MIJIN BUZUWA complete Hausa Novels.txt

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   4 / 144

9K to 12K   out of 431K words

Inda key din yake na nufa in dauko mata na mika mata leda daya ta aje min daga cikin ledejoji dake rike a hanun ta nace lah dakin dauka wallahi na fada maki ai ban son komai daga irin abinda kike dawowa dashi.
Lumshe idon ta tayi cike da jin takaici na tace na sani amma wanan ba inda kike zato na samo shi ba sako ne da samu an kawo min daga gida naga idan na barshi ma a hannu na baci zai yi shiyasa nace bari kawai in mika maki.
Ledan nabi da kallo a raina nace watau sakon da iyayyen ta suka aiko mata dashi bai da wani amfani a gare ta sai na mazan da take bi ke nan.
Karban key din ta tayi ta fita dakin na bita da kallo tana saye da kayan da ya matse mata jiki sosai ga kitson kanta da ta sako su har kafadan ta.
Tsuki nayi na shimfida anbin sallah na tayar da sallah na na idar na koma na jingina da katifa na ina jan casbi a hankali waya na dake gefe yayi kara a lokacin.
Number ne ba suna na daga ina mamaki waye mai wanan special number yake kirana kuma kusan kiran zai katse na dauka.
Da sallama a baki na sai naji shiru kara maimaita sallaman nayi wanan karon sai aka amsa min a gadarance kamar naso in sheda mai kiran amma na kasa canka.
Shiru har lokacin na sake cewa hello naji ance ina jinki nace wai waye please ko wrong number aka kira ne yace ke kina magana da Abdulsamad Abdulrahim ne .
Nace waye haka kuma bazaki sani ba don ba lallai ne ki sani din ba nace kai ta shafa wanan kuma banda lokacin irin ku haka kuke kiran mutane don bata masu lokaci kawai.
Ke ban son rashin kuyan da kika iya ke har a wayan ma sai kin nunawa mutane halin ki ba wani abu yasa na kiraki yanzu sai don inji wayarasu hajiya ta tafi zariya.
Au kace min miskilin mijin buzuwa ne nikan ina zan sani kaji ka da wani magana ni zaka tambaya wa hajiya ta rasa kuma ?
A har zuke yace eh don a bakin ki mukaji ta tafi zariya shiyasa nake son jin wanda muka rasa din bawai na kiraki bane kimin rashin kunya.
To ban sani ba kuma kada ka kara kiran layi na kaji na fada maka zan kashe nace wai ma a ina ka samu layina dan fitina ?
Wanda kika ba ya bani layin ki mara kunyar yarinyar kawai zaki gane baki da wayau idan na kama ki don naga rashi kunya yana nema yakawo kaina.
Kit na kashe wayan ban bari ya gama fadin abinda yake fadi ba don ba zan iya tsaya in saurare shi ba nace wanan wani iri fitina ne kuma?
Ina ruwan shi dani da zai wani bugo min waya wai yana tambayana wa mahaifiyar shi ta rasa da ta tafi zariya gaisu dan rainin wayau shi ba danta bane baifini kusa da ita ba waini may hadina da wa yan nan mutanen ne haka da suke son su shiga min rayuwana ina zaune kallau.
Shiko a ban garen shi ji yayi kamar ya samay ni ya fafala min mari ya sauke haushi yaya akayi ne na raina shi haka ne.
