MIJIN BUZUWA complete Hausa Novels.txt

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   124 / 144

369K to 372K   out of 431K words

ai na kowa ne sai dai ina gudun abinda kaje ya dawo ga zaman su a wurina a matsayin su na diyan kishiya na kishiyar kuma irin matar ka da bayarda da Allah tayi ba.
Cikin tsigar rarashi ya soma magana tana fadin kece hope dina yanzu kan yaran nan don nasan zasu samu kula yadda ya kamata a gurin ki.
Idan kin rike min su da zuciya daya Allah zai baki lada akan riko da kikai masu din darajan ki kuma agun yaran zai karu ne.
Nasan kina kokari akan iyalina khadija ina son ki kara duk da kalubalin da zaki samu duk da haka ina son ki daure ki rike min su amana.
Ni dai tunda ya fara magana ban yi magana ba sai sauraren shi nake yi na rasa may zance mai don yadda nake ji din a lokacin.
Wani nayi ya dauko ya kara dorawa a kaina har yaushe nakai munzalin daukan wanan nauyin ya dora min kuma akaina.
Shirun da nayi sai naji ya rungumoni ta baya ya zauna dab da ni ya kare matse ni a jikin shi da alama hakan yana rage mashi itin radadin da yake ji a zuciyar shi a lokacin.
Can dana ji shirun yai yawa na daure nace dashi ga abinci can na hada ma a dinning cikin karfin hali ya mike zuwa wajen abincin ya dan taba yace ya koshi.
Har na fita na barshi baida walwala a tare dashi nima dai haka nake sai dai na dan dake nabar abin a raina ne kawai in ga iya gudun zancen kafin in maganta kada in yi saurin fasa cikina yai min wani fassara na daban.
Don halin maza sai su laifi nasu ne amma sai su so su dulmiya mace a cikin shi su barta karshe da laifi.
Wanan tunanen ne yazo min na nuna mai kamar ba komai a raina kan maganan da mukayi din kafin in samu mafitawa kaina.
Har na mike zan wuce yace baki ce komai ba ga zancen yaran danayi maki dan murmushin yake na kakaro a fuskana nace
Allah ya taya mu duban su ai da na kowa ne ba a san mai kama wani ba cikin mu dasu nan gaba daga haka na juya na fita.
Daki na koma na kira maryam tazo da magana a gidan mu da safe tace zata idan ta fito school tace may ke faruwa ne dan fara fada min dai.
Nace sai dai idan kin zo din mayi maganan zai fi na kashe wayan falo na koma don kada damuwa ya isheni a daki ni kadai a ciki.
Ina zama Altine na fadin ita bata san yadda zata bawa Sadiya abinci ba ta karba nace ta miko min yarinyar in bata tana bani na fara gyara kan yarinyar yadda abincin zai zaunu mata da kyau bai dawo ba na fara bata tana karba.
Ina cikin bata ya shigo dakin cikin shirin barcin shi yana kallon yadda na ke ba yarinyar abinci tana hadiya ya dade a kan mu yana kallon mu kafin yai muna saida safe ya fita.
Zaune nake da maryam a dakina na gama fada mata yadda mukayi dashi tace cabdi jam akwai magana sosai a wurin nan.
Khadija ina zaki iya rika yaran wanan matar yadda yake nufi wani abu yaje can ya samay su ace kece kikai masu sheri don suna diyan kishiyan ki.
Shi kan shi uban ba yarda zaiyi ba idan kin masu wani abinda bai gamsheshi ba duk kokarin da kikeyi rana daya sai ya goge.
A mararaice nace maryam abinda nake tunane ke nan nima wallahi tace idan gaskiya ne don may ba zai kaisu gurin hajiyar shi ba ?
Nace maryam ni ban iya furta mai komai ba har ya kare naganar shi don ni abin ya daure min kai muna maganan sai ga momy ta shigo dakin.
Ganin mu shiru yasa zata juya muna hada baki gurin fadin momy shigo mana ai ba wani magana mukeyi ba.
Tana zama nace momy dama akan zancen yaran nan ne na buzuwa sai nake fada mata zancen da mukayi da AA din .
Katseni tayi tana fadin ai nasan ba zai fara ya dumfari hajiya da yaran nan ba tun jiya maganan da muke ke nan da ita karshe ma ta fada ma Alhaji ya datse zancen da ba a gidan shi ba.
