karbe Yusuf din da fadin nakasa ne kawai da wulkanci ita ds kowa haka take kamar mai jin warin mutane.
Na fadi shafa turaren zatayi ko ajewa yara su bata wani itin turare ne ban sayo mata da haka zata barshi batai amfani dashi ba yara su zubar ko wani yazo ya dauka.
Ya kare maganan shi cikin jan tsaki yana kiran Affan daga inda yake zaune sai ga yaro yazo da gudun shi yace kace ma laraba ta kawo muna abinci.
Yaron ya kalli uban yace Abba laraba tayi tafiya bata nan da dadewa in fada ma mama ne yace barshi ya mike ya samay ta a daki yace da ita.
Tana kwance baki sa muna abinci bane tace nasa amma ni tunda rana nayi kuma banji kace a kawo maku ba juyawa yayi inda ya fito ya samu Yusuf zaune yana waya.
Ba sai ya tambaya ba yasan bai wuce da zainab yake wayan kallon shi yayi tare da fadin muje gurin hajiyan mu muci abinci don Allah.
Katse wayan Yusuf yayi yana fadin bata girkaz bane ko may yace muje don Allah don yunwa na soma ji rabona da abinci kasan tun safe.
Suna zaune a falon mahaifiyar shi wance ta gama fada da halin Fati din suna cin abinci wayan shi yai kara ya dauka yana dibawa.
Nombana ya gani yayi received din call din tare da fadin slm nace wlsm an wuni lafiya ya hanya ya amsa da fadin Alhamdullahi nace ya su mama da sauran mutanen gidan an samay su lafiya ko?
Lfy ya amsa dashi nace agaida min da su ya su Affan da baba yadda naji suna kiran yaron dashi yace duk suna lfy a huta gajiya a gayar min da anty Fati don Allah, dama na kira inji lafiyan su ne in maka sai da safe yace ya gode ya kashe wayan shi.
Yana aje wayan hajiyan su tana fadin wacece yace khadija ce wai tana gaida ku dan murmusawa tayi tana mai jin dadi har cikin ranta.
KHADIJA
Muna gama wayan dashi na gyara kwanciya dama a kwancen nake don har na kashe wuta ko tun karfe shida da rabi na rufe kofan part dina.
Fruit kawai nasha sai naji na koshi a lokacin sallah nayi na watsa ma jikina ruwa, na haye gadona shine na kirashi.
Tofe jikina nayi da adduan neman tsari a wurin Allah na gama na tofa a hannu na tare da shafe hannaye ga jikina na gyara kwanciya na.
Allah yasa washe gari ban shiga school haka yasa na sha barci na da safe ban ko tashi na nema ma cikina abinda zanci ba.
Sai da yunwa ya damay ni cikin barcin nawa na mike na shiga bathroom nayi brush tare da kewayawa na fito na fada kitchen.
Simple abinci na hada na fito falo dashi na zauna ina ci na bar wayana a kuryan daki ashe yai min har three miscall ina falon ban sani ba.
Sai dana gama na shigo inyi wankane naga kiran nashi diban lokaci nayi naga rana yayi tunane nayi yana ganawa da iyayyen shi a daidai wanan lokacin.
NAFISA
Tana zaune falo gidan tare da yan uwanta fada take masu akan sunki kokarin su kama wani namiji daga irin mazajen birnin nan da suke zuwa wurin AA itama ta samu ta huta da nauyin su haka.
Tunda yanzu duk maganar samad daya biyu zaice ta kwashe yan uwan ta tabar mashi gidan shi tunda bata son a zauna lafiya.
Duk wanda ya ganta zaune a falon yasan Nafisa na cikin wani yanayi dan kwanakin nan.
Kalo daya zakai mata ka hango matsala a tattare da ita wai a cikin ma tana karfin hali ke nan tunda tana samun yadda take so a gidan har yanzu.
Sai dai matsalan ta daya ne shi kuma abinda ke bata mamaki da haushi da takaici mamakin ta da haushinta ta ko shi wai ashe dama zata iya zama da kishiya a gidan nan kwana da kwanaki.
Bata taba zaton ko yar yaren su na buzaye ta shigo gidan ta zata dauki kwanaki a tare da mijin ta ba.
