dan huta a daki idan nayi sallah.
Na mike suka bini da kallo sai dana shiga ne laraba tace mace mai hakkuri komai tana gani a gidan auren ta don kin san dai wanan maganan ba gaskiya a cikin sa fada ne ba halin ayi kawai.
Altine tace hakkurin yarinyar nan yai yawa wallahi ba zakace zaka samu yaran yanzu da wanan halin ba.
Nan dai suka zauna suna zancen ina ciki bayan na idar na jawo wayana ina fada ma maryam abinda ke faruwa don bamu samu kebewa ba a school.
Ina gama wayan daidai lokacin ya dakin ba sallama balle inji shigowan shi sai muryan shi naji yana fadin baki ga sako na bane dazun.
Nagani nacea takaice tare da juyar da kaina gefe daya na bar kallon shi yace dake nake magana ai .
Nace don banda bukatan komai yasa ban amsa ba idan ma ina da bukata ai kasan duk abinda ya dace a saya a gidan ko ?
Bai iya furta komai ba don yadda yake jin zuciyar shi a lokacin kamar zai tafi yace ba haka na saba ba don haka ki fada min abinda kuke da bukata nace.
Shiru nayi mai ban bashi amsa ba na matsu ya fice min daga dakin ya sake fadin bakiji bane ina magana dake ya fada a hasale.
Nace ka sayo muna abinda ka sai muna last time kafin ka yi tafiya shike nan ko sai madaran yara da za a saya masu kuma.
Barin fada maki ban daukan wanan tsiwan naki yanzu bai kai karshe ba nace ai ba sai ka fada ba don alama ya nuna kansa.
Don ko ganina baka kaunar yi a kusa dakai don haka nima na kama kaina da kai tunda ba dole dama zaman biyayya nake a gidan nan ai.
Kana ja min tashin hankali na ba gaira ba dalili a cikin gidan nan ina zaune ban shiga shirgin ku ba duk da hakan ban tsira a gare ku ba.
Duk hakkuri da dauriya da biyayyan da nake maku kai kan ka baka ganin hakan sai ka cisguna min ka wullakanta ni yadda kake so.
Menene laifina may nayi maka da zaka dauki karan tsina ka dora a kaina don kawai ka cusa min bakin ciki da tashin hankali a zuciyana.
Ya isa haka kin fadi abinda kike son fadi kin gaji dani yasa kike fadan haka sai dai ki sani zama a gidan nan kamar yanzun kika fara don gida ba fita a cikin shi kin shigo cikin shi ke nan.
Murmushin takaici nayi nace tunda kaine autar maza kake ganin idan an shigo ba fita ka sani ni ba irin tarkacen matan ka bane dake tsayawa yin asiri ko wani abu a kan ka.
Yace nasa don nasan ko wacece ke har da halin da baki san kina dashi ba nasani kaita sani mana wanan kai ta shafa kamar yadda kace baza ka dauki halina ba a yanzu nima haka ba zan dauki naku ba a yanzu daidai zamuyi da kowa a cikin ku.
Khadija wuyan ki ya isa yanka nace har datsa ma ya isa ba yanka ba sai ka shirya ka datse shi din ki shirya min abinci irin na jiya don banda lokacin wanan a yanzu.
Kaje matar ka ta shirya ma ita da kake ganin idon ta da kwali a gare ka yanzu dama ku maza haka kuke kun fi son macen da ke latsaku a zauna lafiya.
Yakai kofa ya juyo yace ashe shiyasa kema kike son ki gwada latsa ni din to bari kiji idan kinyi haka ke wuya zaki ji a gurina wallahi.
Haka kace yace ai kin ji na fadi yanzu sanan may ye dalilin ki na kin shiga motar dana saya maki nace don bada zuciya daya ka saya min ba ai ba don ni ka saya ba may ye mutum bai sani ba.
Kallon mamaki yai min yace haka kika ce to in kara ganin kin shiga wanan motar dake ci mun rai idan ran ki bai baci ba a gidan nan.
Wanan din dai da aka bani da zuciya daya zan shiga tunda bakai ka saya min shi ba OK zamu gani dani dake a gidan nan kuwa.
