Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MIJIN Buzuwa Complete Complete Hausa Novel by Nil

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   103 / 144

306K to 309K   out of 431K words

kai yai mata yawa a rayuwa har bata iya tsinana wa kanta komai na rayuwa na ci gaba.
Sun dai dade a zaune gurin hajiyan suka mike zuwa gida ban samu shiga gaida su ba a ranan don muna gama girki nayi wanka na kwanta sai barci.
Damana na aje masu komai da zasu bukata na kuma aje na sauran mutane duk na halartawa laraba na shige na kwanta.
Can cikin barci nake jin yana ja min kafa na a hankali na bude idanuwa na sauke a kanshi yana tsaye saman kaina yace kizo zaku gaisa da childship dina mikewa nayi zaune.
Zaki iya tashi yace min na kada mai kai ya fita ban fito ba sai da nai makeup a fuskana na dan gyara tare da dora gyale a kaina.
Tun ina saukowa suka sako min idanuwa naji suna magana kasa kasa har na karaso inda suke su biyar ne bakin namu.
Ina zuwa nayi sallama tare da dafa kujaran da yake zaune a kai na zube kasa ina gaida su da zuwa tare da masu barka da sallah.
Masha Allah naji sin fada tare da fadin maye gaskiya Allah yakaimu ga danshin ka wanan zukeke haka ga ladabi da sanin ya kamata gaskiya kai muna wayo ka kuma falkar damu ko muma Niger state zamu koma ne ?
Suka sa dariya wa wanda ke maganan mikewa nayi na shiga kitchen na hado masu abinsha da naman kajin da akai pepeying sai cake din da maryam ta ai min.
Na fito masu dashi wani daga cikin su ke fadin wanan ai ba maraba da buzuwar taka har ma ince tafi buzuwan taka komai gaskiya ka gode ma Allah.
Ban sake fuska ba don maganan su ya nuna yan duniya ne ba kunya gare su ba don basuki in zauna cikin su mu taba ba idan sun hadu da yar duniya kamar su da sai in biye ai ta darawa.
Kitchen na koma bayan na gama gabatar masu da abin sha din usualy mama laraba dama kamar a kitchen din ne wurin zaman ta.
Tambayan ta nayi idan yaran sun ci abinci da suka shigo tace ta basu sunci sai dai uwar su ce bata fito ba tun dazun nace mama ki shiga ki huta daga ciki mana.
Tayi murmushi tace ai banda hutu yar nan kamar can umurni ne haka daga uwargidan nan tace in dinga zama nan kusa da kitchen kada in nisa da nan irin wanan lokacin .
Na juyo nace haba mama mutum ai anason shi da hutu wanan aikin da muka sha kuma ba zaki zauna ki huta ba hakana.
Ta danyi murmushi tace haka na saba ai shiyasa da naje guri ki can ai naji daban do kin dauke ni kamar ta jikin ki.
Mama kada kice haka ke fa uwace a gare mu kuma ko banza ma kin haife ni don haka ki bar wanan tunanen ki daina daukan kanki a matsayin yar aiki a gidan nan ke uwa ce a gurin mu.
Muryan AA ke kira na daga falo na amsa da naam na nufi falon wurin su tire din dake gaban su yace in shiga dashi ciki na kwashe kayan zuwa kitchen.
Dakin anty na shiga na samay ta a kwance tana waya nace anty baki fito ba har yanzu abinci fa ko a kawo maki nan daki ne ?
Tace bayan amsa sallaman barshi ai yanzi zan sauko idan nayi wanka nace to barkan mu da sallah Allah ya kara maimaita muna tace amin daddy nagani yana barci a kasa nace daddy barci kayi ne ai na dauka kana gurin hajiya ne tace yana nan tunda suka dawo yaci abinci yazo ya kwanta.
Ban san sun dawo ba fa su nake jira su dawo muci abinci ashe har sun shigo ina barci na fita bata kara min magana ba dai.
Inda na idar da sallah ina zaune AA ya shigo da kudi masu yawa a hannun shi yana fadin bakin ki sun wuce sunce a baki wanan yana miko min kudin.
Anty ya kamata kakai wa nace dashi wani kallo yai min ya nufi gado yana aje min kudin tare da fadin idan kin ga zaki iya bata sai ki bata wanan dai ni ke sukace a bawa na dawainiyar da kikai masu ne .
