da diban time din agogon daki naga takwas ya dan gwauta kadan.
Ban dade da aje wayan ba ya sake kara na dauko daga cikin jakka ina dubawa sunan shi na gani again na dauka tare da fadiin hello dear.
Ke ba dear ba abu kazar uban ki kada ki kara gigin kiiran wayaan shi idan kin san muna tare da ke ke har waya baki wanan matsayin da kike son kai kan ki ne a gidan nan ?
Sai da nayi dan murmushi takaici nace wani matayi kike jira kuma in kai tunda abinda ya kawo ki gidan nan shi ya kawo ni nima.
AA ne kuma dole ko kin ki ko kin do mu cudanye shi tare da ke ko kina so ko baki so yadda ya ke murzan ki haka yake murzana son rashi dole kuma anjima ki bar min shi ya murjeni son ranshi.
Karya kike wallahi karuwan cin ki bai kai can ba in fada maki sai dai kije gurin wasu su murje ki amma badai samad ba don wanan kayan yafi karfin irin ki.
Ke dashi sai gani sai hange nace a tunanen ki ke nan ruwa ya dade da gaurayewa da jini zatai magana naji ya wafce wayan a hanunta yana fadin.
Wanan wani irin hauka ne wai wanan wani shashanci ne haka zaki dauki wayana ki kirata kina zaginta wai nafisa kishi haukane halan.
Nace idan kun gama muna jiran ka please sai lokacin ya tuna bai kashe wayan ba ya kashe.
Kallon maryam nayi nace wanan mahaukaciyace wallahi bata da wayau ko kadan ana kira mata hauka yana binta.
Kara zagewa ki nuna mata ke ma fa matar gidan nan ne don Allah cire wani tsoro da kawaici ki din ga nuna mata ke ma kina da power a gidan nan.
Haba abin yai yawa wallahi har da kiran mijin mutun sai an saka mashi dokan haka kuma wanan abin yai yawa wallahi.
Maryam fitinane banso wallahi kuma shi din ya rokeni akan in dinga kyale ta idan tana yi kinga idan ina biye mata sai mu koma daidai da ita.
Tace wani ain ake kyalewa maryam wani kan idan an maka shi yafi gaban kyalewa wallahi tunda ba garejewa yake yana rama maki ba.
Daukan wa kanki mata ki a fito a gwabza tasan kema mace ne kamar ta amma wanan abin nata yayi yawa wallahi.
Maryam nima bashi ba ke damuna sai yawan fadin da take min wai ni dashi sai gani sai hange din shine yake daure min kai da ita wallahi.
Yau idan munje wurin anty Salbiya zan fada mata wanan kalamin ta sama muna mafita akan shi don fadin dz takeyi yayi yawa.
A kin san a tunanen ai tariga da ta shiga tsakanin ki dashi ba zai iya aiwatar da komai na kwanciyar aure dake ba abin da take nufi kenan ba wani abu ba.
Dariya nayi nace badai wanan mugun mijin nata ba da bai san daga kafa ga mace ba da kulun sai ya lalabe ni ya kwashi rabon shi.
Kyale ta surprise zamu bata sai tasha mamaki a gidan nan tasan an dade da tsere mata tun 1900 ita ta makara take haukanta da bugun daji.
Yana gama shiri a gurguje yasan ba abin karyawa zai samu kusan tare suka fito daga dakin sai dai ta riga shi saukowa ne ta zauna falo tana dakon shi.
Yana fitowa ya tunkari kofan part dina tace tana mikewa tsaye samad ina zaka kuma yace gun Deedar mana mu gaisa kuma in fada mata nagama su fito mu tafi.
Daga haka ya sa kai ya shiga ya samay mu muna zaune muna dakon shigowan shi dakin sai gashi gaida shi muka fara na nuna mai kamar komai bai faru ba damu.
Shiko sai kallon fuskana yake ko zaiga na daure mai fuska akan abinda tayi min din nace zamu makara sosai yau wallahi don an kusa shiga lectures yanzun haka.
Muje yace dani tare da fadin maryam kuyi hakkuri don Allah wallahi yau makara nayi yana gaba muna biye dashi muka fito daga part din.
Har lokacin tana tsaye cikin jin fitina shiga na ta fara kallo tana ana mazuru ana shahu da sunan karatu mai zuwa daukan darasine aa hakan mu da muka ga turawa basu bamu tsoro ba.
