Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MIJIN Buzuwa Complete Complete Hausa Novel by Nil

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   144 / 144

429K to 431K   out of 431K words

bi bayan shi.
Ya dan jima waje tare da su kafin ya dawo ya samay mu sai zuba habaici anty Fati keyiwa nafisa bata samu bakin maganan ramawa ba.
Koda ya dawo bai furtawa kowa komai ba ya haura sama ya barmu a gurin naso jin matakin da zai dauka amma sai ya bar mu a duhu ga zancen.
Itace ya kamata tayi girki a ranan sai yace fati ta karba nidai ido na sa mashi har in fahinci may yake nufi da mu kan zancen.
Sai bayan kwana biyu ne na fara fahintar komai don haka zai dawo ya zauna damu a babban falon gidan da yaran mu nan zamu zube ai ta hira da raha ita kuma tana daki da yan uwanta ba wani walwala ko ni shadi a tare da ita.
Ga Ihisan daya hana ta zuwa gurin Nafisa din koda wasa yarinyar ta tsorata sosai dashi bata zuwa wurin nafisa din koda baya gida.
Haka yasa samira ma ta dawo mu,amula damu idan muna falo itama anan zata zauna gurin mu koda uwar ta kirata minti biyu yayi yawa zata dawo inda muke din.
Har komawan mu yayi wanan karon da Ihisan muka tafi Nafisa ta tayar da hankalinta sosai har takai karan shi gurin iyayyen shi.
Abba ya kirashi nan dai ranan ya warware ma Abba komai na zaman su da nafisa din bayan ya gama sauraran shine yace ka kyauta da bakai saurin sakin ta ba.
Don idan mace ta kauce irin haka ba saki ne abin yi gare taba kamata yayi namiji ya horata a gida ko zata gane ta dawo hanya madaidaiciya ta gyara halin ta.
Idan ta gyara zaka gane idan kuma ba mai gyaruwa bace zata koma ma halinta kaga a wanan lokacin duk matakin daka dauka a kanta shine daidai.
Amma sakin baida wani amfani gare ta sai kaga mace bata hakkura ba ta koma ga wani hali wanda bai dace ba yanzu dai idan tana da hankali zata gyara halinta tunda ta gwada taga ba wani riba ga mace mai irin halinta.
Shi saurin saki illa ne gama ga haihuwa a tsakanin ku duk inda tabi dole mutane suyi kwatance da kai suna fadin tsohowar matar wani ne uwar yayan shi.
Sai yara su taso basu san abinda ya hada iyayye fada ba sai su dauka don wance aka saki uwar mu ba sauran shiri tsakanin su da wanan matar ta gida kaga an samu akasi a gurin.
Don haka na gamsu da bayanin ka don ba matar da za a barma diya ta tarbiyartan dasu bane da wanan halin nata.
Yayiwa Abba godiya washe gari muka daga muka bar kasan nan muka barsu da Fati a abuja zaune ba wanda ke shiga alamarin dan uwa.
Bayan wata uku yake shigowa ya koma wanan tafiyan mun dauki lokaci sosai bamu zo Nigeria ba har muka kai sadiya asibiti akai mata aiki a kanta watan mu daya a can Anty Fati ne tazo ta zauna muna da yara har mu dawo.
Alhamdullahi aiki yayi kyau sosai don an gyara kan ya koma daidai yanzu ta fara tafiya bata san uwarta data haife ta ba sai ni ba wani ban bancin da nake nunawa a tsakanin su da diyan dana haifa.
Sai dana kara haihuwa ya bari nazo Nigeria lokacin na bunkasa sosai na kara ilimi yadda ya dace ko wanan zuwa munyi shi ba a cikin dadin raiba don jikin Abba da ya kiya yana asibiti kwance.
Na daukarwa yarana hutu muka shigo Nigeria yarinyar da nake riko itama ina jin dadin ta ban barta ta zauna haka ba sai da tayi karatu a can.