Yaja tsuki ya fara laluben nomban mahaifiyar tashi dole ba don yaso ba yaji may yasa har abu na faruwa irin haka take nisan ta shi da ita duk da yasan fushin da hajiyan keyi dashi a kan Fati ne ba komai ba.
Kamar bata dauka ta dauka tare da fadin sallamu alaikum ya karba mata a cikin ladabi sai ya fara gaida ita bayan gaisuwa ne yace cikin kwantar da murya hajiya naji ance anyi maki rasuwa a gida kin tafi ?
Eh haka ne nayi rashi amma ni ya shafa ai rashin da nayi don jin ka baida wani amfani a gareni inda dai dangin ka na kauyen maradi ne da ka tafi ko tuntuni.
Shiru yayi yana sauraren zafafan maganan da mahaifiyar shi take fada mai tace wai tunkuna ma wani dan karabanin ya fada ma nayi rashi a dangina har kaji duk da nasan ba kiran mutane yanzun kake yi ba buzuwan matar ka da dangin ta sun ishe ka.
Hajiya kiyi hakkuri nima a wurin yariyar nan Yusuf ya jiyo muna shine nace ba a fada min ba tunda har zaki je zaria ki kwana biyu haka ba karamin rashi kika yi ba.
Tace wace yarinya ke nan kake magana a kanta yace yarinyar da kika hadamu da ita kwanaki muka taho abuja sai dai yarinyar bata da kunya ban gane inda maganan ta ya dosa ba.
Au khadija kake nufi ko wa yace ina ganin sunanta ke nan Yusuf ya hadu da ita take fada mai yaban layin ta na kirata tana karanta min shirmay .
Tace Ladi ce matar kawun ka Allah ya karbi abinshi shine nazo ita khadijan kuma ta damu da nine shiyasa tasan damuwa na har taji.
Yanzun kai bakaji kunya ba ace wai har khadija zata ji zance na kai bakaji ba haduwan ka da yarinyar gaba daya ya canza muna kai kana ko tuna makomar ka ga Allah.
Bani ba ba mahaifinka ba duk kayi watsi da alamarin kowa kana ganin buzuwa da yan uwan ta sun isheka rayuwan duniya.
Mu din dai da kake gudu din mune dai iyayyen naka har gobe zance guda ne abin nan da ka guje mu akan shi yana nan yana jiran ka .
Sannan da kake kiran khadija mara kunya ita ma ka sa mata tsanar ne na babu gaira babu dalili saboda da tafi karfin matar son naka ko may .
Zai yi magana ta kashe wayan ta ta kyale shi ranshi yaji ya baci sosai da maganan hajiya yasan akan Fati take wanan fushin haka dashi to shi may ye laifin shi a ciki.
Hajiya suna gama waya binta ta kira tana tambayan ta ko sunyi waya da khadija tace mama ta kura tana tambaya na ke nace kin tafi zariya an maki rasuwa acan zaki kwana biyu.
Tace oho yanzu yayan ku ya kira waya wai sin hadu da yusuf take fada mai a wurin ta suke jin an min rasuwa don baida kunya har khadija taji abu ya samay ni tana jajantawa amma shi bai ji ba.
Sai kokarin son ya zagi yar mutane yake wai bata da kunya shi waya fishi rashin kunya yanzu shida ya nuna muna ba komai muke a gare shi ba.
Sun gama da binta gulma ya ci binta sai ga kiranta ina shirin kwaciya ya shigo min.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: 🧠MIJIN BUZUWA🧠

