ba namu ba ke nan.
May ye kuma na cin wani hakki anan din na karbi goran ruwan ba tare da nayi mashi magana ba na tsiya na shanye na mika mai cup din.
Ina kawai kwance kallo ya bini dashi har na kwanta ya ja tsuki tare da fadin kai dana san wanan tafiyan haka zai zama maki ai da banzo dake ba wallahi.
Zanyi magana wayan shi yai kara ya duba tare da mikewa tsaye ya bar dakin bai dade ba sai gashi ya dawo dauke da leda a hannun shi.
Take away ne na karba tare da godiya ya tsureni da ido yana fadin tashi mana kici sai ki kwanta dole na tashi na sauko a kan gadon bandaki na shiga na kurkure bakina na wanko hannu na fito na samay shi a zaune.
Sai da yaga na zauna kasa ina bude ledan ya tashi ya fita daga cikin dakin tare da fadin kici sosai fa don Allah sai da safe nace yace ba yanzu ba ai.
Kilama anan zan kwana tare da ke da sauri nace rufa min asiri don Allah mu rabu lafiya da anty Fati yadda nazo yace ita bata san ciwo bane halan ?
Yana fita na mike nayi ma kofar key na dawo na zauna ban iya cin abincin ba don dandanon shi bai min ba na ture gefe drinks din na dan sha namike na kurkure baki na kashe wutan dakin na kwanta bayan nasha magani na .
WASHEGARI
Wasai na tashi banji komai ba bayan nayi sallah na koma na kwanta har inji motsin mutanen gidan in fito mu gaisa dasu.
Anan kuma barci ya kara dauka na gurin bani na tashi ba sai goma da wani abu mamakin barcin da nayi haka naji na mike na shiga wanka na fito har na shafa mai ina shiryawa naji ana kwankwasa min kofa.
Na tuna tun jiya kofan yana rufe na bude Laraba mai aikin gidan nagani tsaye a kofan tana dauke da kayan abinci a hannun ta kula guda biyu.
Murmushi na sakar mata tare da kai hannu in karbi kulan tace haba hajiya aiki na ke nan ai gidan nan ta shiga dashi ciki ta aje tare da fadin yaya karfin jikin jiya kun iso ance baki da lafiya.
Nace nace naji sauki mama na gode ta juya zata fice daga dakin nace mama don Allah fita da wanan kayan abawa mai ci shi a waje.
Ta duka tana daukan kayan ta dan bude tace a, a hajiya ai ba sai ankai waje ba ma ni nan ina da bukatan shi yaushe rabon da inci nama haka a gidan nan sai idan Alhajin gidan nan yana gari koshi baifi inci tsoka biyu ba don matar gidan kan raba idan na gama.
Murmushi nayi nace ayyah dauka to kije dashi amma sai kin dumama shi don yayi sanyi tace bama zan tsaya dumamawa ba wani ya ganni dashi.
Ta fice ta barni da mamaki a raina tare da tambayan kaina amsan da ba mai bani shi a lokacin na gama shiri na bude kulan abincin data aje min doya nagani busashe sai dan kwai a ciki da baida yawa.
Dayan kulan kuma jeloup din taliya ne ne kai na girgiza don ban iya cin ko daya daga cikin su dama akwai kayan tea ne sai insha tea din in tashi.
Bakin gado na koma na zauna na tasa kayan a gaba ina tunane kala kala a raina naji an turo kofan dakin AA ne ya shigo dakin.
Da alama ba daga barci ya tashi ba ya nufo inda nake zaune kafin ya karaso nace ina kwana bai amsa ba sai da ya karaso inda nake.
Kin tashi lafiya yace yana taba fuskana tare da fadin ya jikin naki da sauki nace ina dago kaina gare shi.
Hajiyan mu tana gaida ke da jikin da sauri na dago ina fadin ka fada mata ne kai ko yace eh nace tare muka zo amma tunda muka iso baki jin dadin jikin ki ne kina kwance.
Nakan naji sauki nace dashi yanzun ma nake son shiga can in gaida su daga nan in wuce gidan ya Amina itama in gaishe ta.
Har kinji saukin yawo haka ne nace naji ai dama ba ciwo nakeyi ba gajiya ce kawai ta kamani dama.
Idan kin shirya sai ki magana a kaiki yace kin ma karya kuwa yana kallon kaya abincin kai na girgiza mai tare da fadin banjin cin wanan da akayi sai idan naje gurin mama zanci.
Tsuki yaja tare da nufar kulan yana budewa sai ya daga ya kara jan tsuki bai iya magana ba ya fice daga daki bin shi nayi da kallo har yafita na sauke ajiyan zuciya na mike na dan kara gyara jikina na dauki hand bag dina na fita.
Ina sauka faln na samu ya fito daga dakin Anty Fati rai a bace na fito nace dashi ya dago ya kalle ni idanuwan shi sun canza launi a lokacin.
Ya amsa min da kyat tare da fadin muje in sauke ki ban gaisa da anty ba nace mai bai yi magana ba sai kama hanyar fita waje da yayi.
Ni kuma na wuce dakin anty Fati din da sallama na shiga dakin tana zaune saman dogon kujeran dake dakin nata tana gani na ta kakaro murmushi a fuskanta da kyat.
