Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MIJIN Buzuwa Complete Complete Hausa Novel by Nil

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   128 / 144

381K to 384K   out of 431K words

ringing ba ta daga kiran na fara gaida ita bata gama amsawa ba nace.
Momy akan shatu na kiraki a gidan nan don gaskiya na fahinci namu dai bai zo daya da ita ba a gidan nan.
Subbahanallahi tace tare da fadin mai yai zafi khadija ban san ki da korafi ba dole akwai abinda ke faruwa ke nan tsakanin ku.
Momy kawai dai ba zan iya zama da ita bane don kauce wa matsala murmushi naji tayi yayin da sukai shiru suna sauraren wayan nawa.
Nace momy ba zamu jittu da ita ba a hakkura kawai indon yara ne a barsu a tsakanin mu zamu rike su insha Allahu.
Tace bani Shatu din idan tana kusa zan mata magana nace momy ba sai anyi ba don na riga na yanke a raina ba zan zauna ana fitina har abin ya kai akaina ba wata rana nake ma gudu momy.
Tace zanyi magana da ita bata kusane nace eh don ban son bata wayana ma yadda nake jin zafinta a raina na kashe wayan tare da mike na nufi daki na har nakai kofa na juyo nace mama laraba kiwa Sadiya wanka don jikin ta ya baci.
Na shiga daki ya Amina na kira na fada mata halin da ake ciki tare da fadin matar nan ba abokiyar zama bane ya don za,a iya hada kai da ita gaba a cuta min tace kwarai kuwa zan samu momy in fada mata abinda ke faruwa don ta sani.
Bayan min gama wayan na jima a dakin sai da zan kwanta na fito nace Altine ku dauki yaran nan ki kwana dasu a wurin ki don Allah.
Tace angama hajiyan mu na daiyi murmushi na ce laraba ta shige min da yara daki muka kwanta ita ko tana dauka da wasa sai can dare ta fito daukan yaran basu falon duk mun shige mun rufe dakunan mu.
Don haka bata san wani daki yaran suke ciki ba da safe ban kulata ba dana shirya muka fice zuwa school bayan na yi wa laraba magana kada ta kulata don Allah idan tana fitina.
Sai yamma muka shigo gidan ihisan ma bata jima da dawowa ba gidan ina shigowa Laraba tana Sadiya wanka na leka su nafito daga dakin dakina na fada na fara kwabe kayan jikina da tare da watsa ruwa a jikina.
Sallah nayi na fito falon ban jima da zama ba sai ga Shatu ta fito tace nazo ne in baki hakkuri kan abinda ya faru jiya don hajiya Binta ta kirani.
Ni arziki nazo ci ba zuwa nayi nan don wani abubu naga kuna son hada min kai ai min bakin ciki ga samun da nake yi gidan nan.
Ikon Allah Altine dake zaune tana lazumi ta fadi nace Altine ya isa don Allah ban son fitinan nan haka na daga haka ban kara cewa komai ba.
Ta juya zata tafi tana maganganu nace shatu ki shirya da safe za a kaiki gida tace wanan kuma sai idan dan uwana ya dawo daga tafiya yace in barmai gida zan bari nace yayi.
Ta dauka wasa nakeyi da safe sai ga kiran wayan shi yace ta shirya a kaita gida zata fara magana ta kashe wayan sai da nagama shirina na fito falona na zauna ina karyawa.
Kudi da abu a leda na mikawa laraba ta ba shatu nace driver zaizo ya dauke ta zuwa kaduna har gida za a kaita daga haka na dauki hand bag dina dake gefe na rataya tare da daukan mami zuwa waje Altine ta dauki Al,amin muka fice.
Da Laraba taga mun fita an kule ko ina ta rufe kitchen ta shige dakin ta ta fito tayi cin mutunci a tsakar falon ta fice driver ya dauke ta zuwa kaduna.
Mun dawo da yamma na samu ta wuce hankalina ya kwanta dan zama da ita ba alheri bane ga yadda na hango abubuwa da dama a gareta.
A kulun muna waya dashi lafiya zai kira ya tambayi lafiyan mu mudan taba hira maganan shatu ne ya saka na kirashi kawai ranan don banson damuwan shi bansan halin da yake ciki ba.
