MIJIN BUZUWA complete Hausa Novels.txt

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   107 / 144

318K to 321K   out of 431K words

kadai.
Yace ba yanzu ba gaskiya don ban gama abinda nakeyi ba a nan kofa sati daya ma bamu kaiba garin nan kike wanan zancen.
Yau Friday idan mun dawo daga mosque ina son zamu fita daku gaba dayan ku zaria zamu tafi mu gaida su.
Allah ya kaimu nace ina kwantawa ya juyo ya kalle ni yana fadin ba zaki tashi ki nemi abinda kikaciwa cikin ki ba kin san fa kina da ulcer ga kuma lalurar ciki a jikin ki yanzu.
Nace ina gudun in fita in jawa kaina wani magana ne kuma nima yunwar na fara ji yanzu yace you see maganan may zaki jawa kan ki don kin nemi abinda zaki ciwa cikin ki.
Common taso mu fita ki girkawa kan ki abinda kike so kici dole na mike na bi bayan shi muka fito babu kowa a falon suna ciki suna barci laraba kawai muka samu rakube a gefen kitchen din tayi tagumi.
Tana ganin mu ta dan zabura tana sauke ajiyan zuciya tare da fadin yau uwar dakina naji gidan shiru dama kece mai fitowa mu dora girki kuma sai naga baki fito ba kema yau.
Ganin shi a bayana ta fara gaida shi ya amsa tare muka shiga kitchen din dashi yana tambaya na abinda zanci nace orth zan dama don jiya da zan kwanta nasha tea idan nasha yau kuma zai damay ni ne.
Sai da yaga na dora ya fice kitchen din laraba ta shigo tana fadin yau har karfe takwas ya gwauta ba wanda ya fito daga cikin ku.
Nace kin san banice da girki ba don ba zan kara dora komai don yaran ta suci ko mijin ta ba ta dawo tana nuna min bacin ranta a kan hakan kuma.
Tace aishi Alhaji ya saba idan da sabo da halin matan shi girki fa ba wai ya damay su bane gidan nan a gurguje na karasa abinda nakeyi na wanke har tukunyar nace ma laraba ta kai min daki tajirani a can kuma.
A dakin na samay ta nace mama ki hada kisha iya yadda kike iyawa ki zauna a nan din har ki gama tace nagode tana murna.
Sai da tagama zubawa naja tire nima na hada nawa nan muka zauna tana sha muna hira har muka shanye zata fita da kayan nace ta dan dakata har yabi cikin ta.
Hira mukayi sosai tana debe min kewa sai gashi ya fito a cikin shirin shi zai fita yana fadin mama kina nan ne tace eh zata mike yace zauna a binki fita zanyi nace ka karya ne yace zan karya a gurin hajiya idan naje can.
Ido na runtse tare da fadin mutum da mata uku kuma bai daina cin abincin mama ba har yanzu yace kun bani ne nace idan zaka sha sai in baka ai don akwashi.
Zama yayi anan ya sha cup daya dana hada mai ya fice sai guraren goma mama ta fito tana fadin bari ta sauka kasa kada abar falon ba kowa.
Fitan ta bata dade ba naji karan bude kofan wani daki a cikin su ashe anty Fatine ta fito yaran sun damay ta suna jin yunwa ta fito ta duba idan an gama sai taga kitchen din ba komai.
Laraba ta kwalawa kira a dan hasale tana tambayan ta ba,a dafa komai bane a gidan ta ce yau hajiya bata sauko ba tun dazun.
Tsuki taja ta kalli Laraba din tana fadin yanzun ya take son muyi ke nan har wanan lokaci ace ba,a karya ba sai dai idan na rana zaku dora gaba daya ke nan .
Laraba tace hajiya yadda kikace haka za,ayi ai ko sai dai gaskiya ban tsammanin zata fito yanzu ba kila tunda takai wanan lokacin bata fito ba.
Ki kirata muji ko may ya hanata fitowa laraba ta nufi daki na lokacin har na kwanta in huta sai gata nace tace mata ba komai kawai ta juya zuwa fadin sakon.
Bayan ta fada mata ne ta bata rai batare da ta fadi komai ba ruwan tea ta dora masu suka karya dashi su kuma sauran part din bansan yadda suka karata ba.