Ya tura kofan ya fita a hasale nace mijin tace kawai matar ka ta bata ma rai kazo nan zaka fashe a kaina don nice marainiyar ka .
Da safe na fito zan fita sai wayau don babu motar a gurin na juya a hasale na shiga gidan zuwa part din shi banyi mamakin ganin kofan a bude ba lokacin don kila haka ya kwana yana jirana.
Yana kwance yana waya na banko kofar dakin wani kallo yai min ya ci gaba da maganar shi na koma gefe na tsaya cikin fushi ina jiran ya gama.
Ina jin ya gama nace ina motana yake don na fito yanzu ban gan shi ba yace nasa an fitar min dashi a gida don nace bazaki kara shigar shi ba ai.
Wani kake son in shiga ina wanda na saya maki din bazan shige shi ba na fada ma baki son fita ke nan gidan nan key din babbar motar shi dake aje na dauka na fita.
Dashi na fita zuwa school din in da zamu kotu yin wani gwaji sai dana biya school na ga maryam na wuce zuwa kotun.
Ranan sai five muka dawo gida Nafisa na samu tana magana a waje da wasu bakin ta yun shigowa na kallon su ya dawo gare ni na fito a gajiye ina rataye da jakana da rigan mu na lauyoyi a dayan hannu na na wuce su.
Uhuumm naji wata tace tace kin ga illar barwa kishiya gida ke nan Nafisa tace ai ni wanan shegiyar yarinyar ban san yadda zanyi da ita ba.
Yaya ko zakiyi da ita banda ki kawar da shegiya ai taki kawowa ne wata tace kafin nan ai shi mijin naku zaki tun kara da yaba ta wanan daman haka kina may har haka yake faruwa ga matar da tazo ta samay ki a daga baya.
AA ya shigo ke nan yana kokarin shiga wanka sai gata ta shigo a hasale tace samad abin naku har yakai can kaba wanan yar iskan motar ka tana shiga don an mai dani banza ko may ?
Amma dai kin san ita din mata tace don haka tana da iko da abina kamar yadda kema kika matsa sai da kika dauki wanda nake amfani dashi a baya.
Tace ke nan don taga na dauka yasa ta dauka yace a ganin ki ba mota dai nawace don haka banga dalilin zuwan ki nan kisani a gaba ba haka.
Yana fadin haka ya shige bandaki ya barta a wurin ina sam wallahi ba zai yuyu ba ta shiga motar dani ban shiga ba yana jin ta tana haukan ta ya kyale ta.
Part dina ta nufa sai ganin ta ta fado muna lokacin ina rungumay da yar ta sadiya ina bata abinci tace ke bani key din motar da kika fita dashi.
Ke kina da hankali kuwa zaki fado min daki haka kamar mara hankali idan kina da karfin kwata kizo ki kwata an ki baki din mota kuma ta zama mallakina daga yau.
Na gane kina jayayya danine a gidan nan nace ashe sai yanzu kika gane hakan ke jayayya ai ya kare tunda na mallaki abinda ke kika kasa mallaka din.
Tace kina nufin don kin haifi na miji gidan nan har zaki min gori a kan hakan nace kaji jahila haihuwan namijin kuma shine abin tsone maki ido ni ban kai can ba.
Bani shige ma Allah a gaba idan kina da karfin kwatan key din kizo ki diba na karfi ne a hannuna kaji min mata ko kin ki ko kin son abin miji na kowa ne a gidan nan.
Barin fada maki tace duk yadda kike gani kin kai ga shige shige a gidan nan na damaki na wuce gurin nace may shige shigen naki ya haifar maki ban da saki.
Ni ga Allah na dogara da alamarina ke da kike ganin wani zai baki abinda Allah bai tashi baki ba sai kije kitayi mota dai ce sai dai ki mutu a kan shi.
Tayi zage zagen ta ba wanda ya kula ta Altine ce taso kula ta tunda na daga mata hannu tayi shiru bata kara tanka taba har taci tagaji ta fita kowa yai banza da ita.
Yana zaune sai gata ta dawo cikin tsawa ya kore ta a dakin yace tasan shi tasan halin shi zai saba mata yanzu akan maganan nan idan ta damay shi.
