MIJIN BUZUWA complete Hausa Novels.txt

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   122 / 144

363K to 366K   out of 431K words

asiri baya saurin kamata gaskiya ga kuma tana da rikon addinin ta da wuya a aika mata ya samay ta gaskiya.
Sai dai idan munce zamu mata aiki kema akwai aiki a gaban ki gaskiya don sai kin bar komai daya shafi naki addinin zamu samu aiki ya kai gare ta.
Kallon juna sukayi da Sabuwa sai sabuwa ta kada mata kai Nafisa ta juya gurin boka tana fadin boka na amince da ko may ne zaka fada min zanyi.
Don na tsani wanan yarinyar naki jinin in bude ido in ganta a gidan nan wallahi ya ki kwantar da hankalin ki tunda kin zo nan.
Zakiga aiki maikyau sosai tace boka ko nawane indai bukata zai biya zan baka sabuwa tace ko akashe muna ita har yaran nata ko kuma a haukata ta tabi daji a manta da ita gaba daya.
Boka yace irin su na fada maki ba,a zuwa masu yadda kuke nufi din nan domin Aljanin da zamu tura ba zai samu aiwatar da aikin shi ba sai ya samu bata cikin ibada.
Ko bata sallah gata nan nagani tana yawan ambatan abin bautar ku koda yaushe a bakin ta gatanan anan gurin ina kallonta yace.
Ya mika mata wani ruwa a dan wani roba fari na yought yana fadi wanan kiyi kokari yau din nan ki yayafa ida kika san zata bi daga ita har mijin idan kin samu washe gari sun taka.
Yayi wani iri da hannuwan shi alaman mun raba hanya ke nan da AA yace ba sauran zaman lafiya a gare su karshe auren zai watse babu wanda zai tuhumay ki.
Sai wanan ya mika mata wani dan kuli yace zaki gina rami daidai bayan dakin ta ki binne a cikin ramin ki kawo babban dutse ki taushe gurin zata dinga jin gidan gaba daya ya fita ranta ga baki daya sai ta barshi ba shiri.
Wanan kuma a inda ake girki zaki saka da zaran zafin wuta yana dukan shi bata da kwanciyan hankali a zuciyanta tsana da ganin bakin mijin zata ji.
Idan kinyi haka yau ba tare da samun akasiba ina mai tabbatar maki bata kai wata daya a gidan nan komai tsananin ibadan ta.
Boka mun gode zakaji dasin aiki damu sosai nan gaba dama ai rashin sanin wurine yasa baka ganmu ba da tuni munzo ai.
Sai dai ya matsalan mijin nata ne kai ya kada yace wanan gaskiya samun shi shima yanzu ba abune mai sauki gare mu ba don uwar shi tsaye take akan dan ta.
Kai har uban ma yana tsaye sosai akan diyan shi amma da zaki iya samo muna dan kwalin kan uwar shi da kasan kafanta akwai aikin da zan hada maki zai ci sosai kuwa.
Sabuwa tace boka mun gode in Allah yaso zakaji nan bada dadewa Nafisa ta balle jakka ta fito da kudi masu yawa don jin dadin abinda yai masu alkawari ta bashi tare da fadin sai sun juyo.
Sai lokacin da suka fitone suka dubi lokaci hankalin Nafisa ya dan tashi don bata san gurin yana da nisa haka ba da ta dauko yanyala da yar Aljannan ta sun taho ta raya a ranta don haka take kiran sadiya dashi.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 10:23 AM - Xxxxx: Garin Allah ya waye hankalin kowa a gidan a tashe yake tun shida da wani abu ya bargidan zuwa asibiti ya dubasu inda ya samu jikin yarinyar ya danyi sauki.
Za a kara sa mata wani jinin na biyu ya dan dade tsaye yana kallon ta yana mai jin wani iri har cikin ranshi sosai.
Yusuf ne ya iso ya samay shi a asibitin inda ya dan duba yarinyar kafin su fita zuwa police station su sanar da bacewan Nafisa din.
Dawowan su asibitin yayi daidai da isowa tare da Altine da Fatiha munzo masu da abin karyawa ida nake jan motar da aka ban gift gidan SJJ .
Tsayawa yayi da mamaki yana kallon mu yadda nake tuka motar cikin gwanan cewa da iya tukin bai taba kawowa a ranshi ina driveing ba da farko don ban taba nuna mashi iyawana ba.