Ya fice daga dakin ina idar da sallah kasa na sauka muka gyara ko ina na gidan har kitchen na feshe ko ina da kamshi ferfesu na dora don nasan ba abinci za a iya ci ba da dare.
Four ya gauta na gama komai na dawo na shiga wanka na kara sa wasu tufafi sai dai kayan nawa nasaka wanan karon don atamfar da na saka ya damay ni.
Rigar yai matukar karban jikina har zaka iya gano cikin jikina da ya baiyana yanzu falo na sauko muka zauna da mama laraba muna hira.
Binta da zainab suka shigo gidan muna ganin juna muka dauki ihu dasu sai kuma na juya da fadin Binta ai nayi fushi tace tambayi zainab Abba ne ya hanani zuwa.
Saboda gidan ku baida dadin zuwa ga mutum don babu kwanciyar hankali inji Abba nace kada ki dorawa Abba laifi Binta tace kin tambayi zainab idan baki yarda ba.
Mun gaisa na mike na shiga kitchen na hado masu tire na kawo gaban su na aje ina zama Binta tace ashe abin har ya fito haka ne ?
Nace ya fito sai ki shirya dama kece uban shi ai tace ko yanzu shiga daki ki haihu ki gani idan banda shiri nace uhumm kwana nawa ne Allah yasa Abba yace auren ki dana zainab za a hada inga tsiyar wanan bakin.
Muna gidan tare dasu har dare sai da sukayi sallah isha,i suka tafi tafiyan su da kama minti biyar bakin mu suka shigo gidan.
Ina kara gyara falon babu sallama sai ganin mutum nayi ta fado gidan har na firgita nace a, a sannun ku da zuwa ashe kuna hanya tafe ?
Kamar ba zata karba min ba sai kuma naji tace eh Ihisan na gani na tayo gurina da gudu ta fada min a jiki nace Ihisan nayi missing dinki.
Wani yare taiwa yarinyar naga ta kara makale min a jiki na rike ta tare da fadin tafi gun mamaki kinji.
Sama ta nufa ta bude dakinta ta shiga ruwa na dauka damai sanyi da mara sanyi nakai mata a dakin sai dai ban shiga daga ciki ba.
Yanyala ta fito ta karbi ruwan tana fadin angode na juya na fito Ihsan ta kara biyo ni karo na biyu muka sauko kasa.
Nan suka hade da daddy suna wasa irin ta yara Anty Fati da tun safe sai wanan lokacin ta fito muka gaisa ta kalli yarinyar tana fadin wanan fa?
Nace yar gurin Nafisa ce yanzu suka iso tace cikin wani irin yanayi ai sunzo ne suma ina Affan yace min basu gidan koda kuka taso.
Nace haka ne daga shi ban kara magana ba ita ma haka ta zauna tana cin abinci da bataci sai yanzu da tafito din
Sai tara ya shigo gidan yana shigowa idon shi akan Ihisan ya sauka yace ke kedawa kika zo tana ganin shi ta ruga wurin shi ta rungumay shi.
Hannun ta ya rike suka hau sama zuwa dakin su a daidai lokacin Samira tafito tana ce min anty Abinci yunwa nake ji tare da zama a hannun kujaran da nake zaune rabin jikin ta a nawa.
Nace barin hada maki kikaiwa wa su Ami din ki ko tace No a nan zaci gurin ki tana gyara zama kitchen na nufa na hada masu abinci naba ta takai lokacin yana tsaye suna fafatawa da ita a gurin.
Yana zuwa ya tura kofan tana zaune tana waya saman gadon ta yace ke wa ya baki izzinin shigo min gida cikin iyalina ?
Banza tayi dashi sai da ya kara maimaita abinda yace mata din ta juyo tana fadin naga nims gidan miji nane kuma gidan uban diyana.
Rai bace yace ku fice min daga gida kafin rayukan ku ya baci yanzu awanan lokacin samira ta shigo da abincin dakin ya bita da harara.
Tace gidan miji nane don haka babu inda zan tafi yace ok haka kika ce tace eh yace ok barin zo yanzu ki gani ya juya ya fita.
Kallon abincin tayi tana tambayar yarinyar wa ya bada abinci tace anty ce tace in kawo maku wani irin bacin rai taji a zuciyan ta cikin yare tace yar iska munafuka zanyi maganin ki a gidan nan.