Yau tun daya tashi hankalin shi ke wurin nafisa ya kasa zaune ya kasa tsaye duk yinin ranan ji yake yana son kawai yayi arba da Nafisa a idanun shi haka yasa washe gari ya katse duk wani abindake gaban shi ya juyo zuwa gida.
Ba wanda yasan da zuwan shi don ranan yana da kwana takwas da tafiya muna hira da dare sai ganin shi mukayi kwatsan ya dawo daga tafiyan.
Kallo daya nayi mai na fahinci akwai damuwa a tare dashi sai na dauka gajiya ne ya kwaso mun tare shi da zuwa ba wani walwala a tare dashi ya juya ya nufi part din shi.
Wanka ya fito mun gama hada mai abinda zaici na nufi gurin shi da abincin sai da nagama jera mai na nufi dakin yana tsaye yana fida riga a wardrobe din shi.
Sallama na yasa ya dan juyo gare ni nasha kwalliya a jikina na nufo shi ina murmushi ta baya na dan rugumay shi ina mashi sannu da zuwa.
Bai wani nuna jin dadin gani na ba a lokacin sai cewan da yayi kuna lafiya yana kokarin kwacewa a inda muke tsayen.
Da mamaki na bishi da kallo tare da fadin lafiya ko kake yaya yace may kika gani yana kokarin saka riga a jikin shi.
Tsaye nayi sororo ina kallon shi cikin mamaki hakan bai sa na dadara ba na bishi bakin gadon na zauna tare da fadin sai naga kamar kana cikin damuwa ?
Yace khadija ban son damuwa nan haka da yawa ki barni in huta don ina bukatan hutu ne na dan dade a zaune ba tare da nayi magana ba sai can na mike nace abinci na a dininng na shirya ma.
Yace bazan ci ba a koshe nake jin abinda yace na dago na kalleshi don duk halinda yake ciki idan nayi mai tayin abinci zai dan tsaya yaci.
Sai dai yau naga akasin hakan gare shi gashi ba fuska balle in matsa da tambayan shi na juya zan fita nace ubangiji Allah yai muna saukin koma may nene ke damuwan ka.
Nakai kofa naji yace bar abincin indan ci kamar wanda dama ya matsu in bar dakin nashi dan kallon shi nayi na juya na fita daga dakin.
Ina fita yaji ba dadi kuma a ransa sai dai yadda yake ji din fitan nawa dakin ne alheri a gare shi don wani irin haushi da takaicina yake ji a ranshi lokacin.
Dakina na koma a cikin damuwa sai dai ban iyajin zan koma wurin shi kuma idan ba shine ya nemay ni ba a lokacin cikin dare ma dana kasa barci tashi nayi na dauro alwala nazo zan tayar da sallah.
Ina kallon Labara dake barci da yaran makale a jikin ta na tayar da sallah na laraba sai barcin su suke hankali kwance a raina nace kin huta da jidalin duniya na mazan yanzu.
Salatu tasbihi nayi Allah ya ban sa, a daga laraba har yaran babu wanda ya tashi a lokacin a raka,an karshe ne da nayi sujada na dade duke ina rokon Allah bukatuna daga ciki ko har da sherin kishiya da makiya na duniya a kaina da yayana.
Ina idar da sallah na mike zaune ina ma Allah kirari da sunayen shi tsarkakkaku na dade a wurin kafin in ji kukan mami dama itace mai kwakwan shan nonon dare.
Kukan ta yasa laraba falkawa daga barcin tana dan bubugata nace ta miko min ita a inda nake zaune ga kamashin turare ya karade gurin yana tashi.
Nakai wani lokaci kafin mu koma saman gado da yarinyar mu kwanta da gari ya waye ba school zan shiga ba don weekend ne na kwanta ina ramuwar barcin da ban samu ba da dare.
Sai dai ina jin zuciyana wasai don ba kunci a tare da ni ko kadan a lokacin da ko har jin wani iri nake tun abinda yai min a dakin na fito idan natuna kamar nice bai son gani lokacin.
Gashi ban san abinda ke faruwa dashi ba sai dai hango tsanana karara a fuskan shi da kwayan idon shi a lokacin can cikin barcin dana samu mai dadi nake jin ana dan ja min kafana.
Zubur na bude idona na sauke a kanshi inda yake tsaye yayi kwaliya da gani wuri mai muhinmaci zai tafi lokacin .