Hakkuri zakiyi don inda tanice wallahi zan iya kama yaran nan may ye a cikin rika su din ai duk yiwa kai ne amma matsalan shine Alhaji.
Karshe dai ba mafita momy tace in bishi a sannu tunda yace zai samu wace zata kula mashi da yaran a gidan sai in daure in kama mashi na dan lokaci a gani.
Satin dana koma schools a satin momy ta barmu ta koma kamar yadda mijin ta ya umurce su data dawo gida ga babban sallah daya gabato saura yan kwanaki ayi sallah a lokacin.
Ban sa rai cewa zamu kaduna sallah ba shiyasa banyi wani yunkurin zuwa ba na dawo daga school ne na samu bakuwa a gidan.
Suna zaune a falo tare dasu Altine na shigo muka gaisa nadan dube ta cikin rashin gane ta ko daga ina take Altine ce tace min ai itace matar da zata kula dasu Ihisan itama yar uwar su daga can kaduna tazo.
Dan kallon ta na karayi ina mata sannu da zuwa ta amsa min tare da cewa mun samay ku lafiya ?
Nace lafiya kalau da fatan zamu samu kulawan ki yadda ya kamata tace insha Allahu zata kwatanta.
Sai yamma ya shigo gidan bayan ya dan huta ya fito kafin magariba ya shigo part din yana fadin Altine bazawarin ki ya bugo min waya wai na dauke mai bazawara shi.
Dariya tayi tace ai da ina dashi ba zaka rike ni a nan ba sun gama ba an su ya shigo dakin ya samay yace kin shigo ina wanka.
Nace eh naje in gaida kaine da dawowa yace ya gidan lafiya muke na bashi amsa yace kin ga matar da momy ta samo muna ko ita ma dai yar uwar mu ce kamar Altine sai dai ita a kauye take zaune mijin ta ya rasu ne a baya ta aurar da diyan ta.
Kinga ba yarinya bace itama don Allah ki daure kuyi zaman mutunci da ita kikuma sa ido ga irin kulawan da take ba yaran nan a gidan nan.
Yanzu a ina zata zauna sai lokacin na sauke ajiyan zuciya nace mai sai mu zauna a nan ba na dan lokaci ba ne har uwarsu ta dawo bai ban amsa ba ya fita.
Yana fita nace na shiga uku ni kan a gidan nan baka gama wanan ba ka fada a cikin wanan waini ko wace mace haka take rayuwa irin nawa ne a gidan ta.
Matar mai suna Shatu bata da yawan hayaniya sai dai kamar tana da zafin rai da yake ni ba zama nake ba ban san wani hali nata na boye ba.
Zaune muke a falo maryam ta sayo min abinda zamuyi amfani dashi na sallan ita da Altine suka fita zuwa kasuwan don ban yarda naje kasuwa ba banyi arba,in ba.
Laraba ce take kokarin kwashe kayan ta dauki kwandon tumatir take fadin shatu ta dan kama mata.
Ta cewa laraba ita ba aikin girki aka dauko ta tayi ba gidan don haka ta fitar da ita a cikin zancen aikin su a gidan nan.
Dukkan mu kallon mamaki mukai mata daga can laraba dake fitowa tace amma idan an girka kina ci ko ?
Dakatar dasu nayi da zancen nace haba mama Shatu bai kamata kuna haka ba da girman ku Laraba ki rage sai ki diba zuwa kitchen din.
Tun wanan dole na mayar da hankali ga takon shatu a gidan don yadda take nuna hasala da sauri zata iya cutawa yaran da take kulawa dasu.
Da safe ina shiri nake jin kukan ihisan har dakina na fito da sauri da ga daki ina tambayan may ya samay ta take fadin wai daga shirya tane take wanan kukan haka.
Dan tsayawa nayi ina nazarin yarinyar na kama hannun ta zuwa daki ina tambayan ta take fada min dukan ta tayi da zatai mata wanka yanzun kuma ta kara dukan ta din.
Dan shiru nayi a raina nace matsala ga wanan ga wancan yaya zan fito ma wanan matar don dai a haife ta haife ni kuma gata da rashin fahinta .