Yana fita ya kira waya ba,a dauki lokaci ba sai ga yan sanda har biyar mata biyu maza uku sun shigo gidan kai tsaye yana gaba suna biye a bayan shi
Muna ganin haka muka bisu da kallo yaran dai suna gurina suna cin abinci hakalin su kwance can mukaji hayaniya daga sama inda dakunan suke.
Nan yan sandan mata suka taso su a gaba kamar a falki sai ga Nafisa tana share hawaye yanyala na goye da yar baby a bayan ta Nafisa ce a falon ta kalli yaran take fadin su taso Samira tace Ami na gaji da wanan yawon haka ku tafi ku barni gurin anty don Allah har ku gama.
Yace maza ta tashi tabi uwar ta da sauri nace please yaya kada kusa yara a cikin zancen ku dan Allah wani kallo ya watso min sai da na dukar da kaina kasa.
Ya kuta ya bi bayan su tana kan zagin shi na fitar arziki Allah ya kyauta nace Anty Fati daga inda take zaune take fadin Allah nagode ma da ka nuna min wanan ranan da raina da lafiyata.
Can rikici ya kaure masu tace bazata shiga motan yan sanda ba tunda gidan shi yace ta fito ta fita ai sai da yaga wucewanan su daga unguwar ya koma cikin gida bai tsaya falon ba ya shige dakin shi muna zaune munyi tsit a inda ya barmu zaune sai dai wanan karon ihisan ta gama cin abinci ta kwanta tayi filo da jikina da ita da daddy.
Ashe bata wuce ba Family house din su ta shiga gurin iyayyen shi da kuka tace tazo ya kore ta gidan shi ko tausayin yarsu da take fama da ita baiji ba.
Don inda yanyala tabi tanata da sun bar yar a gidan bata tafi da ita ba ga yarinyar tana callara ihu gwanin ban tausayi amma haka ya rufe ido ya kora su daga gidan.
Mommy hajiya mama ta aika a kira don dare ne kowa na part din sai ga mommy don binta ta fada mata ga buzuwa tazo yayan su ya korata daga gidan shi.
Har su umma an kira sun zo da anty amarya Biinta ta shige daki ta kira yayyun su tana labarta masu dan abinda ta sani daga cikin zancen.
Mommy ne tayi karfin halin magana bayan ta karbi yar daga hannun yanyala ta dubata tana fadin Allahu Akbar Allah mai iko sai kuma ta dago kai ta kalli nafisa tace
To Nafisa abinda ake gudu ke nan ya faru samun wuri yasa kin wuce iyakar ki kina taka kowa yadda kike so baki tuna akwai Allah.
Nan muka je gaida ke akan lalurar rashin lafiyan cikin yarinyar nan kika rufe ido kikai muna cin mutunci a gaban kawayen ki da kowa.
Mu dai mun san babangida namu komai ko ya faru bazai taba kin mu ba don mune dai iyayyen sa mudin da kika wullakanta.
Yanzu kuma ki dauko kafan ki kice kin zo wurin mu wai neman sulhu ko kin manta da maganar ki na ranan da kikayi akan zuwan mu.
Anty Amarya tace irin wanan ranan akewa gudu duk abinda bawa keyi Allah yana kallon shi ai don yanzu tun a duniya Allah yake fara hisabinsa.
Ke baki zauna lafiya da miji ba, haka kuma yan uwan zama ki baki zauna lafiya dasu ba kin bi gida duk kin burkuce mai da bakar fitinan ki.
Ga magana suna ta zuba mata babu daman ta basu amsa don ita yanzu bukatan ta kawai a samu a shawo mata kan Samad din ta takeyi daga baya sai ta san abinyi.
Hajiya umma ne tai magana karo na farko bayan ta gama kallon yar tace yanzu da kika zon nan din may kike son muyi maki ?
Wanda ke zama dake ya gaji da halin ki yace baiyi mu may ye namu a ciki ko lokacin da ta auro ki ya kawo ki gidan shi mun sani ne ?
Ba irin wullakancin da baki wa yaran gidan nan dama yan uwan mijin ku suda gidan dan uwansu kin hanasu zuwa kin tare gaba kin tare baya.
Yanzu ki koma don mu ba abinda zamu iya maki tunda kince ba son ki muke yi ba sai kije gun masu son ki su gyara maku zancen tana fadin haka ta mike ta bar dakin.
