Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MIJIN Buzuwa Complete Complete Hausa Novel by Nil

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   102 / 144

303K to 306K   out of 431K words

ba bacin rayukan mu ba a can.
Ciki ciki nai magana ina fadin mutum dai ya rika shuka gaskiya a lamarin sa shine kyau yace may ne may kika ce nace ai kajini.
Murmushi naji yayi nace ai dama kaji may ye na bukatan in maimaita kuma kin dai ji na fada maki tun anan ko in nuna maki kala na acan.
Nace ko yanzu ai nasan kalan ka don ka zama sabo da kaza bai hana yankata ina jiye min ranan da nima zaka iya korana da abinda zan haifa dakai a gidan ka.
Tunanen ki ke nan dama dako kinyi kuskure don ba haka nake ba hukunci nakan yanke dai abinda mutum yayi ne.
Ba mamaki idan halin ki ya sauya in yake maki makamancin hukunci da kike ganin banyi daidai ba kansa.
Shiru nayi ina nazarin maganan har lokacin da naji ya rungumoni zuwa jikin shi yana fadin ku dai mata ba a gane gaban ku na gaskiya ko ?
Washe gari banyi wani barcin safe isashe ba na shirya muka fita mun dan taba sayaya muka dawo muka kara shiri kusan maryam ne ta hada min komai da zan bukata acan idan mun tafi.
Duk damuwan rabuwa da yaran da zanyi yana cin raina suko ba abinda ya damay su sai ma murna zasu kaduna da sukeyi.
Karfe sha biyu da rabi muka bar garin Abuja zuwa kaduna baysn yasa an rufe gidan ya bada umurnin kada a bude ma kowa gidan idan bashi ya dawo ba.
Yai masu ihisani muka tafi bamufi minti ashirin da dagawa ba Nafisa dasu madam suka iso gidan tare da wasu yan yaren su dattije da wasu da madam taiwa magana su zo aba shi hakkuri abindai a wullaknace.
Nan sojan dake gadin kofan yai masu nuni da su koma da hannu kada su karaso kofan sai da kyat suka samu ya saurare su yace masu gidan sunyi tafiya.
Tace ina suka je cikin tshin hankali take tambayan shi gashi ko kayan sakawan yaranta bata dauka ba suka tafi.
Yace shima bai sani ba amma da gani zasu dade inda suka tafi din ya kuma ce suyi maza subar kofan kafin ranshi ya baci dole suka bar kofan gidan.
Tunda suka shigo motsa madam ke fadin da sake gaskiya don sun damay ta da hayaniya a gidan tace nafisa abinda nake fada maki ke nan kullun baki ganewa.
Na fada maki ki bi alamarin nan a sannu tunda kikaga yarinyar nan ta shigo gidan nan da karfin ta ta shigo kikaga kinyi asiri bai yi wani tasiri akan ta ba har wanan lokaacin to ki bita a sannu.
Yanzu gashi kinjawa kan ki komawa baya a gaban idon ta ya nuna mata ke ba kowa bace a gurin ta wanan abin damay yai kama ?
Duk rashin hakkurin ke ne yaja muna wanan koma bayan yanzu ina kike son in kaiku kuda yawa hakan nan a gida na ?
Bakin magana Nafisa bata samu ba a lokacin abin mamaki da alajabi yake bata wai yau itane ake tagaririya da ita ana mata wanan wullakancin haka a gidan samad.
Ita ce samad ya wullakanta a kan wata abin ita har yanzu kamar a mafalki take ganin sa a idon ta ba wai ta yarda samad ne yai mata haka ba.
Ta tuno ko a indiya kudin da ta kashe zai iya sai mata gida da abin hawa a garin Abuja su zauna ita da ya uwanta ba sai sin rabo a gidan wata ba ana masu wullakancin akan abinda tafi karfi shi a yan shekarun da suka shude kai bama shekuru ba a jiya jiyan nan ma.
Dole ta fidda da kudi da madam din ta bukata masu yawa wanda zasuyi amfani dashi domin sallah da ake sa ran za a tashi dashi gobe.
Mun isa kaduna a wahalce duk dauriyan da nake yi sai da ya gane ina cikin wani hali sai ga amai da ya biyo baya da kyat naga mun kai garin kaduna din.
Yau ma kaman wancam karon a jirkice na iso garin muna shiga na nufi sama amai nayi ta shega yasa wai dole in kara azumin dake baki na nace naji yasa laraba ta hado min tea kafin ys shigo na dan kai rabin bayi na koma na lafe kamar nasha tea din sai barcin wahala da ya dauke ni.
Bayan nayi sallah na dade ina barci sai da aka kira sallah magariba na tashi nayi buda baki wanka nayi nazo nai sallah ban dade ba kuma na koma na kwanta.
Bani na samu kaina ba sai washe garin sallah da akai sanarwa da anga wata garuruwa daban daban na kasan nan dama wasu kasashen duniya
Ga kayan da muka zo dashi ba a bude ba don rashin lafiyan das nna iso gartin dashi dole na fito a cikinn karfin hali na bude kayan ya bawa kowa nasa tun da safe.
Abinda ke ban mamaki ya daure min kai shine lamarin anty fati ko wancen zuwan da nazo a haka matan nnan bata tako dakina dubs ni da jiki ba haka kuma batai min sannun kirki ba.
Hakane ma wanan karon tunda na shiga bata leko ni ba a dakin har zuwa lokacin da na fito ina bawa kowa abinda muka zo dashi garin.