Sai da muka dawo da yamma ranan muka rufe don sallah da za a yi a gobe shi kuma zai tafi sallah gida nace mama Shatu dama ina son magana dake don Allah dai kinga yaran nan kanana ne sosai duka bai dace dasu ba a yanzu.
Don Ihisan ta fada min dazun kina dukan ta don Allah mama a bar dukan nan inda hali a tsawata mata dai yafi duka sauki ga yaro.
Yar nan kina tuhuma nane komay ko wani sheri kuma ake son a laka min don hadin ga wanan magana don nasan fada maki wanan zancen akayi.
Nan dai na lurar da ita na kota gane ban sani ba sai dai ina tune a raina idan ma nice ke rikon yaran haka dan abu kadan a kansu zai iya jawo min matsala tsakani da maigidan ke nan.
Washe gari ya tafi ya barmu a Abuja a nan zamuyi sallah mu tunda ba school a gida nake ban fita zuwa ko ina sai dai zaman su Altine ya debe min kewa a gidan sosai.
Sai shirin hada abinci muke yi muna kitchen gaba dayan mu in ka debe shatu dake daki gurin Sadiya da tai kashi tana canza mata pampers.
Sallama kayi aka shigo gidan laraba ce ta leka don ganin mai sallama sai gata ta dawo da sauri tana fadin uwar dakina yau fa muna da baki a gidan.
Su waye na tambaya tace wanan kawar Nafisa din nance tazo tana falo a zaune hannu na na dauraye na fita ina zuwa naga wanan Sabuwa din ne tazo ashe.
Mun gaisa take fadin gurin yara tazo ta duba nace to bari a kawo su ku gaisa na shiga nace Shatu ta fito da yaran.
Tana ganin su tace Ihisan ke ce kika ramay haka kika lalace kamar bake ba daga inda nake zaune ina kallon ta ina dan karkada kafa na.
Wanan ai basai an fada ba yaran nan a cikin kunci hajiya duban yaran ki kazo ko kin zo ne ki fada muna magana a kan yaran nan.
Tace gaskiya nake fada kin san dai yaran nan sun lalace ba haka uwarsu ta barsu ba nace da baku son su lalace ai sai ku tsaya ku duba abin ku ko.
Ta mike tana wani tafiys tare da fadin ita zata tafi dama Nafisa ne tace ta shigo ta duba mata yaran taga lafiyan su.
Sai ki je ki fada mata abinda idon ki ya ganan maki a kan yaran nace mama Shatu shaga da yaran ciki Allah ya baki ladan riko .
Taja tsuki ta fita tana zage zage har kofa na fita na kira security na nuna masu ita kan kada su kara barin ta shigo muna gida don Allah don ba alheri ke kawo ta gidan ba ta buga motar ta ta fita.
Altine tace mai yasa ba a kira ta ba ta yi daidai da yar iska nace ko makiyin Allah yasan yaran nan suna samun kulawa a gidan nan yanzu.
Aikin mu muka karasa maryam ta shigo min da dinkunan na fitar ma kowa nasa na bashi ranan sallah mukayi abin ci da sha iya mu sai security a gidan.
Zaune muke muna hira sai faman ciye ciye suke yi duk abinda ran mutum ke so ba wani sha maki ga kowa dama kuma haka muke ban saka masu ido ga abinda sukeyi.
Yana can bayan sun fito sallah wayan shi yai kara ya dauka ba sallama sai masifa data fara mai ya hada kai dani ana zaluntar diyanta duk yara sun lalace sun fige.
Kashe wayan yayi yana kashewa ya kirani yana tambayan wacece tazo gidan nan bayan shi nace kawar Nafisa ce .
Ina fadin haka ya hauni da fada inda yake shiga ba nan yake fita ba nayi shiru ina sauraren shi ba tare da nayi magana ba na kashe wayan.
Komay ya tuna kuma sai gashi ya sake kira ban daga ba har kiran ya katse yai kira uku ban dauka ba ina zaune ina ba Sadiya abinci ina gani naki dagawa.
Na gama na dauki yarana muka koma daki ban dade da shiga ba sau ga Altine ta shigo tana mika min waya tare da fadin mijin ki yace yana kiran layin ki baki daga ba.
Ta miko min wayan na karba ina karba yana fadin ina kike waya na ringing baki daga ba nace ina zaune a daki ne yace ok.