Hajiya mama tace kin ji abinda yaya tace don haka ki koma inda kika fito yaje can ya samay ki shida yaji yana iyawa don yanzu ban san may zan fada ba don in ina tuna abubuwa raina kara baci yakeyi.
Hajiya umma ne ta dawo dakin tana fadin ki taso Alhaji na kiranki ta juya tace hajiya Binta ku taso muje gurin Alhajin .
Suka fito banda yanyala da bata bisu ta zauna a dakin hajiya mama din don ita hajiyan tace babu inda zata.
Yanyala ta kala bayan fitar su tace kunci abinci tace yanzu Dija amarya ta aika muna dashi muna shirin ci yazo ya kore mu daga gidan.
Dabiar yar uwaku baida kyau bai kuma da dadin ji samun wuri ai ba hauka bane tana ganin dama Allah bazai tambaye ta wanan fitsaran da take bane wa mutane.
Yanyala tace hajiya hakkuri zakuyi don Allah ku taimaka muna mun sha wallah sosai tsakanin shekaran jiya zuwa yau abin ba dadin fada.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Washe gari na tunda safe na hada breakfast ina gamawa na aika laraba ta mikawa kowa nasa don guje wa fitina kuma.
Girkin rana na dora don firlta hakkin mutane kada in fita banyi ba alhaki ya hau kaina a gurguje na gama komai na zuba again takai masu.
Wanka nayi na shirya na nufi cikin gidan su part part na shiga nagaida kowa na dawo gurin hajiyar su.
Mun dade a falon tare da ita tana kara min godiya irin canji da take gani a tare da dan nata take fadin sai kin kara jajircewa don wanan matar tashi ban yarda da nadamar ta ba har yanzu.
Babu komai nace mama adai taya mu da addua tace fauziya suna fada min abin arzikin da ya samay su jiya sai dai kin san ba abu bane da za ai saurin bayyanawa a fili sai in maganar ya tabbata ko ?
Nace gaskiya ne hajiya tace banson ko mommy ku taji wanan labarin sai idan abin ya tabbata gaskiya ya mika masu takardun a hannu kowa ya sani.
Don mijin nan naku ne baida tabbas a al,amarin shi yasha yin alkawari irin haka karshe ya barni ana yaba min magana a fakaice.
Mama ki kara hakkuri don Allah muma haka muke dashi alamarin nasa sai da addu gaskiya don zakaga ya bi hanya kwana biyu kuma sai ya kauce kamar bashi ba a rasa gane kan shi.
Sai naji tace Alhamdullahi dana samu wace ta fahinci hakan gare shi wanan abin yana ci min tuwo a kwarya khadija yanzu ki duba dan wurin hajiya yaya ummar ku nan.
Surajo ai ba kaishi yayi ba ga komai amma yadda yake kula da mahaifiyar shi da yan uwan shi a dakin su sai abin ya baka sha,awa ni nawa sai sunan kudi amma babu amfani gare mu daman ma yanzu ne nake dan ganin haske abin.
Tausayi ta bani yadda ta zauna tana fada min damuwar ta nasab abin yana cin ta sosai a rai tunda har ta iya zama dani tana fada min hakan.
Tace bandamu da sai yai min ba amma ya dinga kulawa da mahaifin shi da yan uwan shi bawai dole sai nawa ba a,a duk dan da ke cikin gidan nan yanzu shine babba a gare su ai yakamata ace suna alfahari da abinsa ai.
Shiru ni dai nayi ina sauraren ta tana kuma ban tausayi ga maganan ta wanda gaskiya take fada koda ba a cikin kishiyoyi ko take ba kowa nason ace nasa na kwarai ne.
Mun gama nake cewa zan leka gidan anty na in gaidasu da sallah tace to a dawo lafiya zaki leko ta nan ne kafin ki koma gida ko nace insha Allah mama.
Har na fita gidan ina tunanen wanan magana Binta ce ta rakani don zainab tana kwance tun safe wai bata jin dadin jikin ta.
A kofar gidan Ya Amina muka hade da mijin ta a get zai fita tun daga nesa yake min dariya na karaso inda yake nace ya Adam abin dariya kuma na zama gare ka ko yanzu ?
Yace mamaki nake wai yar khadijace haka ruku ruku da ciki nace ai

103 / 144

Chapters