ZAINAB IiDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: ZAINAB IDRIS MAKAWA
08036959275

Kitabbatar da hakkina a kan ki idan kin karanta baki biya ba kibar wace bata san darajan Allah da Annabisa da hakkin data dauka kada son zuciya ke ma yakai ki ga halaka alhaki bin maishi yake ta inda baiyi zato ba.
Ina kara jaddada wanan maganan don akwai ranan tambaya yana tafe kan mu ko yau ko gobe ko kuma yanzun da kike karanta hakkin da ba naki ba .
Musulumin baya so ma dan uwan sa abinda shi baya so akan sa ba shiyasa a kulun nake maku wanan tunin a matsayin ku na musulmai da suka isa dauka hakki akansu.
Na gama abinda nake na koma dakina na kwanta don har lokacin jikin ba ya gama warwale min bane waya nayi gida ina sheda ma daddyn mu mun sauka lafiya jiya mun iso bana jin dadin jikina ne ban samu kiran su ba daga nan kuma inda nake na kira ya Amina ina sheda mata halin da nake ciki.
To wai idan kin ce kin biya ya zama naki kina da ikon kiba wanda kike so amma ko da kin jahilci sharudan ciniki wanan a haka yazo don online novel ne mai shi tace ga ka,idan abinta dake mai tsoron Allah ce ai ba zaki biya ki saya ba sai ki barta da kayan ta tunda karatun novel dai ba ibada bane.
Muna cikin waya da ya Amina nake danji murya alaman fada a kasa da sauri na aje wayan ina saurare daga ina maganan ke fitowa nan na fahinci a falon kasa ne dai a cikin gidan kuma.
Jin abin bai kare ba yasa na sauko kasa don gane ma idona abin dake faruwa a gidan kuma da wanan safiyar sallah da kowa ke cikin fari ciki da barka da buda baki na wanan shekaran da Allah ya nuna muna lafiya wanda wasu Allah bai nufa suga shi ba.
Wasu sunga farkon shi amma Allah bai nufa suga karshen shi ubangiji ya gafartawa magabatan mu na kusa dana nesa idan namu yazo mucika da kyau da imani.
Kina ban dariya wai karfin hali barawo da sallama shi malamin da yace haka kin masa bayani ga yadda mukayi dake kafin ki saya akwai ka,ida a tsakanin online ne ba takarda bane da zaki dauka ki kaiwa wasu.
Yanzu dai idan kin nace da fitarwa alkalin mu Allah da ku don duk abinda akace abarwa Allah idan kana da hankali da imani kaiwa kanka hisabi tun nan cikin duniya.
Hakina na ban fara ba sai dana roki Allah akan hakan na fara a cikin baiwar sa na kuma samu a cikin iyawarsa yanzu zabi ya saura gare ki dake damasu biye maki ku halaka ku halaka zurian ku akan novel din da ba ibada bane.
Isowana yayi daidai da furcin shi yana fadin nawa na turo maki akan sallah nan dubu dari biyar nasa Yusuf ya kawo maki don ban san halin da tafiyan mu zaiyi ba acan .
Shine yanzu zaki tare ni da wanan maganan banzan wai ba a sai komai na aikin abincin sallah ba don baki san zamu zo nan sallah ba.
Idan ma banzo ba ai ina da iyayye da yan uwa da zaki ba abincin sallah ke kanki ba don karki gani ga wani na tura maki kudi haka Fati ni na rasa gane may kike da kudi ne haka wai.
Ke ba a gani a jikin ki ba ba a gani ga diyan ki balle dan uwa kowa korafi yake da rowan ki ba wanda ke tare dake yake jin dadin ki saboda bakin halin ki na tsiya.
Tace idan ka bani ne don kasan abinda nake dashi kabar bani mana yace haka kika ce ko tace hakane mana tunda kabani kaba kowa na sani yanzu kan wanan magana danayi zaka aza min wanan tujaran haka.