Kin gane daga yau ban son a kara barin kowa ya shigo min gida da sunan duban yaran nan ban dai tanka mai ba kawai ina sauraren shi.
Naji yace ana magana sai ki kyale mutu kamar bakyajin shi nakai iya wuya dashi nace wanan ba matsala na bane kuma na kashe wayan.
A gaban hajiyan shi yake suna gaisawa tace ma dama ina son ganin ka don may zaka hada yar mutane tana fama da kanta ka dauko wani wahala ka dora mata.
Hajiya banda yadda zanyi ne shiyasa na barwa deedar su a gida amma kasan itama tana da nata diyan ko so kake a tauye ta don kawai tana da hakkuri ?
Nan dai yayi mata bayanin an dauko mai kula da yaran Shatu nacan gurin su tana duba su ai tace duk da haka ai a karkashin ta suke su duka.
Kada kace zaka sa ido da son diya arai har ka kasa ganin kyautatawan da yarinyar nan ke maka
Yace hajiya don haka ne na dauko wace zata kula dasu na musanman a gidan
Tace ka dai ji hukuncin da Alhaji ya yanke akan yaran nan don haka kasa yadda zaka bi da gidan ka a samu zaman lafiya.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/6/21, 8:09 AM - Xxxxx: Zaune dai nake ina washe baki a cikin su amma ta ciki na ciki ina tunanen wayan mu dashi ga sadiya kamar mai wayau idan bani ba bata yarda wani yai mata wani abin.
Ni har na fara tsorata da lamarinta a raina yadda yarinyar tasan dimin jikina da hannu na ko guri nake idan ana gurin da ita zata fara kokarin juya kanta gare ni.
Sai na shiga tsarguwa a raina kodai maganan Nafisa gaskiya ne ita ya tace aka sauya mata to ta yaya na kawar da wanan jahilcin a raina irin nata.
Ga dai su yan biyu zakace bani na haife su ba don kyau da kwarjin yara kara fita yake a idon mutane kulan da suke samu ya saka suna komawa kamar diyan larabawa dasu don shegen kyau.
Fari dai nasan ba nawa bane kadai haka girman jiki sun dauko shi duka biyu don AA da yan uwan shi jajir suke suma haka hajitan su take.
Duk da manyata ya kama ta amma haka bai sa farin ta ya gushe ba sai dai idan ya tsaya a cikin mu ne farin shi ke gushewa.
Tunda nayi sallah ban fito ba don na fara sallah ina dakina zaune anan Altine ta samay ni mun dan taba hira da Altine din ta sako zancen Nafisa ina kaucewa.
Don ni yanzu ban ma son zancen a tare dani da naji ta matsa ne nace Altine ni fa gara ta dawo ta dubi yaran ta yafi mun don ko ban samu matsala akan komai da magidan nan ba akan yaran nan nasan zamu samu saboda yadda yake ganin bamu basu kulawa da ya dace dasu.
Tace kafin in kai ayya kai yana soma shi kulan da kike basu ko yaran ki kin tsaya kin basu shi yaushe shi ko uwar yaran da take nan ta kula dasu hakane.
Ke harfa laifin ki nake gani akan haka wallahi yaushe zan tsaya kula wasu diyan kishiya in bar nawa can su girma suce nice makiyar su nina kore masu uwa gida.
Nan nake fada mata laifina da ya gani tace amma mijin kan buzuwan wanan ta gama dashi ta ko ina wallahi.
Ke nifa tun kan yaran can biyu da bai damu dasu ba kamar ba diyan shi ba wallahi idan kana da matsala da uwar su yaran ba naka bane da zai dinga kin kula su yadda ya dace.
Laraba ce ta shigo muka maida kallon mu gare ta tana dauke da Alamin a jikinta tace uwar dakina yau fa kamar yaron nan baijin dadin jikin shi.
Nace mama nima na kula da hakan tunda yamma yana kuka na bashi nono yaki kamawa sai kuka yakeyi cshine kikaga na goya shi yayi barci dazun.
Tun dare baiyi ba mu kaishi asibiti a duba shi Altine ta fada nace yanzu kan ai dare yayi ina zamu fita da wanan sanyin haka ?
Laraba tace ko in daka albasa mu shafe mai jiki kila mura ke damun shi zai

124 / 144

Chapters