Da mamaki take kallon shi tare da tunanen irin kudin data kashe a kan shi gashi komai sai kara lalace mata take ganin yana yi a gidan tun daaowan nata.
Fitinan yau daban na gobe daban duk dako malam yace zata ga canji sosai a gidan idan ta koma ba abinda ta gani daga cikin aikin malamin sai sa, an dawowa gidan kawai data gani.
Daki ta koma ta kira malam Yalliyan tana fada mai halin da take ciki yace har yaushe ta koma gidan idan da bai mata aikin kwarai ba har yaushe zata koma gidan.
Hakkuri ta shiga bashi akan gajin hakkurin da ta gani a gidan ta kashe wayan tana sauke ajiyan zuciya tare da tunanen wani mataki zata dauka kafin maganin ya fara mata aiki kan wanan yar iskan Banufar.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/16/21, 5:48 AM - Xxxxx: Har sati biyu ina amfani da motar AA bai taba tambaya na don may ba nima kuma da yake ba zama nake ba ban kula da lamarin kowa a gidan.
Yau na dawo a gajiye ba abinda nake so sai in yi wanka in dan kwanta shigana ke da wuya waka na fara yi ina saka riga sai gashi ya fado dakin.
A cikin yanayin daure fuska nagaida shi ya amsa tare da fadin may ye hujjan ki na fita kibar yaran nan a gida.
Naga ai sunyi wayo yanzu yasa na barsu tunda ina da masu kama min su a nan din don wahala nake dasu idan na fita gashi satin nan duk bamu zauna a cikin sulchool ba tun wancan satin muke shiga kotu.
Ban dai son hakan may yaran zasu hanaki yi idan kin je dasu din tunda ba ciki zaki shiga dasu ba ya fada cikin daure fuska shima.
Nace don ba kai suke tsotso ba amma barin su gida aiko su saukin su ne hakan nagani zaki fasa fita ke nan muddin kika ce ba zaki fita dasu ba kuwa.
In fasa karatu fa kace yace haka nace don naga kin dauki karatun fiye da komai a zuciyar ki yara kan a gida zan barsu don shine sauki a gare ni yace ki barsu din idan kin isa.
Washe gari na fice ba tare da yaran ba kira uku nagani nasa ban daga ba sai da aka gama wani sharia da muke saurare na fita na kira shi.
Yace may na fada maki jiya khadija nace may kafa da min fa yace ban ce kada ki fita gidan nan kibar yaran nan a gida ba.
Nace ka fada min to don may kika ketare doka na tunda kin nuna ban da muhinmanci daga yau ba zaki kara fita ba wayan na kalla ba tare da nayi magana ba sai na kashe wayan.
Mamaki ne ya kamani don naga dai karatin nan da abina ya ganni ciki don may yanzu yake son tsiro min da wata fitina kuma.
Duk abinda akeyi sai faman tunane nake a raina karshe dai na yanke shawara da zai fitar dani ba tare dana fada ma kowa ba layin Alkasim na kira.
Don tunda ya kare COE mina yake zaune gida ba aikin yi shi nakan kira idan ina da bukatan wani abu nace kada ka fada ma kowa zaka zo wurina ina son yau ka shigo Abuja akwai inda zaka kai ni.
Mun fito ban tsaya ba na nufo gida direct tsab na shiga shiri ba tare da kowa ya gane mai nake shiryawa ba komai da zan bukata na saka a mota da sunan zan kai wanki.
Alkasim ya iso ya sanar dani nace ya samu hotel ya kama da asuba zan fito mu hadu hanya na koma kamar ba komai naci gaba da mu,amula na da mutane.
Ya dawo yazo part din ina zaune ina ba yara nono ya su Altine suka shiga gaida shi da dawowa ya kalloni tare da fadin kin mai da magana na zancen banza ko?
Na dago kai na kalle shi tare da mayar da kaina ga yarinyar dake shan nono bance dashi ufan ba ganin haka su Altine suka mike suka bar wurin.
Kara matsowa yayi inda nake tare da rage tsawon shi kadan ya fara zazaga masifan shi tare da kara nanata min ba inda zan kara fita in bar mai yara da wahala.