Gyara kwanciya na nayi ina fuskantar ya dube fuska a daure yace tashi magana nazo muyi dake jin haka yasa na tashi kaina babu dan kwali ko hulla sai gashina dana daure a baya da ribon sai wanda yadan zubo min daga gaba kadan ina gyarawa.
Ganin na natsu ina sauraren shi don jin abinda zai fada min din nasan abune mai muhinmaci daya shafe mu nidashi.
Ganin na dago ina kallon shi yace Niger zan tafi yanzu in dawo da Nafisa don zata dawo dakin ta wurin yaran ta dani.
Allah ya tsare hanya nace mai ban kara tanka mai ba yace ban son ki dauki dawowan ta da wani fahinta don dama kin san komai.
Nasa kuwa sosai Allah yasa aje lafiya a dawo lafiya na kara bashi amsa tsaye yake a kaina komay yake tunane ban sani ba yaga ina kokarin tashi saman gadon daga zaune.
Sai da na mike da kyau nace mai ko wani abin ne kuma don zan shiga ban daki in watsa ruwa ajiyan zuciya naji ya sauke yace zan kara rokon ki idan Nafisa ta dawo gidan nan ban son tashin hankali don Allah ku barni in huta please.
Ka san ni da tashin hankali ne yaya AA inda dai zaka ya kamata ka tsawata tun a can amma ni may ye nawa na wani tashin hankali kuma.
Tare fa na shigo na samay ku a gidan nan idan naga abin da bai min ba ba matsala bane sai in tatara nawa i nawa in kara gaba inda nafi wayau a zauna lafiya idan dai nice matsalan ku dama.
Wanan kuma wani zance kike son ki dauka kuma ni dai kinji abinda na fadi yanzu na tafi a sauka lafiya na bashi amsa dashi ban iya shiga wankan ba na zauna a bakin gadon.
Tunane nake wanan abin ko na kai sake ne ko kirane dabara ya fado min na jawo wayana dake gefe na kira kakana Bado bayan mun gaisa nake fada mai matsalana.
Yace duk da dai kina kirana akaikai nasan wanan kiran na yau ba banza bane nace kamar ka sani tsoho don wallahi abokin nan dai naka ke son ya dauko min wani fitina kuma.
Yace na sani dama kuma na fada maki zai dawo da matar shi kada ki tayar da hankalin ki ko kadan halinki nagari gare su ba zai barsu su samu nasara a kanki ba da yardan Allah.
Ki bari ta dawo din mu ga abinda zata dawo dashi idan zai yi tasiri a kan ki ke dai ki dage da rokon Allah zan sa ai maki saukan alkurani anan da sadakoki yadda ya dace ayi.
Godiya nayi mai mukai sallama bayan yan nasihohi da yai min akan zaman aure da hakkuri tare da kawar da ido ga komai don aikin asiri bamai dorewa bane yace ko anga nasara akan shi na dan lokaci ne kadan.
Idan da hali yace kwana nawa nake zaton zaiyi a can nace bai wuce kwana biyu Bado yace barin gani idan zai yuyu zan shigo gaein naku yau din nan insha Allahu.
Haka yasa naji dadi muna kashe wayan na ji kamar na kara samun warakan da kunan da zuciyana ke min a lokacin
Mikewa nayi nashiga wanka na fito falo wurin su Altine muna hira tana tsokana na wai taga mijina ya dawo yana daure fuska yau ko ba an da take mai yaki karba mata.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/12/21, 6:57 AM - Xxxxx: Murmushi na sauke a fuskana ina sauraren maganar Altine yayin da cikin zuciyana nake dauke da tarin damuwa ina ji wani iri a raina sai dai ban baiyana hakan a fili ba ta yadda zasu fahince ni.
Nace Altine dan uwan ki ba hushi yake yi da mu ba, damuwa ce tayi mai yawa yana da tarin damuwa yana cikin wani hali da yake bukatan adduan ku a yanzu.
Da sauri ta dago daga ita har laraba dake ba Alamin ruwa tace cikin nuna damuwa ga magana na tace may ke faruwa dashi ne haka wallahi nima naga alaman hakan a tare dashi ai.
Nace buzuwa tayi kiran shi tun daga Canada ya juyo ba shiri zuwa Niger yana can ya tafi ya dawo da ita zuwa jibi nasan zasu iso nan din insha Allahu.