Yace oh baki komai ba ke nan ko tayi shiru yace yau zaki gane baki da wayau baki san kalman da ya dace ki fadawa mutum ba komai ya fito bakin ki zaki iya fada ma mutum shi kai tsaye.
Wanan dalilin yasa baki taba ganin fuskana don a gaban kowa ba abin kunya bane gareki ki disga ni baki san komai ba sai bakin rai da hassada dake cin ki.
Don Allah dai ku bar wanan magana na fada daga inda nake tsaye nace indai don wanan kuke wanan abin kuyi hakkuri ga komai nan nazo dashi wanda na saya can a zatona acan zamuyi sallah da naga nan ne na ce mama ta kwaso muzo dashi nan ga baki daya don girman Allah dai kuyi hakkuri wanan maganan ya wuce.
Inda nake ya kalla ya nuna ni da hannu tare da fadin you see kinji abinda tace kinji ma kunnuwan ki kudin dana bata baiko kai wanda ke na turo maki kuyi hidima dashi ba nan.
Amma ji irin abinda ta sayawa yaran ki suka dawo dashi ke da kanki kike nuna min yanzu babu ko kunya wanda ke kin kasa yi masu hakan kuma ke kika haifi abinki fa.
Yaya don Allah kayi hakkuri kabar gurin nan idan ba ka kauce ba zancen baya karewa a tsakanin ku itakuma fadi take wanan munafuncin ni ban iya ba.
Wani sheri ne na kishiya mitum bai sani ba kuma yace idan munafunci ne yin haka ke kiyi mana a gani ai shima ribar zamane.
Kince Nafisa bata da kula bata son ki bata son diyan ki wanan kuma kin kirata da munafuka ke wace kala ce to a cikin ku yanzu.
Tace dama idan ba kaci min mutunci ba ai hankalin ka baya kwanciya yace idan magana akan gaskiyata ce cin mutunci naci maki din sai ki abinda zakiyi.
Kitchen na wuce na kyale su kayan da mukazo dashi nake tambayan laraba da take tsaye a cikin damuwa wajen kitchen din ta fito tana fadin gasu canbda aka shigo dasu aka aje su daga can.
Nufar kayan nayi don mu fitar a dora girki dasu nan dai muka shiga aiki da laraba ban san lokacin da suka gama suka watse ba.
Na fito naga Affan zaune a cikin damuwa daddy kuma yana wasa nace Affan ba zaku je ku shirya kubi abba masallaci ba ne ?
Yaron yace maman mu batai muna wanka na nace ku tashi muje kuyi wanka da sauri na wuce suka bini a baya zuwa dakina na gama masu nace su karbo kayan su in saka masu sai ga shi ya dawo yana fadin maman mu ta koro ni.
Mikewa nayi na nufi dakin da sallama a baki na ta dago kai ta kalle ni nace anty kiyi hakkuri don Allah kada ki sa wanan abin a ranki mana.
Bani kayan yaran in shirya su kada su rasa falalan wanan ranan ta wuce su ko kuma a rasa wanda zasu bi zuwa sallah idan shi ya wuce.
Kayan ta nuna min saman gado na nufa farar shadda da maryam takai aka dinka masu na dauko da hullan nan su na fice daga dakin.
Bina tayi da kallo mai kama da harara taja tsuki nikan tsab na shirya yaran suna fitowa daidai shima ya gama shiri ya fito da sauri kada ya makara.
Nace ga su zasu bi dan kallon mu yayi batare da yai magana ba suka fice nace adawo lafiya banji ba ko ya amsa kitchen na koma na samu laraba mukaci gaba da aiki.
Kafin wani lokaci mun hada tuwon farar shinkafa sai miyar ganye kadan stew yafi yawa da kaji da akaiwa yakan ci muga iyakar ka nan fa akeyin ta don babu kula na kwarai da zan kai abinci cikin gidan su.
Ba kuma dama in tambayi matar gidan da tahau ta cika nasan ko na tambaya bakar magana ce rabona sai wanan karon naji nima ya kamata in samu kayan aiki a gidan fa.
