har yanzun dai baki dadara da bin bokaye da malamai ba Adda duk kin sai da dan abinda kika samu kin koma kamar wata almajira dake.
Na tabbatar da zaki dogara da abinda kika samo acan zai isheki rayuwa mai inganci har na bayan ki su samu amma duk kin bi komai kin sayar kin mika ma malamai kudi suna maki karyan sihiri.
Tace idan bakin fata kike zaki koyi kunya Fatiha don gidan Samad dai sai na koma Fatiha tace idan ba komawan Allah da Annabi zakiyi mai ba ko yanzu idan kin koma gidan jiya zaki samu.
Don wanan da kike yi kanta tafi karfin ki saboda ta fiki rike makami a hannun ta na tabbatar da in har ta dogara ga Allah ba zaki taba cin galaba a kanta ba.
Maganan yai matukar bata wa Nafisa rai sosai haka yasa ta harzuka ta hau fada ma Fatiha magana cikin bacin rai ita ma.
Har take fadin ta gane da ita makiya ke mata dariya dama ta fahinci tana tare dani ai nan dai sukayi kaca kaca da junan su sai da kyar uwarsu ta samu ta raba su.
Bayan kamar awa hudu da fadan su kowa ya kama gaban shi tana zaune saman wani matacen tabarma wani yaron dan makwabatan su ya fara shigo da kayan abincin da AA ya tsaya ya sai masu a hanya da ya shigo kasan Niger din.
Ido ta zubawa yaron dake sintirin shigo da kayan Fatiha ce tayi karfin halin tambayan yaron wa ke da wanan kayan haka yaron yace bako sukayi a gidan.
Nafisa ko sai tunanen maganan malaminta yalliya take yi a ranta sai zuba ma kofan dan gidan nasu wanda ba wani gida bane ido.
Sallaman da yayi ne ya shigo gidan yasa gaban ta faduwa don sai take ganin kamar mafalki take yi bashi bane ya shigo gidan ba.
Fatiha dake tsaye a gaban kayan ne ta iya taron shi tana fadin sannu da zuwa ashe kana hanya maraba da babban bakon mu.
Kallon Nafisa yake yadda ta ramay tayi baki duk ta jemay ka wani kwano a gabanta da bussashe tuwo a cikin shi da akaci wanda alama ya nuna itace taci abincin ta kasa kawar da kwanon a wurin don kiuya.
Kawar da kai yayi daga kallon ta ya mayar ga mahaifiyar ta data fito daga dan bukkan ta tana son itama ta ganewa idon ta.
Dakin iyayyen su Fatiha tayi mai shimfidan ta barma mahaifin su dake kwance a gefe yana jinya ya dago da kyat shima yana masu sannu da zuwa.
A gurin da akai mai shimfidan ya zauna tare da gaida dan tsohon da yunwa ke barazanar aikwa dashi lahira ga kuma ciwon dake damun shi.
Nafisa na ganin ya shiga daki ta mike da sauri ta fada dakin su tare da saurin canza kayan da ya samay ta dasu don ita kanta taji kunyan a yadda ya samayta ya samu gidan nasu kuma.
Don zuwan karshe da sukayi duba jikin uban ya bata kudi da za ai masu gina a canza gidan amma ta hada ta dunkule ta koma Nigeria da kudin ta halakasu wurin bokaye da malamanta.
Tana shiyawa a cikin sauri wanan zancen ya fado mata a zuciya bata san yadda zai dauki wanan abin ba tunda bata sa zai dawo zuwa yanzu ya gane ma idon shi bata aikata abunda yace tayi ma iyayyenta din ba.
Nan dai ta zauna a dakin don matukar kunya da nauyin samad din ne ya kamata yadda ya samay ta da kuma gidan nasu da iyayyen nasu.
Fatiha ce ta shigo dakin tace lalai bokayen ki sun iya aiki don aiki ya biya sai dai bamu san irin kamun da zakiyi ba a yanzu kuma.
Nan dai fada ya kaure kuma dole taja bakin ta don kada AA din yaji hayaniyan su ya kara raina mata hankali kamar yadda yasha yi mata.
Fatiha tace yazo da maganan maida auren ku ne duk da dama a shiye kike da hakan don da sanin ki hakan zai faru.