2ï¸âƒ£
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU

NOVEL DIN NAN NA KUDI BIYA DARI UKU KO KATIN DARI UKU TA WANAN ACCOUNT DIN 2254380105 ZAINAN IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KI KIRA TA WANAN LAYIN 09026931792 KO 08036959257 ASHA KARATU LAFIYA


Hayaniyar yaran da suka dawo daga makaranta ya dawo da ita ga tunen tace shike nan nawa ta samay ga Affan da dan banzan wayo kawai na shiryasu zuwa cikin gida wurin kakanin su tasan idan sunje can sa samu abinda sukaci a cikin su.
Yaran suna shigowa suka fada mata a jiki suna fadin mama mun dawo yunwa nakeji sosai wallahi karamin ya fada take taji gabanta ya fadi don hakan halin su ne .
Sai subar abinci a cooler makarantarsu su dawo dashi kuma suce yunwa suke ji halin yaro ke nan oya a cire uniform kuje cikin gida wurin su hajiya kwaci abinci a can banson yawan hayaniya yau.
Acan cikin gida kuma dawowan yaran gidan makaranta yasa hajiya ta kasa kunne taji shigowan jikokin nata da take zaman jiran tsamanin su tunda safe.
Ba afi min ashrin ba ta fara tsinkayo hayaniyar su daga kofan shigowa gidan tace a ranta nasan a rina dama tabbas hashe na ya tabbata ke nan wanan yarinyar har takai can.
Yaran suka shigo dakin da murnan su don anan kawai suke samu su sake suyi yadda suke so batare da wani tsangwama ba.
Suna shiga Affan ya cire rigan jikin shi ya rage daga shi sai singlet yana fadin hajiya maman mu tace muzo nan muci abinci a wurin ki wai yau bata son damuwa.
Yar ta Aisha ta kwala wa kira tazo ta basu abinci sai gata ta fito daga daki tana saye da dogon riga a jikin ta tana ganin yaran tace a a su Affan ne yau da rana tsaka anan zakuci abincin rana ke nan ?
Hajiya tace zuba masu Abinci don Allah ki kawo masu nan ta wuce kitchen cika umurnin mahaifiyar nata da sauri sai gata dauke da plate din abinci ta kawo masu.
Hajiya na zaune gefe ta kurawa yaran ido tana kallon yadda suke cin abincin gwanin ban tausayi dasu tunane tayi aranta da yau babu ita fa kamar yadda babu ran kakarsu ta wajen uwa yaya Fatima zatayi da wanan ukuban haka ?
Hajiya kubura da take matse ita tunda rana sai gata ta shigo wurin hajiyan da mamaki a fuskanta tana fadin yaya kin ga hasashen yana son ya tabbata a kan yarinyar nan ko sai ga hajiya karima uwargidan su tashigo a bayan su tace tabbas maganan mu ya zama gaskiya.
Ya tabbata ke nan ta ki bari yarinyar nan ta girka abinda zasuci a gidan abin har ya tashi ga ta hana mai aiki yi masu girki suci ya koma ta hana masu abinci.
Sallama ake daga kofan shigowa dayar yarinyar gidan ta leko daga kofan hajiya karima tana fadin sannu da zuwa yaya Suraj.
Bai amsa mata gaisuwa ba sai tambaya yayi ba kowa a gidan ne ina sallama gidan shiru tace suna dakin hajiya mama ina gani can yanufa dakin don yasan idan sunyi irin wanan taron akwai abinda ke faruwa da ya shafi dayan su ne don don iyayyen nasu nada hadin kao sosai a gidan.
In ka debe ko wanan ya kasance amaryan su Asiya bata gida ne a lokacin da su hudu zasu hade a dakin kofan ya nufa yana saye cikin uniform din shi na sojoji.
Sallama yayi a bakin kofan daga ciki suka amsa mashi mahaifiyar shi hajiya karima tace kamar muryan suraj nake ji a kofa yace nine ummi.
Dakin ya shiga kallo daya yayiwa iyayyen nashi alokaci guda ya gane akwai wani matsalan da suke fuskanta wanda ya shafi hajiya mama a gidan.
Gaida su ya fara yi a cikin ladabi kamar ba soja ya samu wuri ya zauna bayan sun karba mai gaisuwa.
Duban hajiya kubura yayi yace mommy akwai matsalane su Affan dake cin abincin su hankali kwance ta nuna mai tana fadin wanan fitinaniyar matar uban tasu ce kila ta rufe dakin girkin gidan ne yau ko da safe a nan suka dauki abincin zuwa makaranta.
Yanzun kuma kaga uwarsu ta turo su nan su da sauri yace ita Fatin fa may zataci to ya tamnaya yana kallon fuskokin su gason jin amsan su.
Mommy tace ai shi muke tunane a nan dafe kai yayi yace wanan mata ban san abinda take nufi ba a gidan nan tana son mayar muna da dan uwa binan.
Kada kaga laifin ta ai shine mai babban laifi mama ta fadi a hasale sai mummy tace ba yin kanshi bane yaya bar irin shuuman matan nan wallahi.
Suraj ya mike a hasale yana fadin yau sai naci mata mutunci idan haka gaskiya ne wallahi ko a gidan maza ana ma mutum horo da yunwa ne balle gidan brother za a ce anyiwa mutum haka.
Ko maigadin gida ai yana iya kyauta da abinci tunda bai rasa ba balle diyan shi ummi ta kalle shi lokacin da yake shirin fita daga dakin tana fadin ina zaka ?
