MIJIN BUZUWA complete Hausa Novels.txt

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   115 / 144

342K to 345K   out of 431K words

haka yazo ne mu tsayar da magana a sa mai lokaci wai baison ya zauna nan ba mata nace zaki iya da yaran hajiya umma kuwa ?
Tace da ita zan zauna bafa gari daya zamu zauna ba waike baki murnan zamuyi aure a gida daya dake ne ina ruwa na da wata umma can.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Monday da muka shiga makaran ta da kyat na samu zuwa don yanayin da nake jin kaina ranan dai a dadafe nayi komai daya kaini.
Asibiti na wuce sun dubanu suka ce wai juyawa ne yasa nake jin haka ko wani month din zai juya sai mace ta dan ji jiki magani pain killer suka bani muka dawo maryam ce ta raka ni.
Two ina gida ruwa na watsa a jikina nayi sallah na kwanta can cikin barci nake jin laraba na kirana sama sama na bude idona.
Tace baki kike dasu a falo da kyat na tashi sai dana dan jima a zaune na mike zuwa falon mata ne da ban san su ba su biyu zaune.
Tun kan na zauna nace laraba kawo masu abin sha mana na juyo ina masu sannu da zuwa ina kaiwa zaune.
Gaida su na fara suna amsawa laraba ta kawo masu drinks din kwali da cups ta aje a gaban su matar tace sun gode.
Ai da kin barshi muzo maki godiya ne dama maigidana ne ya turo ni ai mai godiya a wurin ki nasan baki san mu ba ko ?
Nace wallahi ban sheda ku ba tace matar SJ jalingo ce da sauri na dago kai ina kallon ta nace ayya ban san ku bane na fara gaida ita tare da tambaya ya gida.
Tace yaso muzo tare dashi yai maki godiya kan alherin da kukai mai keda maigida shine ya fara turo mu.
Nace ai babu komai idan wanan ne ai don yaya Adam akayi tunda ba sanin ku nayi ba sai dai mun sha rigima yace a nan kuka biyo mai kuma.
Matar tace ya fada muna ranan da mukaje office din shi yace abinda mukai mai baiji dadin shi ba ai ko wurin Adam muka bi zai muna din.
Murmushi nayi nace haka yake shi nace hajiya baku sha ruwan ba tace no ki barshi a koshe muke nace haba ko kun raina ne da sauri tace haba dai.
Wallahi tun dazun muka so zuwa sai wanda yasan gidan zai kawo mu ya dan bata muna lokaci nace Allah sarki ba komai hajiya ai ba sai kunzo ba.
Don yanzu mun zama daya daku tace hakane ashe cikine dake haka nayi murmushi tace Allah ya raba lafiya wace suke tare ne ta karba da Amin.
A raina na amsa mata tace a, a kina kunya irin namu na fulani ne sai dayan da batai magana ba tace nima zubinta yai min na fulani tunda muka shigo.
Nace mu fulani ne asalin mu sai dai bama jin fulanci ne tace haba kinyi kama da fulani sosai wallahi suka mike tana fadin ana jiran mu a waje ga wanan maigida yace a kawo maki.
Da sauri na kada kai nace a, a wallahi hajiya bazan karbi ko kwandalan ku ba don Allah nayi maku Allah yasa a more .
Da mamaki ta tsaya tana kallo na tace haba dai kanwata idan kinyi haka ba zamuji dadi ba ai nace wallahi hajiya bazan karba ba tace to shike nan ban layin ki don in kin haihu muji muzo barka.
Na karanto mata layin nawa tasa a wayan ta har wajen gida na raka su motar shigan su kawai ma abin kallo ne daidai nan nafisa ta danno gidan da motar ta idon ta a kan baki na.
Ta fito ta shige da yaran ta ina tsaye matar tace wanan fa kardai ince kishiyar ki ce don mun taba hadewa a gurin wani buki da ita.
Murmushi nayi nace kishiyatace hajiya ta kada kai kawai tace bari zamuyi waya tunda ina da layin ki don kin min sosai wallahi.
Nace na gode suka ja motar su suka tafi na shigo cikin gidan Ihisan ta sheko ta rike ni nace ihisan kun dawo ya school tace cikin shirmay yara uncle din mu yace ban iya karatu ba zata fara zuba sai ga uwar ta fito.
Wani tsawa ta daka ma yar tace maza ta bar gurin ta shiga sake yare nan na fahinci tana koyawa yaran yaren su.
