Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MIJIN Buzuwa Complete Complete Hausa Novel by Nil

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   141 / 144

420K to 423K   out of 431K words

na kyale shi ya fita a cikin fushi laraba ta dawo min da sako na na tashi na danci na koma na kwanta .
Shigowan su hajiya mama da momy ne ya sa na tashi daga barcin da nake muka gaisa suna min yaya jikin nace naji sauki.
Momy tace baki da lafiya haka kika tafi gurin buki ai ciwo ya kawar da komai ga ran mijin ki ya baci sosai wallahi.
Hajiya mama tace tasan ba zai barta zuwa bane ta boye mai amma kuma ai lafiyan ki dana abun cikin ki yafi komai khadija kada ki kara irin wanan gangancin don Allah nan gaba.
Kai na gyada mata kawai tace zainab ma halin da take ciki ke nan ya hanata halartan bukin da kyau.
Sai lokacin nayi magana nace zainab cikine da ita ashe tace cikine irin naki itama mai wahala takeyi yanzu dai naji yace ai zaku fita ne ko ?
Don bukin nan ya dawo dashi dama nayi saurin dagowa ina kallon mama din momy tace kin san babangida ai tun da ya kafe da ita zai wuce har yaran shike nan kuma ai.
Da kyat na bude bakina nace don Allah momy a rokar min shi ban son zuwa kasan nan wallahi ya barni nan zan kula da kaina.
Basu wani jima ba suka tafi sai lokacin Fati ta shigo dakin tana fadin ashe bakiji dadi bane sai yanzu da su momy suka shigo nake ji.
Nace zazzabine naji sauki ai tace Allah ya sauwaka wanan karon Nafisa ba shigo ba wurin bukin sai lokacin nake ji bata shigo ba ashe.
Banyi mamaki ba don karamin aikin tane don ba shiri suke da Suraj din ba ko banza fa kuma maryam da ta tsana a rayuwan ta.
Don gani takw babu abinda muke da maryam sai shige shige akanta da mallake miji shine aikin mu kamar yadda take da kawayen hurdan ta.
Kwana uku muka kara a kaduna su maryam har sun bar garin ko ita da angonta zuwa cin amarcin su tun kwana biyu da tarewan ta.
Mun iso lafiya nan ma dai ba a cikin dadi nayi tafiyan ba don keta kuma ya ki saya min ticket din jirgi in bi ko da nida shine.
Tunda na dawo ban leka waje ba ina ciki kwance gashi shi ba zama yake ba don Yusuf bai dawo Abuja ba shi kadai ke komai a nan yanzu.
Ya dawo a cikin dare ya shigo gurina ya dubani sai yake fada min cewa wai zamuyi tafiya nan da kwana biyu in shirya kuma zamu dan dade a can din.
Fuska na bata tare da fadin gaskiya sai dai kaje kai kadai don ba inda zan tafi a hankan da nake ko ka dauki wata kuje tare.
Kin san abinda kike fadi kuwa ya tambaye ni ni ince kiyi abu har ki tsaya kina min korafi akai wanan tafiyan ya zama dole kiyishi don ba zan zauna acan ni kadai ba alhalin ina da mata.
Dawa kike son in wanan tafiyan cikin ku bayake duk cikin ku akwai mai ilimin da zata taimaka min da wasu abubuwa a can ne ?
Shiru bayi tunda ya fara magana don jin abinda ya fada din nace kasan wata mai zuwa kuma zamuyi buki a gida shine dalilina.
Buki ba wanda zasuyi ne idan kin tafi wai may yasa kike son ja danine kina tsanmani ko kina nan za ai bukin zan barki kije ne a hakan yadda kike din nan don haka ku shirya harsu Altine don yara zamu tafi.
Jin dasu Altine yasa hankalina ya dan kwanta da tafiyan sai dai banso rashin samun bukin yar mama Tani da za a yi ba haka yasa washe gari na tura ma mama tani din kudi masu yawa tare da bata hakkurin rashin halartan bukin da baczan samu yi ba.
Nafisa ta so ta tayar da rigima yake ce mata idan kin je can wanu aiki zaki min a can ita aiki ne zai kaita ba shakatawa ba.
Wani aiki ta iya da zatayi a can yace idan taje zaki gani lokaci ya kure mata don da bata yarda da wanan tafiyan da za ayi dani ba ta nasa a ranta.