Sai da muka firfito daga motar na rufe muka nufo inda suke tsaye a cikin jimamay tare da gaida su inda muke hada baki gurin tambayan anko gano inda nafisa din take.
Yusuf ne ya bamu amsa cewa wallahi har yanzun shiru ba a ji komai ba gamay da ita har na fara tafiya nace wai ba za a gwada tambayan wanan matar madan aji ko tasan idan taje .
AA yace wanan dabaran bai fado min ba sam wallahi don shawara ne babba yace ma Yusuf suje su tambaye tana cikin asibitin ai.
Suka nufi dakin da madam din take kwance sun fara gaida ita da tambayan ya jikin tace da sauki sosai sai tayi shiru.
Yusuf yace munzo mu tambaye ki ne ko kina da masaniyar inda Nafisa ta shiga tun jiya da safe da ta fita ba a ganta ba har wanan lokacin.
Tace cikin farga tun jiya fa yace kwarai sai tayi dan shiru ido suka kafe ta dashi yadda take nazarin wani abu a danta ke tunane a ranta sai can tace .
A bunkici Sabuwa idan basu tare don jiya tazo nan da safe dubani tace suna sauri zasu tafi wani guri tare da Sabuwa bata tsaya ba tafita duk ko da nuna matan danayi yin haka kuskure na.
Wacece Sabuwa AA ya katse madam da ta fara zuba cikin tsana tace wata aminiyar tane datayi sabuwa tana zama uguwar Nyanya ne.
Ki muna kwantace idan kina da layin ta kuma ki bamu cikin rawan jiki tace ina da layin ta sosai kuwa bari in duba maku mu gani.
Ta kira masu layin yasa a waya tare da danna ma layin kira sai dai amsa dayane kamar na wayan Nafisa din dai har itama.
Kallon juna sukayi da Yusuf yace itama not rechable ke nan wani abu dai yana faruwa dasu duk yadda akayi.
Kara kwatacen gidan Sabuwa tayi masu suka juya suka wuce batare da mata godiya ba sai AA ne da ya juyo yace idan a nason karin bayani zamu kara dawowa gurin ki kuma.
Wani irin takaici da bakin ciki mai tatare da Nadama ne ya rufe madam a lokaci daya har kwallan takaici suka zubo mata tana kiyas ta wani a cikin ranta.
Mun duba yarinyar shigowan likita yasa bamu wani dade a gurin ba ko da muka fito daga dakin motar su AA baya gurin nake cewa da su Altine ai anan ne madam din take ko ?
Fatiya tace eh don ranan sun zo da dare sun gaida ita da yar uwarta muka sa kai zuwa dakin don mu dubata.
Tana zaune da ganin idanuwan ta tayi kuka lokacin mukai mata sallama tare da gaida ita da mata ya jikin tace da sauki tana mamaki a ranta mai ya kawo mu asibitin wanan lokacin.
Nace ya kafan da sauki dai ko tace da sauki ta gode na bude jakka na na ciro mata kudi na bata dubu goma sai ta fashe da kuka.
Fatiya ce tace ba kuka zakiyi ba kiyi tawakkali ga Allah da kaddaran da ya jarabce ki dashi ai tace dole ne in kuka yar nan kuka dole ne gare ni ai.
Wanan yar tai min abinda ban zata ba gashi duk da abinda nake mata tazo dubani da zuciya daya har da alherin ta gare ni haka.
Ba komai nace da zuciya daya nake tare dakowan ku ni na juya tace yanzu maigidan ku ya barnan yana fada min Nafisa ta bata tun jiya ba a san ida take ba.
Ni dai jiya tazo nan a gurguje to ba abin alheri bane inda zasu koda bata fada min ba nasan wani kawai zasu da sabuwa don yanzu itace sabuwar amiyar ta.
May yuyuwa basu kasan nan ko kuma wani abu ya samay su a hanyar zuwa bamu dai fatan hakan amma ba a raba daya biyu daga cikin wanan dai.
Fatiha tace kauye kuma suka tafi yin may tabar yarinyar ta jinjira a gida zata tafi kauye ta barta yar a gida.
Madam tace ke dai Allah ya yafe muna kawai ni yanzu nayi na dama wanan karayar yaza min kamar ishara ne a kan duniya.
Idan mutum bai nufe ka da share ba kace kai zaka nufa tun a nan duniya Allah ke nuna maka abinka yanzu ba sai anje can ba.