Mun zo da kwana daya muka wuce kaduna duba Abba ranan yayi fada da anty fati na rashin zuwan su duba Abba din don cewa tayi bai bada bakin su tafi bane.
Don haka bamu je tare dasu ba yara kawai muka aje a gidan wurin Binta muka nufi asibiti inda muka samu Abban a cikin wani yanayi na jin jiki sosai.
Yana ganin mu duk da sunce bai magana sai gashi yana murmushi yana son ya yunkura ya tashi ya kasa.
Mun dade a gurin Abba din kafin mu dawo gida washe gari su maryam suka iso da safe da yaranta biyu .
Sai su Anty Fati da Nafisa da suka zo suma ga zainab da yaranta muka cika a gurin Abba din don yace muzo mashi da yaran ya gansu.
Ranan anyi murna kwarai da jin saukin Abba din don alama ya nuna ya dan samu lafiya ina hada mai abincin da zai kara mai kuzari ya kara jin katfin jikin shi sai gripe water irin na yara da nake sa momy ko anty amarya su bashi.
Don yana taimakawa sosai gurin mutumin da ya dan manyanta ya ji karfin jikin shi ba wani hayaniya sai dai na kula da Nafisa dake son jan yaranta a jikin ta.
Yaran daine basu bude ido da ita ba don haka basu damu da al,amarinta ba ko inda take basu zuwa.
Ga na kula har lokacin ba yarda a tsakanin ta da maigidan da ma yan uwanshi dake yawan hattaran ta a kusa dasu.
Satin mu daya Abba yace ga garin ku muka tashi a cikin tashin hankali don ban tabs ganin AA ya shiga irin halin da ya shiga ba a ranan.
Anyi zaman makoki na kwana uku mutane suka watse har mutanen Niger ( minna) sunzo mota uku yan uwa da abokan arzikin mu da yan uwana na Ka,oje suma sai da suka ciko bus sun zo min gaisuwa don muna zumunci sosai dasu.
Satin mu uku kaduna muka dawo Abuja inda yanzu nauyi ya karu akan AA din Allah ya taimaka yana da karfi sosai ya kawo saukin abin.
Don bamu dawo ba sai da ya hada kan gidan nasu ya ba wa kowa abinda yake bukata ya biya wa yan makaranta kudi school fees.
Nan ya gane tsohon ba karamin kokari yake akan iyalin shi ba gashi ya hada kan zurian shi guri daya kafin ya tafi ba wani baraka a tsakanin su sai dai wanda ba,a rasa ba din.
Ranan da muka dawo don su Nafisa sun rigamu dawowa ita da Fati sai daga baya muka dawo nafisa tayi abinci amma da muka iso tace tabar min girki nace a a tayi abinta.
Nasan yana daga cikin halin da take son nuna mashi ne na nadaman ta a yanzu sai dai duk wanan abin bata burge shi ba don tsanan ta ya riga da ya darsu a zuciyar shi ko.
Zaman dai suke hakana bai yarda wani daga cikin mu ya nuna mai banbanci a gida ko kadan wanan abin yana damun nafisa don kishi a zuciya yake haline na halitan mace sai dai na wata yafi na watane kawai.
Idan ya tuna da maganan Abba yakan ji jikin shi yayi sanyi akanta yaso yayi koyi da abinda Abba din ya koyar dashi.
Da alama ba zamu koma kasan waje ba don yaran daya nemawa makaranta anan yanzu suna falo zaune na fito da yara zan kaisu islamiya ko wanin su yasha fararan kaya da hula.
Sai sadiya data rike min hannu muka fito tare tana min shagwaba nayi masu sai mun dawo nafita da yaran ta bimu da kallo.
Lokacin maigidan baya gari yayi tafiya washe gari koda na fito banga motar nafisa ba yasa nasan tafita ne har na dawo gidan maryam ina zaune ina cin abinci wayana yayi kara na dauka.