Ba tare da na samu sallama da kowa ba mukai wanan tafiyan zuwa waje kasan hongkong muka nufa ba sai na fada maki yadda naga kasar ba kacar dani .
Sai nake ganin rashin tausayin shi da ya jajirce akan sai nayi wanan tafiyan ko ta halin kaka sai na tafi tare dashi can.
Da farko don laulayin da nake yasa banji dadin garin ba amma da bazo ina samun kulawa sosai sai na fara jin dadin yanayin garin a jikina.
Sannu sannu na gane dalilin shi na zuwa dani da farko dai doin kare lafiyan shi da mutuncin iyalin shi sai na biyu don yaran shi yana kusa dasu.
Sannu sannu alamura suka fara canzawa yayin da cikin jikina ke kara girma yana fitowa ba zan iya cewa Nafisa ta san da zancen cikin ba.
Sai dai nasan tana kiran shi suna fina kan rashin zuwan shi Nigeria din wurin ta muna da wata uku da zuwa ya barmu can yazo nageria.
Sai da ya share wata daya ya dawo gurin mu karatuna na koma ina business inda bake turowa Ya Amina da zainab dasu Faiza kaya suna sayar min a tura min kudina in sake turo wasu.
Tsayawa in fadi canzawa na a yanzu bata lokaci ne don gaba daya na sauya na zama wayayiyar mace mai aiki da zamani ga ilimi dana samu a can.
Watan cikin jikina tara yanzu ban fita ko ina sai zuwa daukan darasi kawai ke fitar dani ban ketare wata tara ba na haife dana mai kama da diyana sak yazo duniya.
Allah ya taimakeni yana kasan bai fita ba na haihu nasa rai zamu dawo gida don sunan dan sai cewa yayi ba inda zan tafi karatun yaran shi ya samu tsaiko.
Ya dai buga waya ya sheda ma mutane na haifi Abdulsamad jinior kamar daga sama Nafisa ta samu labarin haihuwa na daga bakin shi.
Ba karamin fitina tayi ba har da dan kukan ta wai ta gane dai yanzu bai son ta har nayi wani ciki na haihu ita ko bata n wata bata kara yi ba har yanzu.
Wayan ya kashe don bai iya sauraren shirmay ta yanzu ya kira fati ya fada mata tayi kokari wurin boye kishinta tayi addua akan jaririn da aka haifa din wanda hakan ya kara daga daranjanta a idon shi.
Hajiya mama da momy ne suka zo dubani inda watan su daya a wurin mu yana nuna masu gata bayan wata daya suka shirya suka dawo Nigeria,
Zainab ma ta haihu ta haifi dan ta namiji ita ma sai maryam suke fada min cikin ta ya girma amma sau daya suka zo kaduna gaida su basu sha da dadi ba wurin umma ya dauki matar shi suka koma tun kwanakin da zasuyi basu cika ba tun wanan lokacin basu sake dawowa ba inji momy.
Hajiya mama ba mau son hayaniya bane sai dai tayi ta kallon mu tana murmushi wanda hakan ke nuna farin cikin ta a fili.
Ana saura kwana biyu ta koma ne take fada min cewa sunyi magana da AA yace yana son akai su Affan karatu saudiya.
Nayi murna kwarai ya yarda da shawaran dana dade ina binshi akai ke nan sai dai maimakon ya kaisu inda nace sai canzawa yayi zuwa kasan saudiya wanda hakan yayi min dadi sosai.
Ban nuna mashi naji ba sai bayan tafiyan su hajiyane yake mun magana na nuna mai farin ciki na sosai yace zai shiga Nageria don shirn yaran karshen wata zai dan dauki lokaci don wani aiki da ake mai a can yanzu.
Ya barmu can yazo sai dai tun zuwan shi Altine ta tayar da gankalinta akan ita fa zaman garin ya isheta hakana gida take son ta dawo.
Na kirashi ina fada mai yayi mamaki yace ko dai wani abune ya hada mu da ita nace ba abinda ya hada mu gaskiya gida daine ya biyo mata a rai.
Yace a bata wayan suyi magana ya dan rarashe ta akan ta bari har ya dawo ai zamu zo gida muma bada dadewa ba.
Niko nasan dan ci gaban data samu ne yasa tayi wanan maganan don taje ta shana a kaduna asan itama ta faso gari don gwargwado AA ba maketaci bane.
Yana kyautata ma duk wanda yake kasa dashi yadda ya kamata dan kudin da suke samu ne ba basu shawaran su dinga juyawa suma suna samun ci gaba.