Juyowa nayi ina mata gwalo kan aiko ta fara sababi da zagi tana goranta min wai a haka zan kare yadda na shigo haka zan fita cikin labani kullun a mota.
Tundaa muka fara tafiya bai wanda yai magana a motar sai can naji yace ki shirya jibine tafiyan mu da safe .
Naa juyo nace Allah ya kaimu lafiya ya sake fadin akwai yan sayayyan da nake son ai su hajiya yau ko gobe zan turo maki da list ki duba ki gani wanda baiyi ba sai ki gyara naji nace dashi.
Amma yau ba zan dawo da wuri ba don zan tafi gyara kaina tunda muna da tafiya a gabana idan nace sai gobe zan iya makara gashi kace zan maka sayayya kuma.
Mun isa maryam ta bude motar ta fita na bude zann fita baji yasa lock din motar na juyo na dube shi da sauri.
Dan langabar da kan shi yayi yana fadin kiyi hakkuri Deedar nasan ba, a kyauta maki ba wallahi bada sanina ta dauki wayana ba na shiga wanka a lokacin.
Ai na sani nace dashi ba komai wallahi zata zo ta daina wata rana da yardan Allah kaidai kai muna addua kan hakan don Allah ji nayi ya rugumoni da sauri nace na makara fa yallabai kadubi lokaci ka gani.
Ina fadi ina aika mai da hararan wasa nace bari matar ka ta biyo ka ta ganka haka yace da haukan ta yayi yawa ai idan ta biyo ni nan.
Zan sauka yace miss you nace miss you too na sauka na rufo mai motar tare da jan guntun tsuki ina fadin munafuncvin maza kawai wani miss dina zakayi can adai tafi a hakan kawai.
Yau ma mun dade cikin makarantar don exam ne ke gabato muna baifi sati uku ba mu fara hakane yasa muke dan jimawa yanzu sai yamma lis zamu dawo gida.
A gurguje na biya gidan anty Salbiya ina sheda mata kwana biyu ba zata jini ba daga nan na wuce wurin gyaran kai haka yasani kai dare ban dawo gidan ba gashi kuma nice zan karbi girki a ranan.
A salon din shiya biya suka dauko ni muka juyo gida dasu tun a mota yake faman matse min hannu na a cikin nasa yana yaba kyau da nayi da gyaran da akai min din.
Mun shiga gida kowa ya nufi part din shi dan rage kayan jikin mu sallah nayi na fito na shiga kitchen don kada mukwana da yunwa.
Cus,cus na dafa muna sai cabage dana yanka da albasa mai yawa acikin don yaba da ma,ana mai dadi.
Soyayyan nama nayi amfani dashi sama sama a ciki ina gaf da kamalawa ne ya shigo kitchen din ya samay ni a ciki.
Saukan hannuwan shi naji a saman weast dina sai na dan zabura kadan tare da juyowa in kalleshi fuskan mu ne ya hade a wuri daya yake fadin may kikeyi yanzu anan ?
Nace abinci na hada muna kada ka kwana da yunwa ya juyo ni gare shi yana fadin wa yace dake zan kwana da yunwa bayan gaki.
Murmushi na sauke tare da girgiza kaina ina fadin kadai baka jin kunya wallahi kana wanan maganan haka a gabana.
Yace au ke kin saura da kunya na ashe har yanzu shiyasa kike son ko yaushe mu kasance a cikin duhu idan kina lalabana ko ?
Ikon Allah nine kuma nake lalabanka ma ashe bakai ba hannu na dana mika in gani idan dahuwana ya sulala yasa shi sake ni a lokacin.
Sai da na kashe gas din na gyara wurin har lokacin yana tsaye yana kallon yadda nake aikin yana tsaye ya jikina jikin shi daga kofan shigowa kitchen din.
Juyowa nayi nima ina kallon yadda ya tsaya din yana saye cikin three quarter fari da rigan armless na shan iska murmushi na sauke a fuska na tare da fadin dan gidan hajiya mama ko yunwa ne haka ya fara damun ka ?
Kai ya girgiza min yace gyara zancen kice dan gidan mommy don hajiyan mu kan na bar maku ke dasu zainab da Binta.
Nace realy yace of course don kun fini fada a gurin ta nace halin kane bata so yasa kuke yawan fada tunda ka zama yaro mai lefi kullun.