Ta juya da hausa tana fadin idan ba mutum ya haifar min yaraba ya barnmin abina mana wanan wani irin bakin naci ne haka.
Nace kinga kafana agun yar ki sai dai su biyo ni idan kuma sun zo bazan koresu ba don ni ba irin ki bace mara hankali don ni banda lokacin ki yanzu.
Na shige na barta awurin kalamin ta yasani tsayawa cak tace munga ciki sau ra muga haihuwan shi kuma in don shi kike taka kowa yarda kika ga dama.
Najuyo nace ke jahila ce ta karshe wallahi mai jayayya da ikon Allah ni bazan biye maki ba mu koma daidai don haukanki yafi karfi na na rufo kofan part dina na barta nan.
Maganganun ta suna matukar ci mun rai sosai wallahi wanan ko haihuwar nayi gidan nan yaya yaran nawa zasu taso a cikin wanan rayuwan gida kullun fitina haka.
Duk da anty hauwa tace in yi kokari in haihu a cikin gidan nan ammani ina jiyo ma kaina abinda kaje ya dawo ne idan na haihu a cikin wa yan nan kurayen dake farauta na haka.
Zan mai magana ya barni in koma gida ko kaduna da zaran month dina ya kama wata zuciya tace min karatun ki fa.
Ajiyan zuciya na sauke nace kuma dai dole fa inyi hakkuri da wanan karatun in sama ma kaina lafiya a gidan nan tukun zai fi in da hali ni kan ya canza min gida ma da yafi.
Ranan da nayi girki ina son mashi maganan kaini gida sai gashi ya rigani fadin gobe zamu Niger da Nafisa babanta baida lafiya.
Cak na tsaya ina fadin goben nan yaya yace eh in Allah ya kaimu sai dai a can zan barsu in dawo sai tayi kwanaki ta gama ganin su ita zata dawo.
Antan cikina ne ya kada sai da naji abincikina yana juya min lokaci guda don mamaki abinda ya fada min.
Dama haka maza suke munafukai ne wai ni naje gida bai kaini ba sai driver yasa ya kaini ya dauko ni.
Lalai na miji ba dan goyo bane ba a kuma bashi amana ni ke nan iyayyena basu kai yaje ya gaida su ba ke nan har ya kare bayanin shi ban kara fahintar may yake fada min ba .
Ya lura da sauyawa na amma sai ya dake kamar wanda bai fahinci wani abu ba daga gare ni a dadafe naga gari ya waye min na fice daga dakin.
Bai kulani ba ya gama shiri ina jin hayaniyar su ya gaure gidan na shige na dakina can sai gashi ya shigo ina kwance a kuryana.
Yasha wani shadda sai maiko take zubawa duk da shi ba gwanin saka kaya hausawa bane sai kayan sukai matukar karban jikin shi sosai .
Amma ni sai kyau di ya koma min duhu a idona ya karaso inda nake ya samu bakin gado ya zauna.
Mamaki yake yadda tunda yayi sallama ban karba mai ba gashi na nuna ma ban san shigowan shi ba dakin.
Muryan shi naji yana fadi bakyajin dadi ko yau ba zaki shiga school bane na ganki a kwance haka shiru nayi mai ya kara tambaya bakya jin dadi ne wai Deedar.
Nace lafiyata kalau yace ki fada min mana udan bakyajin dadin jikin ki ne a kaiki asibiti nace idan ma banjin dadi ne ai wanan ni ya shafa ko ba kai ba.
Yace may kuma yakawo wanan magana haka nace don Allah malam kaje kaji da abinda ke gaban ka ka barni in ji da nawa zancen matar ka shine a gaban ka ni da ban da galihu a gurin ka ai ban samu wanan gatan ba.
Ko asibiti sai idan nakai kaina don jin lafiya ta baka damu da ka san lalurana ba sam a gidan nan ajiyan zuciya ya sauke tare da fadin.
Duk akan tafiyan da zanyi da Nafisa ne kike fada min haka nace Allah dai yakai lafiya umma ta gaida assha na mike na shige ban daki na barshi a gurin.
Ya dade zaune gurin yana jijina magana a ranshi kafin ya mike ya nufi kofan ban daki ya murda yaji shi a rufe gam ina daga ciki ina jiyo muryan shi yana fadin.
Deedar ki fito muyi magana na fahinta dake shiru ban bude kofan ba har yagaji da jira ya fita danaji shiru na bude daki na fito gidan ms tsit a laman sun tafi ke nan.