To wanan daman data samu take ganin yanzu ta wuce zama rainon yara ita ma zata iya tsawa da kafan ta yanzu.
Ya dawo da sati biyu tare da Anty Fati daga wurin kai yara suka wuto zuwa gurin mu, Altine ta barmu can ta dawo Nigeria wurin yan uwanta ban wani shan wahala ba don Laraba mace ce data cancanci yabo ga Anty fati ba laifi tana dan taya mu kula da yaran.
Tare muka zo Nigeria lokacin tana da wata biyu da zuwa wurin mu ko yaron dana haifa ya girma yayi wayau sosai yana rarafe ne yanzu .
Tun isowan mu Abuja Nafisa ta kyala ido ta ganmu don bata san da zuwan Fati ba hankalin ta yayi matukar tashi sosai yau tana ji tana gani matan da tafi tsana a rayuwan ta suna can ashe suna holewa da mijin ta.
Ita tana nan an yada ita kamar wata bora ko taron arziki bai samu ba a guri ta hankalinta ya tashi sosai ga yadda taji labarin nakoma da yarana.
Bai bi ta kanta ba ya fice ga dayan part din da aka budewa fati ta shige ciki shiya kara daga mata hankali sosai don bata gama da batuna ba, ga kuma wata tazo.
Wai may ke faruwa da itane haka komai nata yana shirin lalacewa gare ta sai taga kamar zatai nasara sai abu yazo gaba daya ya rikice mata.
Fatin da take ganin ta gama da batunta a rayuwan su yanzun kuma ta sake dawowa cikin lamarinta kardai aikin ta yatashi ke nan ita ma kan sanadiyar wanan fitsararan da bata jin jifa a kanta.
Daidai lokacin ne da take wanan nazarin laraba ta fito da yaran tana masu burgan turancin data samu a can tana wa yaran.
Galala Nafisa tayi tana kallon laraba ko yaran dake dan wasan su cikin rashin kula da ita a gurin bata taba nadaman rashin karatun ta ba sai ranan don tana ganin da kyau shine nasaba ga komai a gareta.
Dakin ta ta koma cike da bakin ciki da takaicin yaran data gani a jere su uku wai duk wanan yar nufawan keda haihuwan su a gidan.
Ya zama dole ta mike tasan inda take ba zata tsaya kallon ruwa ba balle kwado ya rigata tsalle haka kawai daga shigowa na har na sake diya uku tana zaune dabas.
Kaji jahila wace bata san Allah ke yi ba waya ta jawo tana kiran kande sabuwar aminiyan ta na yanzu Kande dake tare da madam datazo wurin ta maula.
Tana sauraren bayanin su da Nafisa har suka gama tunda Kanden tayi mata alkawarin zuwa Cameron kafin mu koma zata san yadda zata sai dai zance na ya sha ruwa a gidan.
Muna da sati biyu da zuwa naje gida na ziyarce su kowa yaji dadin zuwa na ya Amina tazo muka hade nan da ita ranan raba dare mukayi nuna hira da ita.
Nayi sa, an zuwa don gap da bukin yar mama Tani ta biyu ce sai na roka ya barni sai da muka sha buki muka dawo ranan Fati ce da girki a gidan na samu sun gama fitina da Nafisa.
Duk da rashin son hayaniyar ta ranan saida ta kai karshen ta sukai sa in sa kowa ya gama jin su a gidan don nafisa tace ba zata zauna ba da fati sai dai takoma kaduna da zama.
Ita ko tun a can na kara mata karfin gwiwa gara ta dawo Abuja ta zauna tunda ba kowa a gabanta yanzu da haka harta yarda.
Shine ita kuma nafisan ganin bata da niyar komawa ta tada wanan fitinan na bata yarda da zaman Fati ba a Abuja.
Muna gidan maigidan ya dawo ta tayar da fitina yace akan may kada fa ta daga mai hankali don shi yanzu mace ba dole bane a gare shi.
Dama can bashi ya maida fati kaduna ba itace ta zabi zama can yanzu kuma tace ta dawo nan don haka dakin ta na nan a gidan.
Wayo buzuwa ina wuta ta saka AA ranan don bamu kishiyoyin ta ba har shi maigidan tsanan shi take ji a ranta tayi tunane kala kala ta rasa na dafawa.