Darana ma wai ta tsaya jirana ko zan fito sai da laraba tazo tambayanta may zata dafa tace ban fito bane tace hajiya ina ganin fa maganan da kikayi ne ya bata mata rai ta daina girkawa yanzun.
Don wanan dan maganan dana fada zatace tayi fushi ko may tace laraba ta su shiga kitchen din jeloup ta hada masu wanda a gurin dahuwa yai half done.
Ya bude zaci ya kasa ranan tasha fada ni dai ina sama ban fito ba har sukaci suka sude abin su ban san ma sunyi ba daga baya ne nake ji.
Karfe biyu mun shirya zuwa Zaria da ya sanar ma kowan mu kusan nice karshen fitowa inda na samu anty Fati da yaran a falo ban san abinda nake jira ba.
Na fito muka fita a tare Laraba da Yanyala kadai muka bari a gidan suna gadin gida Nafisa ce ta kamay a gaban mota inda muda yaran zamu zauna a baya.
Tunda muka hada ido sau daya na kawar da kai sai naji yace da ita bayan ya shiga motar ke ya haka ki koma baya mana wurin yan uwar ki.
Ki bar yaran nan gaba da Yusuf sai da tayi dan jim ta bude kofan motar ta fito maimakon ta shiga sai ta sa kai ta koma cikin gida a hasale.
Na dauka zai bita ne don ko ita haka ta zata sai yace mu shiga mu wuce kawai .
A kofan gidan su Yusuf ya tsaya ya dauke shi muka wuce sai zaria inda muka samu taro sosai a gurin su.
Sai yamma lis ana kiran sallah magariba mu ka shigo garin kaduna duk daurewa nake a yadda nake duk da ba wani tafiya mai nisa bane amma sai da na wahala.
Yana yi daga inda suke gaba shi da Yusuf yana juyowa yana min sannu har Yusuf din anty Fati da muke a guri daya batace min kala ba har muka shigo gida.
Nan kuma muka samu Nafisa ita ma ta hau ta cika dashi wai ya wullakantata a gaban iyalin shi ai da ba haka sukeyi ba a gaban mota take shiga tare dashi sai yanzu ne zai tsuro da wani munafunci ko dole ne sai yaje da Yusuf duk inda zai tafi da iyalin shi.
Already na yi miya kagin mu wuce nabarwa laraba tuwo ta tuka min ta kwashe a leda ta sa a cikin kula har mu dawo.
Mun dawo sallah nayi na fito hakana cikin yanayi na rashin jin dadi jikina na raba takaiwa kowa nasa sai na mai gidan dana shirya mai a falo saman d/table.
Falon kuma laraba ta gyara shi kwal kamar yadda muke gyara namu nacan Abuja sai kamshi ke tashi cikin shi.
Tun da na sauko ban koma sama ba ina zaune tare da shine yana cin abinci ta samay shi da wanan fitinar haka.
Sai data gama maganan ta yace akwai wanda kikafi ne daga cikin su ko may dasu basuyi min korafin rashin shiga gaban mota ba sai ke.
Ko wani abin zaki tsunta a gaban motar udan kin zauna din Yusuf kuma na sha fada maki baki isa ki raba ni da shi ba tun farko a tare kika samay mu ko iyayyena basu ce zasu raba ni da Yusuf ba balle ke.
Tace tunda yasan abinda yai ma ba aikai bazaka gane hakan ba ne yace kamar yadda kema kika san abinda kikai min Allah ya kubutar dani daga sherin ki ko ?
Ni dai ina zaune na harde hannaye saman kirji ina kallon su tare da kada kafana tace ai nasan duk bayin kan ka bane saboda an birkice ma kwakwalwa yanzu.
Ke kika birkita min kowa yace mata a zafafe yana kallon ta tace ai kafi kowa sanin amsan wanan din yace ban sani ba sai kin fada min tace nadai fada ma gobe ni zanyi girki a gidan nan din ku sani.
Yace bazakiyi ba don ba haka aladan mu yake ba sai lokacin nasa baki ga zancen su wanda nasan karfin zancen akaina take yin shi dama.
May zaisa kace bata yi tunda tana iyawa wanan ai dama al,adane kawai ba shari,a ba ko Allah ya kaimu goben nace ina mikewa.
Ko baki ce ba ai gobe zanyi din ne don haka ki kama min bakin ki a gurin nan don baki isheni ba ke ta fadi tana karsawa a hasale.