Don nima ai yanzu matar gidace dai mama ta gane may ne tunawa bayan mun gama saka tuwon a leda mun cika babban kulan da nazo dashi shake da nama a cikin sa.
Wayana na dauko nayi wa ya Amina bayani tace barin shiga nan makwabta na dubo maki akwai matar da sana,anta ke nan sai in hado maki da wanda nake dasu anan.
Ba a dauki lokaci ba ko sai ga shi anyi sallama wata yar matashiyar budurwa ne tazo da set uku na kula duka na saye nace ta karo min biyu idan akwai.
Ta fice tana murna mai girma daga ciki guda biyu na cika da abinci nace wa mama daya na Abba daya na cikin gida ne dayan kulan kuma na sawa su AA a ciki don yafi kyau da tsada.
Kafin masu shigo gidan don nasan sun tsaya cikin gidan su ne su gaisa da mutane yasa basu shigo ba har lokacin.
Yar uwa ina typing ne wa jama,an Annabi masu tsoron hakkin wani fa don hakkin su da ke kaina ina son in sauke nayi kina damuna da zancen bati.
Idan kinga zaki iya da hakkin wani ki ta karantawa ba nawa na duk wace zaki iya karanta ki dai sani akwai nauyi babba a kanki na mutumin da baki san ida zaku hadu ba kila sai a gaban ubangijin talikai wanan sarkin kowa da komai da aka hadaki dashi kika yiwa daranjan saboda son zuciya don Allah ki barni haka zabi ya rage akan ki yanzu ko yaron yasan akwai ranan haduwan shi da Allah.
Yana zaune dakin hajiyan su laraba ta shigo da kayan abincin tare da mommy duk yan gidan sai magana sukeyi a tsakar gida suna fadin ikon Allah yau abincin sallah gidan babangida ne a gidan nan.
Hajiya mama daga daki da aka dosa da kayan tace kai mommy yara kuje can kuji dashi da ai ba abincin gidan shi muke ci mu san munyi sallah ba ko.
Mommy ta karaso ciki tana fadin ina zan dashi ai sai kin gani kin sa albarka wanan sabon sauyi da ya samay mu haka ko hajiya ummu tasa bakin albarka gata can tana addua ai.
Yana zaune yana murmushi daga inda yake tace yanzu kai wanan abin don Allah bai ma dadi ba kokai fa yanzu shine muhinmanci auren wace ta san darajan iyayye din da muke nuna maka haka tun farko.
Yace yanzun mai tun da safe muka kwasa da fati hajiya da mommy na hada baki suri fadin kai don Allah bar zancen wanan sakaran da bata san inda ke mata ciwo ba fati kan bansan halin ta ba wallahi.
Nan dai ya kora ma su bacin randa sukayi da ita ya kuma labarta masu halin da suke ciki da Nafisa kafin yazo.
Hajiya mama tace dama kai ka barta tana iya shege nidai abinda zan fada ma shine kada su kuskura su taba lafiyan diyar mutane don Amana take gare mu girma da darajan iyayyen ka yasa aka bada ita ba tare da wani dogon bincike ba .
Shiru yayi yana sauraren bayanin da mahaifiyar shi ke mashi din Yusuf ne yayi karfin halin yin magana yace insha Allahu hajiya hakan ba zaima faru ba.
Don yanzu ai dole ya ya dauki mataki a gidan tunda iyali khadija itama zata fara ajewa kinga ko barin su haka a gidan ai bazai yuyu ba don ko yaran nan da sukaje mata hutu sai kafa kafa take dasu a gidan saboda su.
Tace to don Allah ji yara da gidan uban su basu da dama suyi wani dogon motsi wallahi kaji na fada ma ya zama dole yanzu ka dauki mataki akan alamarin gidan ka.
Ita kuma wanan mara wayon ko wanan kokarin da yarinyar nan tayiwa yaran nan bai sa ta kawar da duk abinda ke ranta ba.
Ta yi kokarin itama gyara auren ta don abin ita nata miskilanci ne shitasa na dawo daga rakiyan ta yanzu don ba yar goyo bace lalaci da son

102 / 144

Chapters