Murmushi yayi yana karasowa inda nake na fara ja baya tare da rike kunnuwa har bayana ya tsaya a jikin sink din kitchen din.
Yace fada min laifin da kika san ina mata in ji yanzu don kunfi kusa ni dai ban san ina mata laifi ba nace kayi tunane mana da kan ka.
Hannu yakai kamar zai danko ni na zille daga kasa na fice falo ina mashi dariya falon ya fito yana murmushi tare da girgiza kan shi.
Yace zan kama ki ai sai kin fada min mara kunyar karya kawai ya juya ya fice dariya nayi na girgiza kaina kitchen na koma na hado mai abinci nasa a basket .
Falo na fito nazo na shiga daki wanka nayi na fito na zauna na gyara jikina tare da shafe kusurwan jikina ko ina da turarukan da ke saman mirrow dina.
Na dauko rigar barcina na saka tare da zanin da zanyi sallah asubah dashi da hijjab na daura zanin hijjab din kuma na sa a wani jakka tare da sauran tarkace na na bukata.
Basket din na dauka na kashe wutan part din na rufo kofan gurin na nufi sashen nashi yan gidan suna falo har kullun basu gajiya da aikin saka min ido idan zan tafi gurin shi.
Yauma hakan ne ya kasance dasu kamshi da shiga na ya dauke masu hankali Ihisan ce ta nufo ni tana hausanta da ya dan surku da yaren uwarta.
Dayake akwai kaya a hannu na ban samu taba taba nadai kira sunan ta tare da dan mata wasa na wuce ashe yarinyar ta biyo ni a baya.
Ina jin suna hada baki gurin kwala mata kira ina bude part din uban ta fada ciki da gudu Samiha ce ta biyo bayan mu.
Zaune muka samay shi a dinning di ya tasa laptop din shi a gaba yana aiki a cikin sa jin hayaniyar mu ne yasa ya dago kai yana kallon mu tare da fadin wai may ye haka ne ?
Fuska a daure ya juya ga Samiha din yana fadin may kike nema a nan cikin dan tsarguwa take fadin dama ihisan ne tabiyo wanan nazo daukan ta.
Wani kallo yai mata ta juya da sauri tabar part din ni dai ina tsaye ina jera kayan abincin saman table ihisan din ke fadin Abincine zata ci.
Tare da iban taso suci yaki kulawa nina jawo ta na fara bata a baki tana ci muna hira dasu jefi jefi taci abincin sosai har uban ya tsaya yana kallon ta.
Shigowan Nafisa ke nan gidan aka fada mata yarta na sama wurina sai gata a sukwane ta fado dakin tana huci.
Ke ban yata nan idan kin yi zuciya ki haifi naki yanzun nan an gaya maki haka ake samun diyan a nakashe ko asha a ruwa.
Daga yau nayi maki kashedin taba min diyana sai ranki ya baci a gidan nan kin jawo ta nan don ki lashe mata kurwa kamar yadda kika lashe ma ubanta nashi kurwan.
To kurwan mu kur a kanki mai bakar aniya kawai kina son burge miji ai ba ga diyana zaki burge ba sai ki zage ki haifi naki ki burge shi dasu.
Hankaka maida dan wani naki kin zama bata irin macen sai ci akai masai kullun kinga nan ta nuna cikin jikin ta tace mai kika gani.
To dake dashi a gidan nan sai irin haka watau hange an shigo aci gado a baza diya a gidan to gaba ba a nan ba yar iska mai kutsen tsiya mai hana farin ciki a gida.
Ina zaune na harde hannaye na saman kirji na sai kallon ta nakeyi ina murmushi mai dauke da takaici sai da ta gama nace zakiko sha kallo a gidan nan.
Idan ban sha kallo ba zan sha dariya ai ki matsa idan kin ce naci ne zakiga tsiya a gidan nan yadda kika shigo haka zaki fita daga ke sai ke wallahi.
Murmushi nayi na mike ina hada kayan abincin ta bimu da harara ta matso zata dauki yar ta data dafe uban nata ya dago da idanuwan shi da sukai ja yace kina taba ta ina marin ki wurin nan sai kin raina kan ki.
Ki bace min da gani daga wurin nan kafin in makeki yanzu yarki ce ko tawa idan kuma kika ce tak akan yar nan sai na shayar dake mamaki ke da ita sai idan ta girma ta nemay ki.