Sai naga Altine har laraba sun wani dafe kirji a cikin damuwa da firgici suna hada baki wurin fadin zata dawo fa kika ce hajiya ?
Nace kwarai kuwa don ko har ya tafi can din don yazo da ita din sai dai idan wani akasi aka samu ne zai sa ba zai dawo da ita din ba.
Nan dai suka shiga fadin albarkacin bakin su akan zancen ni dai ina zaune ina sauraren su ina nazarin maganan su ban yarda na nuna masu damuwa na ba a fili.
Don su din duka dangin miji ne a gare ni watarana nakewa gudu akan su don abu na iya juyewa a tsakanin mu kamar yadda shatu tayi min zuwanta.
Don dangin miji ba abin yarda ba ga matar dan uwan su idan mace nada hankali don duk yadda suke sonta suna da kyashi a kanta a zuciyar su sai dai abar na ciki a ciki.
Ban yarda su san sitin na daya shafi rayuwana sai dai abinda ya shafi cikin gida da sauran su na zahirine zamu zauna muyi hiran shi dasu.
Don kada in shiga daki zuciya ta ta hana ni barci yasa na daure na zauna a falon dasu suna debe min kewa akan damuwan nawa.
Mun kai wani lokaci a falon muna zaune can waya na yayi kara na dauka tsoho Bado ne a layin yana fada min suna hanya zuwa wurina yau yana son min kafi a gidan.
Nace Allah ya kawo su lafiya yace amin muka kashe wayan fita nayi na zuwa bakin get na samu Sanusi security don shi namu yazo daya dashi sosai a gidan.
Nayi mai bayanin komai yace kada in damu idan yazo zai san yadda zai kula da sauran kada su fahinci wani abu akai nayi mai godiya na dawo ciki.
Shi da kansa ya gyara inda kaka Bado zai zauna idan yazo din ya fada masu oga yace bako zai zo su kula dashi idan yazo.
Wurin uku na rana Bado ya iso tare da Al,kassim dayai mashi jagora zuwa gidan namu don shi yasan gidan sun samu taro sosai a wurin mu tunda Bado ya shiga part din naje na gaida shi bai fito ba yana ciki yana aikin da ya kawo shi sai faman fadin yake ayyah kai kasa haba haka da yawa abin yai yawa a gidan nan.
Nidai ba sanin abinda yake nufi nayi ba sai dai binshi da idanu kawai da nake yi.
NIGER REPULIC
Ta gama shiga da fice tana sauraren zuwan shi kamar yadda Yalliya mai magani ya gama tsara mata zuwan shi a duk inda yake a cikin satin.
Ta fito daga cikin dan bukkan gidan su ta zo bakin layin su ta sai dan abinda zata karya dashi don tun safe bata kai komai a cikin ta ba don babu abinda zata ci.
Tafiya take a hankali wasu mata biyu da suka santa suka dan gwauta juna suna gulmanta tunda suka hangota tafe da yar leda a hannun ta.
Taji abunda suke fadi duk da bata ji sosai ba tasan gulman ne akan yadda ta lalace ta zabge kamar ba ita ba ce ke zuwa da motoci tana yadda taga dama a dan kauyen nasu.
Wuce su tayi ba tare da sun gaisa ba duk da tasan su dariya suka saka ta juyo tana kallon su rai bace kamar zatai masu magana sai dai ta kyale su.
Don fada yanzu ba nata bane abinda ke gabanta ya ishe ta a lokhaka ta koma ta dan samu dan kwano ta zauna a tsakar gidan nasu tana cin dan abincin su na kauye data saye.
Fatiha ce ta fito ta kalli yar uwan nata tace dama daga kin gaskiya sai bata kina cikin rufin asirin ki babu ne baki samu a gidan ki.
Kin dauki son duniya kin dorawa zuciyar ki yanzun da haka ta cika dake wa ya kwana a ciki ke kin rasa muda muke ci a inwar ki mun rasa.
Babu takaici kamar yadda kika debo mai kaya kika sa aka tozarta mu a kasan da ba namu ba yanzu ban san da idon da zan kalli mijin ki dashi ba.
Nafisa da sai abincin ta take ci bata kula yar uwan nata ba sai can dai tace Saboda wanan abinda ya amshe ban tsira da komai ba nake son komawa in debi rabona sai nayi mashi tas zan barsu da takaici.
Kallon ta fatiha tayi tace

128 / 144

Chapters