Sai dai ina mai baki shawara ki bi a sannu wanan karon ki rike darajan auren ki ku zauna lafiya da kowa a gidan.
Fatiha taci gaba da fadin ba komai da kake so kake samu ba kai tsaye ki dogara ga Allah daya umurce shi da tara mata iya adadin yadda yake so a gidan shi.
Ko ba a fada maki ba wanan da kike tayar da hankali a kanta tafiki da komai wallahi kece dai ba ki yarda da hakan ba a zuciyar ki.
Kinyi saa idon da zuciyar mijin ku ya makance a kan ki nafisa har bai iya hango illar ki a gidan shi don abinda yasa nace ta fiki ilimi da sanin kai shine agaba ke makin sani.
Don haka ne nake cewa tafi ki ga komai wallahi don tana da ilimin da take amfani dashi gare ki da mijin naku a cikin hikima da basira wanda ni na dade da hango haka a gare ku.
Tace zaki uya zuwa ku gaisa yana dakin soro yana jiran ki idan kin dawo zamu karasa magana da muka fara tace da yar uwan nata.
Ta mike jiki a sanyayye ta fita dakin zuwa dan dakin da yake din ta shiga da sallaman ta dakin yana zaune yana kallon ta ta shigo.
A daidai lokacin kuma tsoho bado na can yana aikin cire kafi da sihirin da bokayen ta suka tura a gidan don bai zauna ba tunda ya shigo.
Take gaban shi ya fadi ya rasa may ma ya kawo shi nan yanzu shida ya rabu da kaya a baya hankalin shi a kwance yanzu a gidan shi yazo ya jajibar wa kansa wani wahalan nafisa kuma again.
Sai ya tuna don yaran ta ne kuma shi din ba wai baya son ta bane a ranshi kallon da yai mata ne ya dan razana ta don ba haka yalliya ya fada mata zai faru ba a tsakanin su idan yazo.
Cewa yayi zaiyi kuka ya gurfana mata yaji duniya babu sauran mace sai ita kodai hakan bai faru ba ita dai idan ya dawo da ita din zai fi mata sauki.
Cikin sanyin murya take mai sannu da zuwa tare da gaida shi da hanya cikin sanyin jiki.
Ya dago ya kalleta yace yanzu ke kin ga wanan zaman yafi maki a nan haka dukar da kanta tayi kasa don nauyin shi da kunya da take ji yanzu baki ya mutu murus bana fadi kuma.
Tace nasan nayi ba daidai ba a baya abinda nayi na nuna son kai da bin shawaran kawayen bariki a kasan ku wanda ashe abin ba haka yake ba.
Nai ma alkawari idan na koma yanzu zaka ga canji a gidan ka a tare dani idan Allah ya yarda cikin nadama da zai iya yarda da tuban ta.
Yace idan kin yi hakan kin kyautawa kanki na baki yau zuwa gobe ki gama shirin ki mu koma tare dake.
Wani irin ajiyan zuciya ta sauke don jin abinda ya fada ya mike ba tare daya tsaya sauraren abinda zata ce ba don yana son yaje yayi sallah a lokacin.
Yana fita ta bishi da kallo don ya cika mata ido a gurin ta sauke ajiyan zuciya taga ya koma fari ya zama wani kato har dan tunbi ya aje tace a ranta dan barin ta gidan ashe bai damu da ita ba ke nan tunda had ya samu kwanciyan hankali a tare dashi haka.
Wai shi samad wani irin muyum ne malamin ta ya tabbatar mata cewa ga abunda zaiyi idan yazo sai bata ko digon girgiza da nadaman rabuwa da ita ba a tare dashi banda shan kamshin da yake mata.
Tace ba komai a ranta ta samu din ta koma tunda har yazo din zata dasa a inda ta tsaya sai taga bayan wanan yar iskan da harda yar uwan ta ke ikirarin ta fita wai da munafukan iyayyen sa masu daure mata gindi a gidan.
Don ba karamin shiri tayi akan komawan nata ba don ga haske ta fara gani tunda har yazo din wurin ta.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
Kuyi hakkuri yau ba yawa kun san ranan yau ina gajiya sosai .
1/13/21, 7:23 AM - Fatima Amarya: Ranan Bado bai kwanta ba sai da yayi duk wani abinda yake son yi a gidan zuwa safe ya gama hada komai koda na shiga gaida shi bayan sun karya yake ce min su zasu koma.