Ina tsaye ina sa kaya a jikina kiran wayan shi ya shigo min ban daga ba har kiran ya katse ya sake kira karo na biyu hakana kyale wayan ya tsuke.
Nagama shiri na fito na samu driver a waje wai yana jirana nace ayya ka huta abinka zanbi kawata ne ta sauke mu sai ga maryam ta iso ta bude min na shiga.
Kallona take yi tare da kallon titi wai may ke damun ki ne khady yau na ganki kinyi wani so weak dake mana haka ina AA yake bai saukeki ba kuma ?
Ban kalle ta ba na bata amsa da fadin ya tafi Niger da Nafisa yau da safen nan da sauri ta juyo tace Ni may khady don Allah ki bar wanan wasan .
Nace wallahi maryam yau da safen nan suka tafi tace amma dai maza shegu ne wallahi yanzu shi baiji kunya yin hakan ba khady.
Nace kunyar may zaiji ba matar shi bace ni don yaje garin su ba shine damuwa ba banbancin da yake nunamin a filin Allah maryam shine ya fara isata wallahi.
Ki duba ni da naje gida maryam ba shi ya kaini ba bai kuma je dauko ni yanzun ma bai fada min zancen tafiyan ba sai jiya da daddare yake fada min.
Tace ya fada maki yasan bai shuka gaskiya ba ta yaya zai fito maki da zancen da wuri ki tayar mai da hankali ya fasa.
Koda yake itama baki san irin kwaram din da suka sha da ita ma kafin suyi tafiyan ki kyalesu su suka sani indai sune ko acan sai sun sayar da hali ai.
Nifa tafiyan bai damay ni ba maryam sai dai ni da yake nuna mata ba kowa bace a gare shi nan dai na kora mata yadda akayi muna shiga school tace kyale shi kada ki daga sai kin ja masa rai sosai.
Mun shiga lectures bacin rai bai barni nayi abin kwarai ba ranan da kyat naga mun taso ta dauko ni ta kawo gida.
Gidan naga yai min mu kadai dagani sai laraba kadai a gidan da dare ma na samu ya kira ni bandaga wayan ba karshe ma kashe wayan na kwanta abina.
Kwana uku ban bude waya ba ina amfani da waya ta tada da layin dabai sani ba maryam na sauke ni motar Yusuf tana shawo kwanan gidan.
Tsayawa mukayi muna dakon zuwan shi gaidashi mukayi ina fadin haba yayana ka manta da kanwan ka gaba daya.
Yace ba hakana bane khadija aiyuka ne sukai muna yawa ban kuma samun zama yanzu sosai nace Allah sarki maryam tayi min horn tace zata wuce nace sai gobe.
Hararan ta yayi yace kece mai daurewa karya gindi ko kin hanata bin umurnin mijin ta tana biye maki ko ?
Nace haba yayana maryam bata da laifi binta shine sauki a gare ni tunda wanda nake nan don shi baisan muhinmaci na ba.
Yace a, a kanwata kada kice haka don Allah don ba haka zancen yake ba gaskiya daga cikin mota maryam tace baku da gaskiya wallahi.
Ke rufa muna baki don Allah tsigar da yake magana da ita na fahinci wani abu yace yanzu khadija ya dace ace mijin ki yayi tafiya baki kirashi kinji saukarshi ba har wanan lokacin.
Ai ba tafiyana yayi ba yayana tafiyar matar sa yayi kuma suna tare kiran mai zan mai kumani yanzu Allah dai ya dawo dasu lafiya maryam tace shike nan kuwa.
Yace ki daina bin zancen wanan mara gaskiyan zata kaiki ta baro wallahi nace yayana maryam din ne kuma yau zatakaini ta baro ?
Yace kin ga mubar zancen nan muyi na gaskiya don wallahi baki kyauta ba khadija mahaifin Nafisa ne bai da lafiya suka je gaida shi.
Daga cikin motar ta kara fadin shikenan kuwa ke dan Allah barnan ai surikin kine zan fada mai kece mai zuga mai mata tace rufa min asiri tana kokarin jan motar ta ta bar gurin.
Yace tsaya ai magana ta fahinta ai abokin kuka ba a boye mai damuwa abinda kikayi ai ba daidai bane khadija dayakiraki ai sai ki dauki wayan kiji korafin shi ko.