Yanzu kudin nan da yariyar nan ta bani ya kara sa rayuwana a cikin nadama sosai wallahi muna binki da sheri kina saka muna da alheri.
Murmushi nayi na juya na fara tafiya Altine ta biyo ni Fatiha muka tsaya jira a cikin mota ta fito muka dauki hanyar gida.
Cikin mu babu wanda ya iya magana tunda muka fara tafiya har tsawon wani lokaci kafin Altine ta kawar da shirun da fadin ita wanan matar taga aya ke nan ga rayuwan ta ?
Fatiha tace aini imanin su ya cika min zuciya mutane babu imani a tare dasu yanzu idan wani abu mumuna ya faru dasu a hanyar mai zasu fadawa Allah kan hakan.
Har suka gama maganan su ban samu bakin magana ba ni kadai nasan abinda nake kiyastawa a raina wanda godiya nake wa Allah da bai min wanan halin na yawon bin bokaye da malamai ba wanda karshen shi nadama ne ke tare da mai wanan halin.
A A kan zuwa ya samu gidan sabuwa a rufe ya kara tayar mai da hankali inda ya tambayi makwabta sukace tun jiya rabon su da ganin ta suma a garin.
Sun kuma tabbatar masu sunga fitan su tare da nafisa din a yadda akai masu kwantacen ta sukace tabbas tare suka fita daga gidan.
Bai shigo ba sai karfe hudu na yamma ya shigo gidan a gajiye don yai wanka part dina ya fara shiga ko da wani labarin ya sani.
Yadda ya shigo na kalle shi ina falo zaune ina shayar da yara nono ya shigo muna gaida shi muka fara tare da tambayan shi anganta da jikin yarinyar.
Yace har yanzu dai ba wani labarin su sai dai makwantan wanan dayan matan sun sheda masu sun gansu a safiyan jiya tare wai zasu tafi wani kauye ne yanzu dai an bamu layin wata mu kirata muji ko tasan inda sukaje.
Wayan ta yana ringin bata dauki waya ba har yanzu nace oh wanan abin tashin hankalin da mai yai kama haka ne ?
Zaki fita zuwa nesa ai sai ki fada wa mutane don gudun irin haka ko akalla dai an san inda ka tafi ai.
Altine tace ai yanzu wanan yarinyar ne abin tausayi wallahi an rabata da nono da karfi da yaji haka gashi bata isa yaye ba ma.
Wallahi nima abinda nake tunane ke nan nace Allah yasa dai duk inda take suna lafiya shine fatan mu dai yanzu.
Dariya mai kama da yake yayi yana dagawa daga inda yake zaune kusa dani yace bari indan watsa ma jikina ruwa inji dadi.
Nace abinci fa ina ganin ko karyawa bakayi ba tunda ka fita gidan nan yace lemo nasha dazun da naji yunwa barin watsa ruwan inci abinci dai ko zanji dama ya mike ya fice daga part din.
Wanan matar akwai tsinanna wallahi, ji yadda ta saka bawan Allah nan cikin wani hali tsakanin jiya da yau din nan har ya fada .
Nace dole hankalin shi ya tashi ko don wanan yarinyar karama dake kwance asibiti cikin wani hali tace dama ba son yarinyar take yi ba ai kin ga idan ta mutu an huta ai.
Amma ke khadija ni sai ina gani kamar gudu tayi yadda suke ma maza idan sun gama dashi sai dai kuma zata gudu ta bar yan uwanta da diyan ta haka ?
Don idan zasu gudu ai shammatar namiji suke yi sai sun gama yaye komai na mutum sai su gudu su barshi daga baya.
Nace Allah dai yasa duk inda take tana lafiya sai Altine tace kai wanan baki san takaici ba wallahi banga abin tausayi wurin wanan matar bani.

NAFISA
Sun kamo hanya da ga yamma yayi masu inda suka dauki mota shata zuwa Abuja tun basu kai ko ina ba dare yayi masu tafiya driver ke yi kamar ai aike shi.
Sai kwasan su yake da uban gudu a daji tun suna firan bokan da sukaje gurin shi har suka gaji sukai shiru da bakin su driver na ta faman tukin mota.
Sun dan wuce kaduna kadan suka hango haske a tsakiyan titi driver su ne ya fara fadin yaushe aka fara checking wurin nan sai ya rage gudu bai kai ga karasawa ba ya gane yan fashine a hanya.
Salatin da ya saka ne ya fargar dasu abinda ke faruwa a titin yan fashin sun tare wani mota suna operiton sai suka hango motar su nafisa tafe.