Don yanzu bazata iya zama kasan su ba don wacen zaman datayi bata sha da dadi ba ga gorin yan garin daya isheta sai da Allah ya taimaketa yazo ya dawo da ita.
Yanzu yaya zatayi ga duk kawayen ta na farko dake mata shige shige yanzu duk sun gujeta sun koma ga wayan da suke ganin sun fita bayarda ihisani.
Dole dai madam zata nemo ta dawo a rayuwan ta su dora a inda suka tsaya da wanan shawaran ta kwanta tana jiran gari ya waye ta lalubo madam din taji yadda za a yi.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/28/21, 6:23 AM - Xxxxx: Washe gari da dawowan mu kururuwan Nafisa ne ya tayar damu a gidan ta samu waya Allah yaiwa mahaifin ta cikawa da yammacin jiya.
Duk wanda ke gidan ya tausaya mata da wanan rashin da tayi don mahaifa ba wasa bane gaskiya ko da ban san tsohon ba a yadda ake fadin yana jinya shekara da shekaru dole mutum ya tausaya mai da iyalin shi.
Har dakin ta na shiga nayi mata gaisuwa na dan dade a zaune babu mai magana a cikin mu kafin in fito na bar part din.
Gurin Anty Fati na shiga don mu gaisa nake fada mata dagagurin Nafisa nake naje nai mata gaisuwa ne tace zan dai yi daga nan indan yana kai ga mamacin amma ba zan mata gaisuwa ba ita.
Don ko uwata data mutu bata sani ba amma idan cin mutuncin ta ya tashi gidan nan lokacin uwara dake kwance a kabarin ta itace abin zagin ta kullun.
Naji ba dadi a raina amma dai na kara bata hakkuri a fili nace ba a binta nata ai don zama ya hada mu tare komai mutum zaiyi sai ya gyara ramin sa don ba ruwan Allah da kishin mu hakkin zama zai tambaye mu.
Wanan nasihan danayi mata yasa jikin ta sanyi na dora da fadin wanan isan mutum nabin ta nata sai ta kona kanta ta kona ka ai.
A falo muka hadu da AA din nayi mai ina kwana tare da fadin ashe rashi akayi haka kuma yau yace wallahi Fatiha jiya ta kirani da dare tana fada min ya kare.
Allah ya jikan shi yai mashi rahama nace ya amsa da amin tare da jan guntun tsuki yana fadin yanzu abubuwan mutum zasu tsaya ke nan kuma.
Nace wanan ai ya kawar da komai don dole aje akan lokaci yace hakane garin nasu ne ba dadin zuwa ke gare shi ba ai nace ko yaya ne ya kamata aje da wuri dai.
Wayan shine yai kara ya dauka nikan na shige part dina na barshi gurin ya nufi hanyan part din shi yana wayan.
Ashe Fati tace tai mata gaisuwan da rana ina falona zaune na kira maryam bayan mun gaisa ne nake ce mata ke yau fa rasuwa akai muna a gidan.
A kidimay take fadin innalillahi wa ya rasu kuma khadija banji dear na na fadi ba kuma nace mahaifin Nafisa ne ya kare jiya da yamma wani irin tsuki taja tare da fadin har kin sa gabana faduwa wallahi.
Nace maryam musulmi ne fa dan uwan mu tace don haka aishi zan ma addua ba itaba sai kuma tace ashe zuwa ya kama mu Niger.
Da sauri nace kedawa tace dake wallahi ai wanan dama ne ya samu zamuje muma muga gidan su wanan karon sai ta jimu wallahi.
Sai kin dawo nace mata yanzu fa AA ya gama fadin garin ba dadin zuwa jiki da wani shirmay don Allah ba dadi shi yake zuwa wallahi nina fada maki sai munje mun gani in ba irin wanan sanan ba yaushe zamu samu zuwa.
Sai kin dawo nace mata tace sai dai na shigo yanzu aiki nake yi yace zau dawo yaci abincin rana shine nake girki amma idan na gama ganinan zuwa gidan.
Mukai sallama ta kashe wayan ta barni ina mamakin karfin halin ta don ban dauki zancen da wani gaskiya ba aiki yana ma laraba yawa haka yasa nace akawo min yarinya daga gida irin Nufawan doko din nan.
Sai wata yar maman mu tace ga yaran ta nan mata har uku in dauki guda daga ciki ko nawa ma nake so na barsu zasuyi shawara na dawo.
Itace ta iso da ranan haka yasa

141 / 144

Chapters