Kai tsaye yace gidan zanje wallahi idan na samu gaskiya ne yau sai tabar gidan nan wallahi ummi tayi saurin cewa dashi kaifa mahaukaci ne na sani a dai karbe key din ka bude wurin shike nan.
Kasan yadda dan uwanka ke son ta hakan zai iya kawo matsala a tsakanin ku yace wallahi sai dai ya kawo ummi wanan wani irin bakin haline haka ?
Ai haka suke mommy tace mashi abinda ake mai gudu ke jan tun farko bai gane ba basu son kowa sai kan su da yan uwan su kawai wanan halin su ba wai ba.
Mama dai ta rike goshin tada hannun ta sai wanda duk yai magana cikin su ta bishi da ido kawai shine nata yayin da zuciyar ta ke mata soya a ciki tana jin wani irin ba dadi a ranta.
Yana tsaye daga kofa mommy tace bari muje tare dakai zaifi da sauri ummi tace haka zaifi kan don wanan kin san mahaukaci ne ya shawo Alluran shi ja sojoji kar yaje ya sauke wa yar mutane a kai.
Ai da zai sauke din haka zai fi gani take duk ta gama da kowa a gidan babu wanda bata iya takawa shiyasa take abinda taga dama inji mama.
Yanzun dai bari mu tafi idan munje ni zan fara shiga wuri ta inji ba asin yin hakan da tayi sai asan abinyi sukace yayi kyau hakan mikewa tayi zuwa dakin ta ta dauko hijjib din ta ta saka suka fice da suraj din a motar shi suka karasa gidan.
Daidai lokacin Abba ya dawo shi da anty amarya daga asibiti da dan ta da bai da lafiya ganin motar suraj ya gilma ya nufi gidan dan uwan nashi yasa suke mamaki.
Anty amarya ke fadin yau suraj ziyara zaikai gidan Abdul ne haka mahaifin nasu yace kila yazo ya samu Fati ta koma dakin ta ne zai dubuta.
Sai da suka shiga gidan ne suke jin abinda ke faruwa karban key anty Amraya tayi bata shiga dakin taba ta bar yaron wirin uwar gidan nata ta mara masu baya.
Sun samu kofar gidan a rufe wai taba maigadi sallahu cewa kada ya bari kowa ya shigo gidan ya damay ta don yanzu ta dawo da yarta daga makaranta zasu huta.
Da kyat ya bude masu kofa sai da suraj yayi mashi jan ido wanan abin shiya kara harzuka suraj din rashi ya baci sosai kusan a tare suka shiga gidan da anty amarya don samun delay din shiga da sukayi.
Bin gidan Suraj yayi da kallo daga sama har kasa kafin ya karasa fitowa daga motar shi cikin hasala mommy tace ashe kun dawo ke nan take cewa anty amarya tace mun dawo ina shiga ake fada min abinda ke faruwa nace barin biyo ku don ba mutunci ne da ita ba.
Anty tasan ida take rashin mutunci ta ai nika yau idan tayi min wallahi balbalata zanyi in daki banza sai dai mu rufe da mijin ta ai mun saba.
A tare suka shiga gida jin karan bude get din gida ta fito a fusace tana fadin maigadi wani dan bura, uba kabudewa, , , , , ganin su mommy yasa tayi shiru ta juya da saurin tana zaton basu ganta ba suko sun ganta.
Kafin su iso ta wuce part din ta ko da sauri don tasan ba bakin ta bane na Fati ne don ita suke zuwa gidan su .
Tunda ta sallamay sallah la,asar take zaune saman sallaya ta tun tana addua ta koma tunane ga tunanen ya bowayeta don yunwan da ke cin ta.
Sun shiga da sallaman su aka gaisu tace mommy kune tafe ashe mune fati har kasa takai tana kara gaida su cikin mutunci suka amsa mata ta dago tana fadin yaya Suraj marmari daga nesa.
Ke kin ci abinci yau ko baki ci tambayan da ya jefo mata ke nan a lokaci daya tayi murmushi tace kajika da wani magana kuma ba a gida ka samay ni ba zakai min wanan tambaya haka ?
Mommy tace Fati ba tambaya muka zo yi ba don mun san abinda ke wakana a gidan ko yau dai bakici komai ba tunda garin Allah ya waye haka ne ko ba haka ba.
Kai ta sadda kasa tace hakane mommy tace to akan may Fati zaki zauna ana maki horo da yunwa dake da diyan ko haka abincin nan akwaishi ba babuba kuma.
Mommy yau fitina take ji tun jiya data dawo ta samu na dawo gidan ta fada min bakaken magana har tana ikirarin sai na rami ya fini shan iska a gidan nan.
Shine yau da safe zan shiga kitchen na samu ta kulle komai tunda asuba wai kada a dora girki a gidan ta fadawa Laraba ni kuma ban koma ta kanta ba tunda nasan don ni tayi hakana.
Haba Fati sai ki zauna da yunwa ai zaki kashe kanki ne idan kina haka yanzu bari muje mu samay ta muji may take nufi wai.
Suraj bai bisu ba ya dan tsaya ganin Fati din yana kuma tambayan ta may zataci yaje ya sayo mata tace duk abinda ta samu yace kayan tea fa tace suna store acen muke ajewa fita ya yi ya mara masu baya.
Sun shiga da sallama cikin isa ta karba masu sai suka tsaya gaisawa da ita tunda iyayye ne su bayan gama gaisuwan mommy tace munzo ne dama muji

4 / 144

Chapters