Cikin dan rusunnawa na gaida ita da kwana ta amsa min da lafiya nace zan shiga gidan su hajiya in gaida su tace min a dawo lafiya karamin dan nata yana zaune yana cin irin doyan da aka kai min din.
Nace daddy ba magana ko san mun doya inci ya dauki kwanan ya nufi uwar shi tare da jingina jikin shi da nata sai na dawo nace mata.
A waje na samay shi zaune cikin mota yana jirana na bude na shiga ya ja motar muka tafi duk da bawani nisa bane a hankali yake jan motar.
Mun kai na bude motar zan fita naji yace dani kayan da kika zo dashi suna nan a cikin mota sai kin dawo ki zauna ki kasafa.
Nice mai kasafa kayan kuma ya gyada min kai da alama har lokacin yana a cikin fushin da yake yi don shirun da naji yayi min har muka zo gidan banda wanan maganan bai kara wani ba.
Fita nayi daga motar na shiga ciki ba tare da na tsaya wani abu da Anty amarya na fara cin karo a gidan tace a, a khadija ashe tare kuke da babangida .
Nakai kasa ina gaida ita daga nan bayan mun gama gaisawa na nufi dakin hajiya umma na gaida ita a na dan kai minti goma na fito zuwa dakin mommy .
A gurin mommy na dade don na samu ya buga mata waya ta hada min abin karyawa don ban karya ba na fito don haka na samu kafin in shigo wurin ta tana hada min breakfast.
Ban fita gurin ta ba saida ta tsare ni na karya muna hira da ita wanda hiran bai shafi komai na rayuwan zamana gidan AA ba ko wani nasa sai hiran Abuja dana karatuna.
Nagama nace barin gaida hajiya mama tace ai tasan kina nan kina karyawa tun a kofa nake jin hayanin su zainab da Binta.
Da sallama na shiga duk suna zaune a falon da ihu Binta ta taso ta rungumay tana fadin tun dazu naso zuwa dakin mommy wai zamu hanaki karyawa da kyau.
Kasa nakai na fara gaida sarakuwan nawa tana amsa min cikin dadin rai cike da kulawa a gare ni bayan gama gaisuwan ne zan juya wurin zainab hajiya mama tace min.
Khadija kina sakaci da cin abinci kina haka kada wani ciwo ya samay ki fa mace mai lalura karami irin naki ba,a son tana wasa da cin abinci.
Duk ido suka zubo min ni kaina ban fahinci mai hajiya ke nufi ba a lokacin tace wanan abin abin farin ciki ne aure a bazata haka gashi kuma an samu karuwa.
Na dago kai na kalli hajiya mama da sauri sai kuma na dukar da kaina kasa cikin kunya.
Binta da ke manne danu tace min ko kuma zaki ma hajiyan mu mussun haka ne kin fa san hajiya ko cikin kwana daya ne tana ganewa a jikin mutum.
Dakuwa hajiya tai mata ta rufe baki tana dariya sai hajiyan ta kawar da zancen da fadin nace ya fada maki zancen kawo kayan zainab da za,ayi gobe.
Nace eh mama ya fada min shine ma nace dashi ina son zuwa ta karbe da fadin sai ya hanaki ko ya kirani kuma yana fada min wai zaki zo amma ya hana.
Dana san kina cikin wanan halin haka ai da ban sakaki wahala ba wallahi tunda lefe ne kawai za a kawo ba wani buki za a yi ba.
Mama nu fa lafiya nake shine ya fada maku banda lafiya don gajiyan motan da na iso jiya dashi kawai ya dauka wani ciwo ne.
Ikon Allah irin wanan lalurar ai ciwo ne babba khadija Allah dai ya rabaku lafiya ya bamu mai albarka ai kinyi kokarin zuwa haka wallahi.
Kunya da nauyi ne ya kamani sosai a gurin kamar kasa ya bude in shiga naji alokacin ta lura da hakan tace gashi kin zo khadija.
Idan yan uwan ki sun karaso sai ku tatauna abinda za, a tari bakin dashi gobe koda yake gida ne duka amma hakan ai ba zai hana ai masu wani abu ba.
Tunda yanzu abin ya zama kamar al,adan aure , wasu ma saboda wanan zasu matsa idan za a kai kaya aje dasu .
Nace mama akwai kayan da muka zo dashi wanda yace na azumi ne za,a raba suna cikin mota har yanzun ba,a sauke ba.
Ya fada min Allah dai yai maku albarka ya kara yawan arziki ta hanyar alheri nace amin mama tace yace kece kika san kan kayan idan kin huta sai a ba kowa nasa kamar yadda kuka tsara nace mama dadai akawo nan din sai a raba zaifi.
Tace da sauri a,a ku barshi can idan kin samu lokaci ku raba a can a aiko ma kowa da nasa idan kun kawo nan ganin laifin juna za, a dinga yi .
Shiru nayi ina nazarin maganan ta sai dai a fili cewa nayi to mama ta katse min tunena da cewa Allah dai yayi albarka ya rabaki da cikin nan lafiya kin yi kokari khadija kwai mafalkina yana shirin zama gaskiya a kan ku.
Tun yanzu na fara hango alherin wanan auren a tsakanin ku yau ga babangida a dakina tun safe har wani lokaci muna hiran matsalan shi dani.
Kin san bai iya boyo ba shi da yasan ina mamaki ganin ya dade a

89 / 144

Chapters