Da mamaki na kalleshi tare da fadin tun yau kaka Bado yace to may zan tsaya yi na gama maki abinda ya kawo mu ai sai dai gaskiya duk wanda yai wanan aikin dana cire a gidan nan yana da karfin zuciya sosai.
Ki gode ma Allah dake baki kariya akan hakan don da wanan asirin dana gani a gidan yana aiki a kanki da yanzu sai buzun ki.
Nan dai ya fada min maganganu masu firgitawa yace harda wanda aka tura ai muna a yanzu duk ya karya su insha Allahu.
Ya kuma dasa nasa don neman kariya a gare mu a gidan ya kara da ce min kada kiji komai akan duk wani abinda zatayi akan ku akan ta zai koma komai ta dauko maku.
Ke dai ki kara dagewa da neman tsari a wurin Allah da gafaran sa shine babban mafita a gare ku nayi mai godiya sosai na koma ciki na hado mai tsaraban da zan basu na kawo mai yace a, a ko kufin motar ki ni ba zan karba ba mu dai fatan mu ku zauna lafiya da mazajen ku ku tara muna iyali masu albarka.
Murmushi nayi tare da masa godiya nace da Alkasim zan bashi sako na muka fita nace ya dauka idan sun isa ya bashi a can ya kara min godiya.
Suka tafi suka barni da kewan su a gidan tun tafiyan su na fara aiwatar da abinda ya bamu a kaina da yara na a cikin da bara nake aiwatar wa.
Ya dade a tsaye yana jiran ta don ance tun safe ta bar gidan zuwa wani guri da ba,a sani ba a lokacin ne Fatiha ta samu kebewa dashi.
Tace ka ga farce ni ga abinda ya faru a bayan wallahi bada sani na haka ya faru ba sai da wa yan nan mutanen suka tsayar damu ne na san abinda ke faruwa.
Yace ba komai Fatiha tace duk da haka sai ka kara hakkuri da Adda don bawai ta canza hali bane sai ma abinda ya karu mata daga halin ta daka sani a baya.
Murmushi ya sauke a fuskan shi yace Fatiha na saba da halin Nafisa banga wani abu da zatai min yanzu wanda ban sani ba daga halin ta kuma.
Allah ya kyauta tace don tasan ba yin hankalin shi bane bai a cikin hankalin shi don koda ganin yadda Nafisa ta koma ba zai kalle ta ba ai.
Tunda ta tun karo gidan gidan ta hango motar shi a kofan gidan gabanta ya fadi tsayawa tayi nisa da gidan tana tunanen abinda zata fada masu don tun asuba tabar gidan zuwa wurin malam boka Yalliya don da nisa sosai da kauyen su zuwa wurun shi.
Hango AA ya fito daga gidan ya kara fadar mata da gaba ta karaso don babu yadda ta iya tana ganin kamar tafiya zaiyi ya barta kuma.
Simi simi ta karaso tana kokatin boye ledan data dawo dashi cikin jikin ta da ganin ta kasan bata da gaskiya a yanayin da take tafe.
Daga ina kike haka ya fada fuska a daure yana kallon ta ta dago kai ta dan kalle shi tace daga gidan yan uwa na nake can cikin gari naje in ban kwana dasu ne.
Yadda take in,inaya yasa ya fahinci bata da gaskiya yace shine baki danar da kowa inda zaki ba da zaki fita tace koda na fita babu kowa a kusa lokacin.
Yace ke dai kika sani tunda ba zaki daina wanan halin da kika sawa ranki ba na biye biyen bokaye da malamai sai dai ki sani indan ni kike wanan shirmay babu abinda zan fasa.
Tace wanda yace ma na fito wanan wurin bai fada ma daidai ba ni sada zumunci na tafi yi a gari yace ki shirya don kin san da asuba zamu wuce ban son inzo in samau baki shirya ba kuma.
Tace Allah ya kai mu ta shige gida tana ta kokarin boye galon din ruwan rubutun da ta dauko a hannun ta.
Tana shiga ta nemi wuri ta aje kayan hannun ta tace wa fatiha ina kika fada ma Samad naje ?
Fatiha tace ina maki hani da kiran mijin ki da sunan nan na Samad don Allah kadai takai can a kirashi da hakan don zunubi kike daukarwa kan ki.