Yusuf ne muka gaisa yake tambayana ko akwai wace ta fita ne a cikin mu nace ban tsan mani ba sai dai barin sa Sadiqa ta duba min.
Ta dawo tace ance nafisa ce ta fita na kirashi ina fada mai yace to sunyi accident yanzu aka kirashi ana fada mai hanyan keffi.
Na maimaita kefi kuma yace eh gashi ma yazo asibitin da aka kawo su sai dai ance a motar wasu sun mutu wasu kuma sunji ciwo sosai.
Hankalina ya tashi na mike na fito ina fada ma fati tace subbahanallahi.
Dama tunda naga ta fita ko sai dawo batai muna ba nake zargin wani abu Allah dama ba azzalumin kowa bane yanzu haka wurin bakar biye biyen bokayen su ne haka ta faru dasu.
Nace kada tace haka ya kamata musan da wa yanda ta fita samiha tace da yanyala suka fita dawata kawar su.
Munje asibitin mun samu tana a wani hali ba a bari mun ganta ba sai yake fada muna sauran sun rasu ko take a gurin da abun ya faru.
Ita ma dai tana a wani yanayi ya kira AA bai samay shi ba yana dai trying din layin shi har yanzu salati na saka tare da fadin yanyala ce wanan dattijuwar da suke tare.
Sai dare ya samu layin AA din yake fada mashi abindake faruwa yace gamu tare a gurin su yace a bamu wayan ko ya saka a handfree kowa yaji.
Ya fara fadin may yasa kuka fito bada sani na ba ku koma gida kada kuma wace ta kara zuwa asibitin nan a cikin ku dama amana ai gudace na fada mata duk wanda yaci amanan wani a cikin mu Allah ya baiyana shi.
Yanzu gashi ashe bata bar wanan halin nata ba zanyi magana ya kashe wayab shi dole muka dawo gida kamar yadda yace don bin umurnin shi.
Sai dai ina tura laraba ko Sadiqa sukai masu abinci acan saboda Allah bayan kwana biyu ya dawo garin abincin ma daya gane ya hana kuma baije asibitin ba ya dubasu.
Kafanta ance sai an fita da ita waje har kano aka tura su sunce bazasu iya ba sai dai idan yanke mata zasuyi a nan.
Yan uwan ta sunzo daga Niger sani Allah sani Annabi ya yarda ya bada kudi koshi don hajitan su ne data saka baki ya yarda aka fita da ita waje.
Watan su hudu a can ta dawo saman keken ta ba kafa ba zuwa gurin boka miji kuma bai kulata tana dai zama a gidan zaman takaici da dana sani.
Tana kuma kallon gata da ranta anayi bada ita ba ga duniyan ga komai amma jin dadi yafi karfin ta yanzu sai dai ido.
Nikan sai yara nake zubawa a gidan sai dana haihu bakwai dashi na dakatar da haihuwa badon ya so ba ga aiki da nake dan tabawa ina aiki da humanright yanzu.
Masha Allah da fatan kun fahinci darasin da wanan sakon ya kawo maku badon kowa zai gamsu ba sai wanda Allah ya ba ikon gamsuwa da hakan dogara ga Allah shine mafita, ga bawa.
Kyau ko nasaba bashi zai kai mu ga abinda muke burin samu ba kyakyawan hali da dogara ga ubangijin mu shine alfanu gare mu da fatan zaku yafe min kurakuren da na rubuta a ciki sai mun hadu a sabon labarin mu mai suna kanin ajali
Nagode kwarai da kaunar da kuka nuna min wanda ba hikima na bane abin daga Allah ne don Allah mu yafe ma junan mu yan uwa.
Taku har kullun zainab din ku labarina dai sai anyi hakkuri dashi akan zamantakewan rayuwan mu na yau da kullun ne a gidajen mu na hausawa.
Nagode nagode nagode da kaunar ku gare ni da fatan zakuyi hakkuri danu hakana.
Sai mun hadu ma,assalam


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU

144 / 144

Chapters