Amma yana can kin saka shi a damuwa gashi kin ki daukan waya ga kuma kinki bari driver ya kaiki school gaki a cikin yanayi.
Nace ai yanayin nawa bai gaban shi nice da kaya ni ya dama ya kada kai yace ba hakana bane khadija ku na ma maza fahinta baibai wani lokaci.
Lalurar ciwo ya kawar da komai yanzun haka sai da yaje ne suka kai tsohon asibiti duk wanan ciwon ba wanda ya kaisa asibiti ashe.
Nace eh hakan yana da kyau sosai yanzu dai barin in kirashi kuyi magana yaji lafiyar ki don Allah ko hankali shi zai kwanta.
Nace akwance hankalin shi yake tunda yana tare da farin cikn shi ai basai yaji tawa ba baza ki min ba ke nan sai naja na tsaya daga cikin mota maryam tace ki saurare shi kiji may zaice din.
Bashi ke nan ba baidai wuce dadin bakin su na maza zai maki tunda kina sokuwa sai ki yarda Yusuf yace khadija ki saurare ni nan kiji may zan fada maki.
Wallahi wallahi duk mu nan musan AA yana son ki shuumancin matar shi kawai ke damun ku khadija kin yi hakuri a gidan nan kowa ya sani kuma kina kan yi .
Kinyi abinda bako wace mace zata daure mayin sa ba saura kiris ya rage khadija buzuwa takai karshen ta a gidan nan.
Yanzun dai ga wayan saura bayani zan maki idan kun gama wayan yana kira ya miko min na karba muryan shine yake sallama na amsa.
Yace kuna lafiya nace kalau yusuf ya zagaya gurin maryam ya barni a gurin muna wayan ba wani magana mai tsawo mukayi ba ya tambayi lafiya tace da dalilin da yasa na ki daukan waya nace ba komai sai anjima na kashe wayan nace wa Yusuf dake duke ga wayar shi ya karba yana fadin har kun gaisa nace eh nagode.
Yace ki kara hakkuri aimu ko hanzu bukatan mu ya biya khadija kin shigo gaki har da cikin a gidan nan.
Wanda ba wanda yai tsamanin hakan a gidan nan haihuwan ki gidan nan shine babban masifan dake addaban Nafisa a yanzu don nike jin irin wayan da sukeyi dashi idan muna tare.
Don haka don Allah ki kara daurewa khadija ansan abinda zafi nima na nuna mashi abinda yayi bai kyauta ba yakawo min uzurin rashin lafiyan tsohon na yarda.
Haka dai muka dan dauki lokaci dasu a gurin karshe mukai sallama suka tafi na shigo ciki na samu laraba a babban falon gidan gana kallo.
Nan na zube falin muna dan taba hira tace ta kawo min abinci ne nace ta kawo min amma kadan na mike ina fadin bari mu shiga ciki dayani in rage kayan jikina.
Sai da na watsa ruwa na fito falon na samu ta aje min kulan abinci na zauna naci muna gurin akai sallah a nan nayi sallah tara muka shige daki.
Cikin dare na falka da tunanen mafalkin da nayi a gidan maganan tsoho bado ne ya fado min a raina tashi nayi na gabatar da nafila ban kwanta ba sai da aka kira sallah bayan na sallamay na fito ina kiran laraba tafito a dan gigice tana fadin lafiya uwar dakina ko jikin ne.
Zama nayi ina fadin mama wani malki nayi a gidan nan jiya yau yakai kwana uku a gurin mugudanan ruwan dakin maigidan nan ko dai akwai wani abune da aka boye a gurin nan mama ?
Tace bazance a a ba don kin san wani lokaci mafalki na zama gaskiyane tunda idan mutum nada tsarin mutanen a kanshi zasu iya nuna mai haka ko kuma Allah da nasa ikon idan zai yake ma mutum wahala sai ta baiyana maka abu ta inda baka zata ba.
Nace yanzun yaya ke nan tace idan kina gane wurin muje mana zan ma mai gadi magana tunda muna shiri dasu sai mu tona mu gani tunda mu kadai ne a gidan.
Tunda safen nan muka fita zuwa baya tare da dayan maigadin dataiwa magana naga kokarin mutumin nan daya iya tona wurin baiji kazantaba sai gashi ya ciro wani kwallaba dake da layu da yawa a cikin sa.
Mamakine ya kama mu sosai jikina har rawa yakeyi yace

115 / 144

Chapters