Ido rufe nace kai nagaji da wanan auren wahalan nagaji wallahi don ina gidan ka sai ai ta min abinda aka ga dama don kawai an ga ban magana .
Allah dai yasa kasan ni ba yar iska bace balle ka dauka yawon banza nake zuwa ina barin yara a gida kasan inda ka dauko ni ka kawo ni nan don ku taru ku cuta min.
Kullun kai ke nan mutum bai maka daidai a rayuwan sa na gaji wallahi da karatuna ka ganni ka ce kaji ka gani yanzun na kusa kamala abina zakace wai ba zan sake fita ba.
Shiru yayi yana kallona da mamaki na yadda na buda mai wuta, don ban taba mashi irin na yau ba sai can yace idan makaranta ne na fada daga yau kin daina ke nan a gidan nan.
Tunda banga amfanin karatun da kike yi ba karatu kika zo yi ko zaman aure a gida don haka na kashe wanan karatun
Na share shi ba tare da na kula shi ba ya gaji ya fita daga part din wani irin hawaye ne ke silalowa daga idona .
Altine ce ta fito ta samay ni a haka tace asha khadija halin namiji kike ma kuka tunda ya fada maki kin fada mashi sai abarshi haka.
Har ta kare maganganun ta ban tanka mata ba da wuri na kwanta don nasan abinda na shirya a raina sai sakawa nake ina kwancewa har barci ya dan sace ni asuban farko na tashi na kamala komai da zanyi.
Zuwa karfe bakwai nace laraba ta biyo ni da Alamin na dauki mami takai min su wurin mota tana fadin ko tazo muje don babu mai kama min yaron nace yanzu zamu dawo ki jira ni ba dadewa zamuyi ba ai.
Tace Allah ya tsare nace amin ta aje min yaran a jiki na bar gidan karan bude get din gidan yaji sai dai yana mamaki wanda ya fita da safe haka don yasan yasa muna dokan talala a gidan.
Ita Nafisa ya hanata fita ko ina tunda ta dawo haka kuma ni ya kashe min fita makaranta wanda nasan yayi haka ne don kawai ya gyarawa matar sa rai a kaina.
Don haka ne ban yarda ba da wanan dokan da ya kafa min zai min salalan tsiya da karatuna gashi muna gab da gamawa yanzu.
A inda nace Alkasim ya jirani na samay shi tsaye yana jirana na fito na bashi key muka dauki hanya sai jahar kebbi jahar da dagani har shi bamu taba zuwa ba labari kawai muke ji.
Sai da yagama shiri ya nufi wurin nafisa suka gaisa yayi sallama da ita ya fito zuwa part dina sun gaisa da su Altine ya nufi kofana dake rufe Altine tace dashi na fita tun da safe ai.
Ya tsaya yana kallon ta da mamaki tare da tambayan yaran fa tace dasu ta fita yakai kofa ya juyo tare da fadin wa zai kama mata yaran a can da bataje da ko gudan ku ba ?
Altine tace zancen da muke ke nan yanzu ka shigo kila dai ba makarantar ta shiga ba sai dai in wani wurin ta tafi kai ya girgiza yace yayi kyau ya fita.
Yana jin zafi a ranshi wayan shi ya dauko yana neman layina akace a kashe wayan yake bai kawo komai a ranshi ba ya wuce zuwa office.
Tun muna tafiyan dadi har kowa ya ja bakin shi yai shiru a motar mun shiga jahar kebbi a nan muka fara tambayan garin KA,OJE.
Ana muna kwatance muna bi har dai Allah ya kawo mu garin lafiya da karfe biyar na yamma muka shiga garin.
Gidan Liman Hamza tsoho muka tambaya akai muna kwatance har gidan a kofan gidan muka tsaya da motar mu.
Ganin basu san mu ba aka tsaya tambayan daga ina muke wasun su ko hausa basu ji sosai sai yaren filace suke yi.
Dan gajeren bayani mukai masu suka gane nan take aka shiga muna sannu da zuwa wuri ya kaure da murnan yar wurin dan uwan su dake Niger state ce tazo gida.
Part din tsohon gidan aka kaimu direct anan aka sauke mu daga