MIJIN BUZUWA complete Hausa Novels.txt

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   139 / 144

414K to 417K   out of 431K words

Don haka ina ga ka saba bata ta halartar da komai yanzun kuma ka janye daga hakan kaga ko dole ka samu wanan korafin.
Nan dai ya kora ma dan abinda tazo mai dashi ya rantse ma uban baisan da zancen komai ba akai Abban yasa laraba ta kiramu dukkan mu a falon.
Nice kusan ta karshen fitowa koda na karaso suna jirana na iso da sallama dauke a bakina na samu wuri gefen kujeran da anty Fati ke zaune na zauna ina gaida Abba da kwana da gajiyan jamma,a.
Kai Abban ya kada ya amsa min ya danyi gyaran murya tare da kallon inda nafisa take zaune yace jiya kin je kin samay ni da korafi akan mijin ku tace hakane Abba.
Don ko gaba daya wanan ta kulle dakin da kayan ke ciki yadda kowan mu nan baizayi amfani da abinda aka sayo ba don bukin.
Dago kai nayi ina kallon ta da mamaki sai na duka don Abban bai gama magana ba a lokacin.
Ya juya gurin dan yace kai kaji maganan ta yaya akayi ka halarta wa mutum daya yace Abba ban san da wanan maganan ba ni.
Ya juyo gare ni yace gwagona yaya akayi muna son bayani na hade miyau dakyat don takaici nace Abba ba shi ya saya min komai dana zo dashi ba.
Sai dai kudin da ya bamu ne nayi amfani dashi don nasan yawancin jama, a anan gurin mu zasu sauka nayi wanan dabaran shima baisan da zancen komai ba.
Ya dago kai yace kinji abinda suka fada ya baku kudin ko bai baku ba kuma tace ya bani da zamu zo Abba yace masha Allah.
Abinda nake son ji gareki ke nan dama AA tace ita kuma Fati gata nan shekaran jiya na turo mata nata nayi mata bayanin komai.
Amma Abba sai nazo gidan nan na samu matan nan ba wanda ya tafi gurin kamun zainab jiya din ni banyi fushi kan haka ba sai ita mai son banza zatayi wani korafi can.
Abba yace a nan dai na fahinci gwago na tafiku da bara da sanin ya kamata tunda mutumin nan ya baku ne don ku fitar dashi da kan ku kunya.
Shiru kowa yayi a falon yace da har nazo da zuman ci ma mijin ku mutumci akan may zai dauki girma da nauyi ya ba karama a cikin ku ashe ita ta sayawa kanta mutuncin komai.
Ba wurin shi ba har gurin mu mu iyayyen shi irin matan da Allah yace ka aura ke nan macen da zata iya rufa ma asiri.
Wanan maganan da Abba yayi yasa Nafisa taji haushin shi sosai watau abinduniya ya rufe masu ido ke nan.
Ta ce Abba ai na dauka don bukatan kan mu ya bamu wanan bukin shi ta shafa don may daga baya za a ce muyi hidima dashi kuma.
Ke rufawa mutane baki a gurin nan kada in kara jin muryan ki a nan don ke fitsararace dama yana fadin haka ta ce Abba na gode ta bar gurin.
Abba wanan ta isheni a gidan nan wallahi don ku nake zaune da ita har wanan lokacin haka ka ganta ka auro ta yanzun ne kake gano illar auren irin su.
Baka da wani kwakwaran dalilin cewa ka gaji da ita a yanzu halin ta ne kai zaka gyara abinka sannu a hankali ta koma kamar kowa.
Ita dai wanan khadija ta nuna muna ita yar tarbiyace ko daga yanayin kamalan ta da mu,amula da mutane mutum zai gano haka gare ta ya dan muna nasiha yayi muna sallama ya tafi suka fita tare da AA.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/25/21, 9:22 AM - Fatima Amarya: Ranan duk yadda naso inyi walwala raina ya baci na kasa tsayawa in yi komai ga anty fauziya sai aiko min in fito mu tafi gidan zainab.
Kiran da maryam tayi min ne tana sheda min tasowan su ita da wasu abokaina yasani fara tunane.
Dama don haka ne na garje nayi wanan don Anty hauwa muna firan bukin a gabanbta tace to kinga shawara zan baki yanzu.