Maganar ta shafe ni ne yasa na saka baki don wanda bai shafeni ba ai bakiji na sa maku baki a ciki ba ko ?
Lalai wuyan ki ya isa yanka a gidan nan amma na baki dan lokaci kadan indai samad ne inda saniyar gaba tasha ruwa ko na baya intazo anan zata sha.
Ba dai ta kawar da kishin ruwan nata ba ko yadda shanun gaba ta kawar da nata tace sai dai ta kawar a burkutacen ruwa nace ruwa ruwa ne komai daudan shi dai ai ruwa ne don ba za a kira shi da wani suna ba can.
Kai ya fada cikin tsawa tare da fadin ya ishe ku hakana ban son kara jin bakin wani a gurin nan kuma.
Sai da na juya ne na ga ashe har anty Fati tana falon zaune ita ma tana sauraren mu nagama abinda nake na haye sama ita kuma tana zaune suna fafatawa dashi.
Wanka nayi na shirya na nufi part din dole sai da na tsaya gyaran part din don ban iya kwaci a hakan ina gamawa na kwanta ban jira shigowan shi dakin ba.
Har barci ya fara daukana can cikin barcin naji hannun shi saman cikina yana shafa a hankali dan gyara kwanciya nayi na shige a cikin jikin shi.
Yace ya naji jikin ki haka da zafi nace banjin dadin jikina na ne sosai na kwanta kin sha magani ya tambaya nace basai na sha magani ba zai bari.
Ina duban yarda zamu koma abuja a haka dake cikin wanan yanayin ina ga sai dai mubi jirgi daku sauran su biyo mota zaifi zan iya na bashi amsa ba tare da na bude idanuwa na ba.
No bazaki iya ba gaskiya ko bukin zainab bazaki zo ba don wanan wahalan da kikeyi idan kin shiga mota nace mama tace zai bari ai ko.
Bai mun magana ba sai can naji yace ki fada ma Adam gobe ina son ganin shi around ten kan maganan AS Jalingo din.
Da sauri na bude idanuwana na sauke a kan shi ya gyara kwanciya yana dan taba kaina tare da fadin wanan na fada maki ya zama na farko yazama na karshe a gare ki don ba haka nake aikina ba ko wanan ina da dalilin yinsa.
Nace koma may ye dalilin duk da ban sani ba dai na gode tunda na samu abinda na saka ma yaya Adam dashi a rayuwa na nima.
Eh hakan na daga cikin dalili na sai na biyu wanan ne karon ki na farko da kika taba rokona wani abu tun haduwa na dake nasha gwada ki ta hanya da dama kina cinye gwajin ki gare ni.
Sai kuma shi kanshi Adam din da nake son in taimakawa wanan ne dalilin da yasa nace ki masa magana yazo mu gana dashi.
Ya Ahmed fa da naji kayiwa alkawari don tunda naji laraban shi abin ya tsaya mun a raina wallahi wani Ahmed nace na unguwar Dosa da mukaji.
Kai Deedar kina da abin mamaki Ahmed kuma ai na gama da zancen shi tun jiya yazo mun yi magana kwagila na sama mashi wanda zai daga shi idan ya iya tanadi.
Mutum ya cika gida da iyali haka tun yanzu wani tanadi kike tsamanin zai iyawa kan sa nan gaba tunda akan haihuwa yake har gobe.
Nace hmmm nan ma kwana nawa ne zamu cika gidan nan yazamanto ko inda zaka zauna babu yace bissimillah udan zaku iya ai ina da bukatan hakan nima.
Ranan ina Allah Allah gari ya waye in bugama Ya Amina waya ya Adam yazo su gana bai bari na fito sashen nashi da wuri ba sai misalin tara na safe.
Ban san may ya kawo Nafisa falo ba ta zauna anan na samay ta har Yanyala da yaranta kitchen na shiga na hada abin karyawa wa kowa a gidan .
Sai dana gama na shiga nayi wanka na gyara jikina lace na saka duk da akwai ciki a jikina bai hana kayan su karbe ni ba.
Ruwan wanka na shiga na hada mai na fito na gyara dakin yadda ya dace mace idan zata fita girki tayi bata bar ma yar uwa daki don sheri tazo tana gyara rai bace ba.
Kamar yadda ni na samu anayi a gidan abin ba kyau don har unders sai ace an manta dashi sai dai kai idan kazo gyara ka kawar inda ya dace.