Yau sai gashi yar nigeria ce ta shigo mata gida duk kudin da ta kashe da irin maganin da take banka ma Samad bai hana wanan shegiyar yarinyan ta zauna mata da miji har su kwana a gado daya dashi ba.
Wani irin yawun takaici ta hade a mokoshin ta tare da fadin a fili lalai ya kamata in nuna ma wanan yarinyar ni bata wasa bace.
Idan tsubu ta iya ko tsafi zata nuna mata karya suka iya don bata kaita iyawa ba ita bata taba daukan akwai wata macen kasar nan da zata iya ja da ita ba a zauna lafiya.
Wanan tunane da take yi ne yasa ta rashin jin karan da wayan ta keyi kiran mijinta na shigo mata a lokacin.
Wanan tunanen dashi take kwana dashi take tashi don bata kaunar ta bude ido taga har yanzu yarinyar nan ta saura a gidan ta.
Ta sha alwashin ko ta halin kaka sai taga bayan khadija a gidan nan kuma ta kama mijin a tafin hannun ta idan ta gama da khadija din.
Daga kai tayi tana kallon kofan shiga part dina taji kamar ni take kallo ta watsa ma kofan nawa harara aiko yayi daidai da fitowana daga part dina.
Zan tafi wurin gyaran kai da sauran part din jikina don kusan wata ban gyara jikina ba kaina ya fara min kyakayi don har na sance kitson a haka nake daure shi yanzu da ribon ni kuma ba gwanar barin kai ba kitso bane tare dani.
Sannu fa nace da ita ban sani ba ko ta karba min sannun da nayi mata din nidai na fice ba tare dana kara kallon inda nake ba.
Ita a ganin ta rangwada nakeyi mata bata san haka halittan diya matan yake da rausaya ba ko a banza.
Na dauki lokaci ban dawo ba don na dan biya nayi sayayyan kayan amfani wanda na sawo pad saboda expecting din period dina da nakeyi a cikin satin.
Ko da na dawo gida yamma yayi sosai ban wahal da kaina ba wanka nayi nai sallah na nemi wuri na kwanta .
Waya na dinga yi da yan gidan mu munfi dadewa da ya Amina a wayan muna hira akan yaran ta don akwai ni da son yara sosai a rayuwana.
Har barci ya dauke ni gari ya waye nasan maigidan zai dawo ranan kuma nice zan karbi girki don haka na shiga kitchem tun karfe hudu na fara hada mashi girkin da zaici.
Dakin shi na shiga na gyara komai na fito bandade da fitowa ba Nafisa ta shigo gidan daga unguwa.
Na fito falon gidan ma na bada umurnin a gyara na koma na kammala girkina shida saura suka iso gidan.
Banji dawowan shi ba sai da Yusuf yazo part dina kawo min sakon mommy nasan sun dawo bayan Yusuf ya fita wurina ne na nufi part din shi.
Na samu ya fito daga ban daki yana ganina I a dan sake murmushi yana gyara hannun rigar dake jikin shi haka yasa na fahunci alwala yayi a lokacin.
Gaida shi nayi ban tsaya ba na koma part dina don bin ka,ida sunna don lokacin shiga girki na baiyi ba a lokacin sai bakwai na marance zan shiga lokacina.
Sai bayan sallah isha,i na gama shiryawa kwalliya na zauna na tsara ma fuskana atamfan super na sa wanda maryam ta karbo min su daga wurin dinki kayan sun matukar karbuwan jikina don sun fitar min da surana sosai na jikina
Kallon kaina nayi a mirrow na naga yadda komai nawa ya zauna cas na kara feshe jikina dakyau da kayan kamshi.
Na dauki basket din tare da kulle part dina zuwa wurin shi dauke da basket din dana shirya abincin shi a ciki .
Falon sama din na tsaya sai da na shirya abincin komai na aje inda ya kamata daga baya na naji an rungumo ni.
Dan firgita nayi tare da juyowa ina kallon shi kaina na dan langabar da kaina tare da fadin wallahi kaban tsoro yace Allah ko sake ni yayi bayan ya murza min hannu yace mai aka girka min cikin sakewa da jin dadin ganin haka yake magana.
Abinda na fahinci kafi so ne na girka maka ko zakaci ban sani ba ya fara bude warmer din ke nan sai ga Nafisa a gaban mu tana fadin.