Duk yadda zakiyi ki kokarin a wurin nan ki zage ki fishi nuna damuwa da sha,anin bukin fa blood sister din shi ne za a yi.
Ke kuma sai ki hikimar da zaki kara haska kanki ga kowa a gidan dama zuciyar mijin ki muna hada baki gurin tambayan ta may zanyi ?
Tace bude aljihun ki ki basu mamaki ki shanmaci kowa a gurin kiyi gifts ki bada karfin ki koda ba a son hakan gare ki.
Nace nasai robobi da zan raba a nawa bangaren taja tsuki tare da fadin mijin ki mai hali ne fa khadija kudin nan badaga aljihun ki zai fito ba don may ba zakiyi abinda sai sunji mamakin ba ki nuna kin fishi son yan uwanshi.
Idan kika kama zuciyar uwar miji dana yan uwan miji don dole miji yai maka ragowa kema kuma naki yan uwan da iyayye su kara haske a gare shi.
Wanan daman mata da yawa suke sakaci dashi gurin mallake miji a tsaya ga asiri ba wani hikima a ciki ni kon gani nan tambayi maryam kiji idan sha,ani ya taso a gidan su man yadda yake zama nawa.
Robolan banza abu zakuyi wanda ya banbanta dana kowa da zai ba mutane mamaki har shi kanshi mijin naki ai ba don komai zaki haka ba sai don daga darajan ki dana diyan ki da yan uwan ki gare su ko ba a wa Allah dole a yi dake.
Itace ta ban shara duk wani abinda zanyi tace ga haushin da kishiyoyin ki zasu ji kan hakan sai a koma gulman kin malake miji shiko yasan ba haka bane.
Ina cikin wanan tunanen ne ya shigo dakin nawa daga ni sai yara na a dakin sai sadiya dake gwalanniyan ta daga kwance.
Har ya karaso inda muke kwance ya dan ja kafana tare da fadin yau ba buki ne na ganki a kwance har wanan lokacin.
Ganin yana kokarin zama yasa na dan matsa mashi kadan ya zauna yace ko dan maganan wanan mara hankalin ne yasa jikin ki yai sanyi ?
Kokarin mikewa zaune nayi nace maganan ta bai sani jin komai ba sai ma dadin da naji don haka ya bata daman gyarawa itama.
Yace idan suna da niya ko ke baki san wa yan nan matan bane sune matan da ake kira da masu hana miji mu,amula da yan uwan shi.
Barin fayace maki abinda kila baki fahinta ba dasu don ni yanzu na gama gane halin kowan ku ita dai Fati da kike ganin ta.
Mace ce shasha wace ko kanta bata iya hasala ma komai ki duba fa yanzu buki ake ji yadda take zama a gidan nan ita dai butin ta a bata kudi ta kimshe su.
Ko tabi wani hanya dasu na daban wanda ba wanda yasan abinda takeyi dasu sai ita don ba a gani a jikin ta ba ba a kuma gani ga wani nata ba.
Sai bakin hali da bakin ciki ga zurfin ciki ko kaine wa baka gane cikin ta don ma bata yarda da kowa ba ita kowa macuci ne gare ta.
Ita ko nafisa ba a maganan ta don ke kanki kin fahinci wasu hali nata burin ta shine ta mallake kowa ya koma karkashin ta harni sai yadda tayi dani ta juyani yadda ranta ke so ita zaki iya kiranta da yar tallaka da gadara.
Da farko kan ta samu yadda take so dani amma shigowan ki a rayuwan mu ya maida ita baya sosai don ta kasa juya ki yadda ta samu daman juya Fati.
Don ke baki dauki wajan ba a gareta da kin yarda ta juyaki da an zauna lafiya ko ki bar gidan nan don bata yarda taga ina mu,amula da wata mace.
Nace tunda don ita kadai aka halice ka ko yace rayuwan ta ke nan sai dai ta juyani da duk wani wanda ke karkashina yadda take so.
Ban san lokacin da nace nifa murmushi yayi ya juyo ya lakuci hanci na tare da fadin gaki nan dai har yanzu na kasa kai karshe ga alamarin ki sai dai nasan komai da zuciya daya kikeyi wa mutum ke.
Aiko na samu sheda mai kyau yace tukunna dai ai ba, a gama shedan mutum cikin yan shekaru sai nan gaba idan na karo maki kishiya in gama gane halinki.