Samad akan yata dana haifa a cikina kake fada min haka idan kana son ta rike ya ai kun san yadda ake samu dan kuyi mana kusamu kuma.
Anga ya yar tubul, tubul son kowa kin wanda ya rasa ake son lashe min kurwanta watau kowa ma ya rasa ke nan ko wallahi ba zan jure daukan wanan hukuncin ba a kan ya ta a gidan.
Tana kokarin jan yar ya mike da sauri nace haba dear kabar mata yarta mana Allah yaba kowa nasa ba shike nan ba akan may za, a tsaya ana fada akan ya abinda Allah baison hakan.
Ta juyo gareni tana fadin may kike nufi da haka kanaji ko kaine sheda idan wani abu ya samu yata kotu ne zai rabani da wanan ta nuna ni.
Ta fice da diyar tana kuka wani iri naji a raina amma a fili na wayance ina fadin kai Allah dai ya kyauta naci gaba da hada kayan.
Muna kwanciya yace yarinya bagaki ba yanzu may kika fadi dazun a dakin ki maimaita yanzu mana da bakin ki.
Dariya nayi nace ai maganar ya wuce ko don munyi shi tun acan ai yace to be frack Deedar na rasa may yasa hajiyan mu take min wasu abubuwa na daban wallahi.
Nace ka fasan halin iyayyen mu da alkunyar dan fari ba wani matsala bane kawai kawaici ne take maka a hakan amma ni ban dauke shi wani abin damuwa ba.
Bazaki gane bane Deedar idan ba muna tare da Yusuf ba bazan taba ganin fara,ar hajiya a tare dani ba tun ina jin wani abu har yakai yanzun na saba da haka.
Shine dalili dayasa kikaga ina shuga da Yusuf idan zan tafi nace kai ya kamata ace ka bata hakkin ka na uwa a gare ta.
Har gobe fa kai yaro ne a gurin ta wani shawara da ita ya dace ka zauna kayi shi amma kana nuna kamar kana gudun ta yanzu da shawaranta.
Ya kamata ace kaja yan uwan haihunka a jiki ta wanan hanyar na tabbatar da idan ka gwada zakaji dadin ta sosai amma ba dadi ace naka nada shi a gida amma baiwa yan uwan sa abinda ya dace.
Sun bukaci wani abu ne a gurina ban masu ba a, a gaskiya yaya AA kasan fa irin tarbiyan gidan ku bazasu taba rokon abu ba kaima ka sani.
Iska naji ya furzar daga bakin ya sauke ajiyan zuciya yace na yarda da maganan ki don Bintace ta taba rokona in saya mata laptop tun farkon shigar su school.
Ban san abinda ya matar dani daga saya mata sai yanzun nake tuna wanan abin nace ka gani kuma nasan hajiyar ce zata kwaba mata kada ta sake ma magana tunda ta fada ma da farko.
Idon shi ya lumshe na tsawon wani lokaci shiru dakin yayi na wasun sa,oi kafin yace wai ke ina kika san wanan abubuwane haka ?
Baristet khadija Adamu ce a kusa dakai yace natuna dama ance nine farko da za a fara lauyewa idan an zama barister nace dane ai.
Yace au yanzu kin fasa ke nan nace kila don ban tabbatar ba ya kara sauke ajiyan zuciya yace think before tommorow may ya dace in wa Fauziya da Fa,iza .
Wai ka bani aiki mai wahala saboda ba sabawa nayi dasu ba kamar binta da zainab don ko gidajen su ban sani ba.
Amma ina ganin zaiyi kyau inda hali kakaisu saudiya ko ka gyara masu dakunan su da dai sauran su yace insha Allahu da halin yin duka ma don yan uwana da iyalina nake neman kudina da zufa na.
Nace amma may yasa bakai wanan tunanen ba tun farko sai yanzu yace nima ban san dalili ba Deedar yanzu dai ne da muke wanan magana abin yazo min a rai na.
Allah ya kyauta nace mai yace amin yana kamoni jikin shi dasafe da muka tashi bayan mun idar da sallah ne na duka na gaida shi kamar kulun yace kibani accout din ki zan tura maki kudi ai sayayya azumi ko nan ko idan munje kaduna.
Don ban sa zan koma ba kafin azumi Allah ya saka da