Samad ya naga haka ke may kikeyi anan ta juyo gare ni tans tambaya na tana aje kulan dafa dukan da ta shigo mai dashi da plate.
Ta fara fadin wai may kuke nufi ne a gidan nan ya karba da fadin kamar na may fa?
May ya kawo wanan wurin nan yanzu may tazo nema a wurin ka ko iskancin nata da samun wuri har yakai haka ban sani ba.
Ke ban fahinci maganar ki ba fa Nafisa ki fito fili ki min magana yadda zan fahince ki kin tsaya kina wani sharfi haka.
Tace amma kasan a ka,ida nice da girki yau don ko yau ka dawo daga tafiyar da kayi kaga ke nan nice zan karbe ka yau.
Yace wani makamin ne ya koyar dake hakan ina ranan jumma,a nabar garin nan da safe da yamman ranan ya kamata Deedar tayi giri bana gari .
Washegarin asabar sai wa zaiyi tace ita yace idan gari ya waye fa tace ita ya kamata tayi yace kin ba kanki amsa yanzu.
Tace wallahi baka isa nice ya kamata nayi tunda daga tafiya ka dawo yaudin don haka a wurina zaka sauka ke nan.
Wai hauka kike yi ne Nafisa ko mai tace kaidai ke haukan don gashi kuna son ku dulmiye ni akan hakkina.
Tsaye nake gefen su mamaki ya hanani yin magana don naga haukar kishi a filin Allah yau sai kallon su nake ina sauraren su.
Ke wace irin dakikiyace wai amfada maki ana haka ne idan kinga anyi hakan tafiyace ya kama mutum da zai share lokaci bakuma ance lalai dole mutum sai ya sauka dakin babba ko karami ba.
Zaka iya sauka a ida zuciyar ka ke so ko wancen karon na sauka wurin ki ne badon komai ba sai don a zauna lafiya badon wani abu.
Don may ita zata fahince ni ke ba zaki tsaya ki natsu ki gane mai addini ke nufi da hakan ba sai shirmay ban za.
Tace yanzun kana nufi a wurinta ke nan zaka sauka ko may yace ba itace dani ba yau don may ko ba zan sauka wurin ta ba.
Samad amma kai macucine ashe har zaka iya rufe ido akan wanan mai ruwan fulanin ka tozartani a gaban ta.
Uban may zata tsinana maka a dakin banda kwaciya tana shafa ma janbaki tana bata gado da katifa.
Bayan wanan akwai wani abinda zai shiga tsakanin ku ne da ita bayan na gane hakkuri kake da ita tunda aka kawo ta.
Yace yaya kikayi kiks san hakan ko labe kike zuwa kina muna ban sani ba koko ita ta fada maki photo nake ganin ta ba mace ba.
Ina macen take anan wanan ai mun sani farin mai ne wanda matan ku ke shafawa an shafo don a gwada dani aja hankalin ka.
Ko gashin dokin da take karawa ne ya rufe maka ido kake ganin days muke a wurin ka dariya sosai maganan ya bani ban san lokacin da nace da itaba.
Au haka kike tunane a she diba ki gani yadda Allah ya baki fari da komai haka nima ya albarkace ni da abina kamar ku idan ma gashi na doki ne ai yana samun gyara akai akai ko ?
Ba kamar nake da ke cushe a guri daya ba sai doyi balle Allah ya tsareni da kari a kaina don ni musulmace ina tsoron haduwa da Allah na tunda ya sani.
Tace ina musulma a nan dida karki bata min suna kamar yadda kike bata mashi nashi don ni khadija nake.
Ki koma makaranta don Allah ki fara sanin Allah kafin kizo kina karanta ma mutane kishin ki na jahilai.
Jahila na gidan ku kin bari a hasale na juyo gare ta dan jin abinda ta fadi wanda nasan uwata take nufi da jahila.
Nafisa kina haukane wai da zaki zagi iyayyen ta tace na zage ta ko zaka rama matane ina sauraren ka.
Nace shi ba jahila bane irin ki don yasan abinda yake yi ki koma makaranta da wanan jahilicin naki hakana ko zaki san abinda kikeyi nan gaba.
Tace Ke da ke zuwa makarantar may kika karu dashi banda bin maza da kike fitayi wanan kuma kanki kike fada ma don ke ce kullun a hanya ke ba kasuwanci ba aikin office ba wawiya mai fitsari taye ba kama ruwa ko tsarki don haka banga laifin ki ba idan kina haukan ko zargin wani.