Wasa yuka a gaban doki baya tayar da hankalin doki ai yace eyyeh haka kika ce nace kwarai kuwa.
Su wayan nan dake gidan ka muke zama tare ai kidhiyoyinane haka kuma wace zata zo bayana ita ma kishiya ta ce mai zai sa daga baya in tsiro da halin da ba nawa ba sai dai itama idan tazo min da akidar rashin gaskiya.
Ko yanzu kai niya sai ka kara ni ba matsalana bane kaine mai aiki kaida ka dauko abinka wace ta shigo ta samu mata biyu a gaban ta haka wata kishiya kuma zata razana ni yanzu.
Lalai shiyasa nace ban gama tantace halin ki ba sai na kusa kammalawa sai ki tsiro da wani halin da ban sanki dashi ba.
Yanzu dai nazo in ji nawa kika kashe a cikin wanan hidimar in baki kudin ki kamar yadda kowa zai amfana da nasa.
Badon ka biya nayi ba nayi ne saboda Allah dakai da diyana da kuma mama da zainab din ko ka manta zainab kawatace nima kamar yadda Yusuf yake aminka .
To tunda kin ce haka zan kara maki gudun mawa na wuri hidimar bukin hakan yai maki ko nace yanzu kayi magana ya mike yana sa hannu a aljihun jallabiyan dake jikin shi ya fito da rafan yan dubu dubu guda biyu ya dora min saman jikina sai da na zaro ido.
Zanyi magana ya dora yatsa a bakin shi yace min shiiii alaman in kyale duk da haka sai da nayi mai godiya ko abindana kashe din bai kai nan ba ai.
Riba biyu ke nan na samu a gare shi a lokaci daya na anyana a raina yakai kofa yace yau kece da girki kin sani kada ki shagala da buki ki manta dani.
Kafin in magana ya fice a dakin ya barni da tunane koda zanyi girki garin nan ai bani ya kamata in karbi girki ba yau da na gaji da tunane na mike na bar gurin na fada bandakin don yin wanka.
Bayan na fito na shirya ban dauki lokaci ba na fito na samu laraba ma sun shirya sai dai Alamin wai yana gudawa.
Dakin Anty Fati na shiga na gaida ita nake fada mata zan shiga cikin gida tace yanzu nace eh tace sai ta shigo na fice.
A coridor din sama muka hade da Nafisa ta watso min uwar harara ban damu ba nayi mata ina kwana kamar ba zata tanka ba sai dai ta amsa min cikiciki na wuce.
Altine kwana biyu tana gidan su, sai na samu sun shigo da yan uwanta muka gaisa sukai min ya gajiyan buki.
Tare dasu muka bar gidan bayan mun rufe duk dakunan da nake da makullin su ka shiga cikin gida inda muka gaisa nake fada ma momy zancen Alamin din da baida lafiya .
Anan gurin momy na barsu muka wuce zuwa gidan zainab da za a kaita don karasa yan gyare gyare sai lokacin ne mutane ke ganin wanan kayan da AA ya saya mata wanda ba kowa ne ya sani ba.
Don ranan farko sunki zuwa gyaran dakin yau ko harda su anty Amarya muka zo gidan da wasu yan uwa da yawa.
Kafin mu koma fida har zance ya kai kunnen Abba murmushi yayi yace shine samun ai kasamu dan uwanka ya san ka samu.
Umma taso jan zance da tsawo sai Abba din ya katse maganan yana fadin abinda zamuyi farin ciki yaya kuke kokarin maidashi abin tsegumi ne wai.
Ina da kune masu korafin yaron nan bai komai ga kowa yanzu kuma an samu hankalin shi ya dawo gida za a kuma ce bai kyauta ba.
Umma tace Alhaji nina ga ba haka aka saba ba ai a gidan nan hannu ya daga mata tare da Anbatan sunan ta.
Yace ina son ki gane mutum bai lokacin shi yace kuma sai yayi na wasu ku godewa Allah da yanzu nake da mai taimaka min tace amma Alhaji kasan dai an munafunce mu ko.
Yace a cikin zancen nan waya munafunce ki rakiya sai tayi shiru kada ta zake da yawa a gane manufanta hakan yasa ta kulle hajiya mama a ranta.
Suka shiga yar tsama da juna da akazo kai gara aka kirata tace ai an tsamay su a ciki don yin abu ake ba a shawara dasu cikin wanan rikicin muka dawo gida muka samay su a hakan.