Driver yayi saurin yin kwana garin juyawa sai motar tashi ta leka da sauri yace dasu kowa ya ta kanshi ya fita ya zura daji da gudu suka mara mai baya suma a guje cikin dajin .
Nan yan fashin suka farwa motar da suka bari da bincike suka kwashe duk abinda suka sama a cikin motar sukai gaba suko wurin gudu sin fadi sun jirji ciwo a jikin da kyat suka samu wani dan kauyen da suka bari a baya suka kwana a tsaye don mutanen garin sun shige gidajen su ko.
Sai washe gari mutane suka fito suka samay su a gurin ga mutanen da yan Fashin suka tare hanya motaci an taru a gurin wasu an kashe wasu kuma sun jirgita.
Basu suka samu isa wurin motar su ba sai da wani ya taimake su suna zuwa suka samu an masu dadaya da kaya duk an watsar da komai a daji.
Tsananin firgicin da ta kwana ciki yasa ta fita yacin ta ga gurin gudu ta gwauce a kafanta haka dai suka samu aka taimaka masu aka kwaso su garin kaduna akai dan bincike basu bar kaduna sai uku na rana koda suka iso Abuja lokacin yamma yayi sosai gidan Sabuwa suka fara zuwa.
Suka kitsa abinda Nafisa din zata fada a gida kafin ta wuce zuwa gida daidai AA ya fito yana magana da yusuf da security din gidan mota ya tsaya da ita.
Kallon mamaki suka fara mata yadda ta koma gaba daya ga jikin ta ko ina ya guje tana tangadi tun da ta dumfaro gidan gaban ta ke faduwa.
Ganin su cirko cirko a kofan gidan bai hanata kokarin shigewa ciki ba wani irin tsawa ya daga mata daga inda take sai da ta kadu.
Yace ke tsaya nan ina kika fito haka zaki shiga min gida ki koma can inda kika fito yawon tanbadan ki kada ki fara shiga min gida.
Yusuf yace ka barta ta karaso muji in da ta shiga aiko tace cikin dakewa kai wani irin mara tausayi ne Samad mutum ya dawo a wani irin yanayi baka bincike ni zaka fara min fada.
Yace na fada maki kada ki soma shiga min gida ya kalli security din yana fadin kada ku bari wanan matar ta shiga min gida daga yau.
Security suka ce angama oga yace yayi bai tsaya ba ya shiga mota suka wuce zuwa asibiti ganin ya wuce ta doshi gidan .
Security din suka taso mata nan gardama ya kaure a tsakanin su a gurin muna ciki laraba tazo tana fada muna abinda ke faru.
Muna fitowa falo Fatiya yadda ta gan mu ta zabura tana fadin lafiya dai ko Altine tace yar uwarkice akace ta dawo tana bakin get an hanata shiga gidan.
Gaba dayan mu muka fita zuwa waje a yadda muka samay ta a gurin munyi mamaki duk bata da dadin gani mun karasa ina tambayan security din suka ce umarni ne daga maigidan ya basu.
Jin haka nayi mata wani kallo nace yanzu sai kiyi hakkuri ki nemi maigidan ya basu izzini ki shiga nan muka bar su Fatiha a gurin ta muka juta zuwa ciki.
Fatiha ce ke tambayan ta ina ta shiga hankalin mutane ya baci ga rashin ganin ta tun safiyan jiya ga yarta tun jiyan bayan fitanta tana asibiti bata da lafiya.
Tace wace yar tawa ciki suka ce Sadiya yar jaririysn ta sai tayi wani iri a fuskanta na ko in kula da hakan tace kin san iya hankalin da aka shiga a gidan nan na batar ki kuwa ?
Sun dauki lokaci wurin har lokacin bai dawo ba nan dai cikin hikima suka lalashe ta take fada masu abinda ya faru da su a daji har suka kwana tace wayan ta da jakkarta duk yan Fashin sun kwashe acan haka ta dawo gidan.
Ga kafarta da tayi targade yana mata ciwo sosai don yayi tsami zuwa tanzu tambayan da fatiha ta jefo mata ya bata haushi.
Addah gurin bin bokayen da kika saba kukaje ke nan kuka hadu da wanan kadaran sai yaushe zaki ma kanki fada akan wanan abinda kike aikatawa ne.
Ke ko abinda ya samu matar nan a gidan nan ranan bai isheki kiwa kanki fada

122 / 144

Chapters