Wanan nafisa tafi yi min don ita Anty fati sau daya ta barshi na kawar mata Nafisa kuma dana gane abin nata kissa ne idan ta barshi a gurin idan nagama gyara nake bar mata abinta yanzu.
Gashi dai yau tace zata karbi girki a gidan inda kwanan ta ashirin da wani abu yanzu da haihu tana tasan ma yin arbain ke nan yanzu.
A tare muka fito falon dashi muna jere zuwa falon tun muna akan steps din take bin mu da kallo har zuwa saukowan mu kasan.
Wurin table muka nufa inda sai da ya ja min kujera na zauna shima ya ja ya zauna a guda daga inda take tace idan baka mutu ba dai zaka sha kallo.
Wanan bokan naki yaci biya wanan rawan kan da jiji da kulawan kan ai sai mota za akai biya gurin tsafi.
Gidan mu bama tsafi bama shirka idan dai kince ayar Allah na aiki na yarda da wanan kan don bamu wasa da karanta shi don neman tsari ga shedanu irin ku.
Tsiyan abindai mutum bai taba samun yadda yake so nace kamar yadda ke ma ba zaki kara samun irin na da ba a rayuwan ki har a bada kenan.
Yan kwana ki na deba maki a gidan nan gaba daya idan kin dauka wasa ne sai mu zuba na bude baki zanyi magana ya bugi table din da karfi tare da fadin enough.
Nafisa barnan tun raki bai baci ba ke ma kuma idan kika kara tanka ta haka a gabana kuna wanan shashancin ranki zai matukar baci.
Duk wace ta fasa daukana sukutun takai gidan boka ta raina Allah yanzun ma ku dauke ni ku kai iyakarta ke nan
Mata baki da aiki sai sa ido da jan maganagirkin nan ina ba hakkin ki bane yau kin zo nan kin kashe mu da ido kina ganin zaman ki a nan din zai sa mu fasa abinda zamuyi ne komay , ?
Idan naki yazo kin bukaci ai maki banyi ba shine zakiyi magana ba wanan takanar fadan ba haka na hauka zalla da kike yi ina jiyewa wanan bakin naki watarana.
Shiru nayi ban kara magana ba har ya gama fadan shi ya fara cin abincin shi masa na aika laraba ta sayo shina dan diba naci kwara biyu nasha ruwa don ya isheni.
Daki nakoma na barshi a gurin na kira yaya Amina na fada mata tace gashi ko zai fita barin fada mai wayan na a hannun ta naji tana fada mai sakon.
Ina ji yana hamdalla a wayan tare da zuka min addua har na gaji na kashe wayan sai gashi ya kira layina da kan shi.
Yana tambayana nace eh to ina ganin maganan ne sai dai kuma bashi bane kadai zakuyi sai dai idan kazo zakaji ko may nene daga bakin shi.
Yai min godiya ya kashe wayan na wurga wayan gefe na kwanta ina maijin kunan maganan Nafisa a kaina da tayi min a gaban shi duk da na bata amsa dai.
Amma sai lokacin nake dana sani ban bata amsar dayafi wanan ba zafi yadda itama zataji zafin da naji a ranta.
Amma nasan dai idan itace ko yau ma ba gobe ba karawa zatayi don haka na tanadar mata amsan da zan bata mai zafi daidai da maganan ta din gare ni.
Shigowan shi dakin ina kwance na dago ina kallon shi da fuskana dake nuna damuwa a cikin sa yace kin kira Adam din don ban son ya wuce lokacin dana bashi.
Nace na fada mai yana hanya tafe insha Allahu yace ai mai godiya kafin yazo ba wani matsala yace yana juyawa.
Sai kuma ya sake juyowa lokacin har na mayar da kaina saman filo yace may yasa kike son mayar da kanki daya da Nafisa ne a gidan nan ko yaushe ?
Nace amma kaji ai ita ta fara takala na da zancen ko sai taja mutum idan ya bada amsa kuma yayi laifi a gurin ka.
Tana dauka kowa yadda take yake idan bata daina kirana da diyan matsafa ba ni zan dauki mataki da kaina a gidan nan.
Tunda ta fada daya ta fada biyu taga ba wani mataki dana dauka akan hakan yasa take ci gaba da aibantani yadda take so idan kuma

107 / 144

Chapters