Idan na kirasa da haka ki hana shi ya amsa min yar sa ido duk sherin da zaki kulla min an rigaki ko don bakin ciki kinga zan komawa mijina zaki kulla min sheri cewa naje gidan bokaye.
Kai Fatiha ta kada tace ai hannun ka bai rubewa ka yanke ka yar sai dai kaita kayan shi hakana a jikin ka.
Ni ban fada mai komai ba tunda ba hauka nake yi ba da zan bata maki auren ki nassn abinda nake kece dai ke dauka na makiyar ki don fadin gaskiya na gare ki.
Nasan a yau zasu dawo don haka tun tashin mu nasa laraba ta gyara muna falo da ko ina na gidan inda naje dakin shi na gyara da kaina.
Mun gama na saka kamshi a ko ina na gidan tare da abinda tsoho bado ya ban in hayake gidan dashi gaba daya.
Daga nan muka dawo part dina muka gyara komai a ranan na canza komai na part din aikin maryam ne wanan komai sai kyali yake kamar ranan aka kawo ni gidan.
Sai zuwa hudu da wani abu muka rage aikin komai ya kammalu karmar yadda nake son shi wanan karon launin purple da fari ne a part din nawa.
Komai ya canza gaba daya sai mutum ya dauka sabon wuri ne muka koma ga kayan da ta karbo min wurin dinki data kai express akwana biyu aka gama min su.
Sai turare dan arab iri iri data kwaso min da kayan make,up abinci lafiyayye Altine ta girka da abin sha zuwa biyar duk mun hada komai mun kara gyara gidan da part fina duk da baiyi wani datti ba.
Shida da rabi suka diro gidan tare da yanyala da samiha sai samira da tai wani baki sai hakora da dogon gashi ya rage a jikin ta.
Suna zuwa part dina ta nufa da murnan ta sai kuma taja ta tsaya tana bin ko ina da kallo ta sauke ajiyan zuciya.
Na tare ta sosai tare da murnan ganin ta ta dan dade zaune a wurina nake tambayan ta ko tayi ciwo ne tace batai ciwo ba yunwa daine don ba abinci kamar nan ba kulawa da sauran su.
Tausayi ta bani sosai da take min bayanin sai gata tana kuka tana fadin ita ba zata kara komawa can ba.
Hakkuri na bata tare da fadin taje tayi wanka tazo taci abinci tace zataci kafin tayi wanka haka nasa a debo mata abinci ta zauna ta fara ci.
Sai da ta kusan gamawa ne sai ga samiha ta shigo kiran samira din da wanan halin nata na rashin sallama idan zata shigo wuri cikin tsawa na dakatar da ita da fadin ke idan ba zaki sallama ba maza ki fice min a part din nan.
Sai da ta dan kadu tace Sallamu Alaikum na amsa a hasale tare da fadin wanan dabi,an baida kyau don Allah mutum kamar ba musulmi ba shiga wuri ba sallama.
Tace a cikin yaresu uwar samira na kiran ta sai yarinyar ta bata rai nace jeki kiji kiran da ake maki sai ki dawo ta mike zuwa amsa kiran da uwar take mata.
Shiru shiru banji ya shigo ba na daure na mike zuwa part din shi in mai sannu da zuwa dauke da Al,amin a kafada na.
Na shiga da sallama na samu ya fito daga wanka yana saka riga a jikin shi ya amsa muna sallaman tare dan juyowa ya kalle ni ya mayar da kan shi ga abinda yake yi din.
A hankali na tako na karasa shiga dakin na tsaya daga bayan shi ina fadin sannun ku da zuwa an dawo lafiya ya mutanen can ?
Lafiya ya amsa lokacin da yake karasa saka rigar a wuyan shi yace ba tare da ya kallo ni ba fuska ba yabo ba fallasa yace waye kika dauko nace Al,amin ne yace ina mami sai lokacin ya juyo yana fuskanta na.
Nace tana barci bayan Laraba bai sake magana ba sai ya dauki turare yana fesawa jikin shi tsarguwa da mamakin shi ne ya kama ni a lokacin.
Shiru dakin ya dauka na dan wani lokaci juyawa nayi zan fice daga dakin don jin shirun yayi yawa akwai abinda zanci ya fada a takaice.
Akwaishi idan zakaci na girka maku dama don ina sa ran dawowan