Abinci ne yau ko zaki mutu nice da miji sai yaci kuma mu kwana tare da baki so ki gani kije ki mutu ko ki fada ruwa ki hade ran ki.
Zata fara ihun ta yace Nafisa bar nan gurin tun muna sheda juna dani dake tunda kin san ba gurin ki nake ba yau.
Agaban ka kake jin zagin da matar ka take min yace waya fara zagin wani dake da ita ki bace min dagani nace kafin ranki ya baci.
Tace bazata fita ba yazo ya ja mikewa yayi ina kallon shi ya ficiki hannun ta tana turjewa zuwa waje ya wurgata tare da rufo kofan saman gaba daya ya dawo ya zauna yana huci tare da rike kan shi.
Da fashi nayi don in nuna mashi bai damay ni ba nace kan wanan abin zaka bata ranka kafa saba da halin matar ka ba komai ya kawo ta ba don kawai ta bata maka farin cikin kane ko nawa.
Ajiyan zuciya ya sauke tare da fadin wanan bansan ranan da matsalanta zai kare ba a gidan nan .
Nace hakkuri zakayi damu don haka halin wasu mata yake akan kishi tunda ba mai kaunar kishiya a tare dashi.
Cikin zolaya yace har dake kenan ashe nace ni ba mace bace da zance ban kishi ko wace mace ai tana da kishi sai dai na wata yafi na watane.
Ranan mun sha zagi a gurin nafisa da kyar yan uwanta suka lalabata bayan tayi masu bayani suka ce itace bata lissafa da kyau ba.
Suma sun sha fitina a gurin ta kafin taja kafan ta zuwa daki tana jin maranta yana masifan ciwo a lokacin.
Yau AA ya sha mamaki duk cikin kawar da fushi a zuciyar shi kamar yadda nafisa ke son ta bata muna daren mu dashi yasa na zage nayi mai abinda ban taba yi mashi ba tun fara aurataya na dashi.
Wanda na barshi da mamakin hakan a cikin ranshi can gabsnin asubs ne mukaji dukan kofa da karfi cikin tashin hankali.
Rigan shi ya zura a jikin shi ya nufi kofan yana tabayan waye a kofan muryan Yanyala ce take fadin Nafisa ce ba lafiya jini ne ya balle mata.
Hankali tashi ya bude kofan yafita daga dakin binshi da kallo nayi tare da fadi a fili ikon Allah Allah ka kareni daga sherin wanan matar lafiya a cikin kwanciyan hakali ka, ka haushe ni akan ta ko da yaushe.
Jin shi shiru yasa na tashi da daura zani a gaba na saka hijjab dina na fito daga dakin.
Kowan su hankali shi a tashe yake na dan karasa part din nata sai dai ba isa kusa ba a daidai lokacin da ya fito da ita rungumay a jikin shi cikkn gala baita suka fice daga gidan.
Su samihane suka shiga ba tare da yanyala ba a gurin su nake ji wai cikin jikin tane yake son ya bare Allah ya sauwaka nai masu na dawo saman wanka na yi a cikin daren nan tare da dauro alwala na fito na tayar da sallah.
Ban kwanta ba sai da akai kiran sallah asuba nayi sallah tare da jawo wayana na kira layin shi ina tambayan shi mai jikin yace da sauki.
Am bata gado ana son cikin jikin nata ya tsaya Allah ya sauwaka nayi mai ban kwanta ba na fito na nufi part dina.
Kafin dan lokaci na gama abinda nakeyi ganin bai dawo ba had lokacin yasa nafito ko zan samu mai sauke ni a school.
Nakoyi sa,a don su Samiha zasu asibitin nai ma driver magana ya sauke ni a school yacs ba damuwa hajiya.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Tunda na isa school hankali na wurin su ban cikin natsuwa don a yadsa naga sun fita da ita ta matukar ban tausayi.
Sai dai abinda ba,a saka ka ciki ba kuma nasan ko na saka kaina ba zanyi fari a gurin Nafisa ba idan ma banyi hankali ba zata iya cewa nice na jefeta da wani asirin haka ya samay ta.
Sai dai na kudurta a raina idan na fito