Bayan mun gama saurare ne ni dai naja kafana zuwa dakin momy inda na samu ya Amina dasu momy na cire gyale na na shiga sallah.
Har na fito suna magana guda a raina nace manya ke nan suma da tasu kalar kishin ko ina dai abin ba dama ashe yanzun kuma may ye a cikin wanan ?
Dakin hajiya mama na nufa bayan na gama ba yara nono na samay ta da yan uwanta na zaria sun shigo ina shiga muka fara gaisawa.
Hajiya mama take tambayana ko naci abunci nace yanzu dai zanci mama na shige ciki gurin da yayan ta duka suke dakin banda zainab da Binta tace suna gidan mu tare da kawayen su.
Ban dade da zama ba suma dai anan din zance gudane kan bakin cikin da ikon hajiya mama suke ta nanata maganan tambayan su nayi yanzu don bata saka baki ba ba za a kai kayan yau ba ke nan ?
Faiza tace min don may ba za a kai ba ga yan uwan Abba can dana hajiyan mu su zamu fitar sukai a raina nace ashe maryam nada aikin sarakuta da wanan matar da kowa ke fadin halin ta.
Hajiya mama mace ce mai kawaici da girmamawa tasan abinda umma ke nufi amma haka ta shanye maganan a ranta ta hana ma ayi maganan sai murmushi take sakewa a fuskan ta.
Duk yadda hajiya Umma taso taga auren zainab kasa dana diyan ta hakan bai samu ba gare ta don Allah yayi zainab zataci daga arzikin dan uwanta da ake tsegumin bai masu komai a baya sai gashi ya garje ya fitar da yar uwanshi da uwar shi kunya don har da motar shiga mai tsada ya danka mata .
Ban samu dawowa gida ba sai goma na dare na dawo na samu ya cika fam dani kan rashin dawowa in karbi girki kuma ya hana nafisa yin girki sai anty Fati ce tayi girki a ranan.
Isowan bakina ne ya kara sani zama busy a gidan tare dasu muka dawo gida inda na sauke su a dakina su hudu ne suka zo tun zuwan su nasa laraba ta dawo gida don shirya muna abinci da gurin kwana.
Ga zainab gidan tare da kawayen mu ban samu ganin shi ba sai washegari da safe ina kitchen ina hada ma bakin mu abin karyawa ya shigo kitchen din.
A tsorace na juyo don jin mutum gab dani ina juyawa na ganshi nayi mai ina kwana sai ya basar dani kamar bai jini ba yace kin kyauta watau ke van isa yanzu ince ga abinda zakiyi kiyi min ba ko ?
Nace kamar ban gane may yake nufi ba may kuma nayi ma yaya AA au ke baki san abinda kikai min ba ke nan ko ?
Wallahi ban sani ba na bashi amsa may nace dake jiya akan girki sai na dan sake murmushi a fuskana nace a, a ba hakana bane yaya gani nayi ai bani ya dace in karba jiyan Nafisa ce zata karba sai ni ko ?
Ke zaki gwada min yadda zanyi dani da gidana matan ki ko nawa ni na aje kowa a cikin ku sau nawa zan fada maki ki bar zancen nafisa a yanzu ko so kike ki bata min rai.
Kayi hakkuri ban san haka zancen yake ba in Allah ya yarda yau zan ma girki idan kin ga dama kada kiyi wanan ba matsalata bace ai.
Murmushi mai kama da takaici na sauke a fuskana laraba ta shigo dauke da flask a hannun ta shiyasa har ya bar kitchen din ba wanda yai magana a cikin mu.
Bakina sunci sun sha da yan matan zainab da suka kwana a gidan mu duk nayi ta fama da dawainiya da su har sha biyun rana muka gama shiryawa zuwa cikin gida.
Kallon da hajiya umma tayi muna ne yasa duk muka tsargu da ita muka bar part din ta zuwa sauran part din gidan a dakin momy na aje bakina don dakin hajiya mama cike yake da mutane.
Karfe biyun rana da rabi shine lokacin daurin aure tun cikin dare na saka zainab shan abubuwa har zuwa wanan lokacin ina bata a fakaice tana sha.
Adakin momy gaba dayan mu muke har su Faiza da

139 / 144

Chapters