zaune tare damu sai cewa yayi wai ke kika saka shi kin san halin mijin naku haka yake abu kamar dan fari ashe shi.
Muka sa dariya da Binta zainab ta dago tana kare dan uwan nata dacewa hai hajiyan mu kina fada mata kuma don ta raina shi.
Binta ta cabe da fadin ai khadija ba ta da raini ga mai rena shi dai can yar haure hankaka maida dan wani naka sai lokacin hajiya take tambaya cikin katse muna dariya.
Tace tasan da cikin jikin ki kaina dukar kasa tare da fadin ban sani ba nima mama na dan kwanta jikin Binta ina fadin nii fa banda komai wallahi.
Binta tace hajiya kinji mai take fada wai bata da komai wallahi kiban dakine ko inji hajiya mama duk muka sa dariya.
Shigowan su anty Fauziya ya katse muna hiran wanda dama na matsu abar zancen sai dai cikin zuciyana tunane fal ke damuna kan maganan cikin da mama ta ambata min.
Gaisaw mukayi dasu suna min yaya hanya Anty Faiza tace ina buzuwar gidan ku yar sheri nace tana lafiya sun shiga aibanta tane hajiya ta katse su da fadin ku bar wanan dabi,an tunda zaune take da dan uwan ku.
Kuma ta fatan shiryuwa idan zata shiryu banji kowan ku ya tabayi yar ta ba wanda jinin ku ne ita ai laifin uwarta bazai shafi yarta ba ko.
Tunda yar jinin ku ne ita don haka ta samu ragowan wanan yar da abinda ke cikin ta yanzu tunda dan uwanku ya dauko yaya za a yi sai hakkuri kowa da halinsa ake zama dashi.
Dazun ya tashi nan ya kawo min karan Fati sun zo bata basu abinci ba yau da safe kuma tasa laraba masu abincin banza.
Kunga ke nan kowa da nasa halin ake zama dashi araina nace saura ni aji nawa problem din gaba tunda yanzu anji nasu su.
Dangin miji akwai matsala sai naji hajiyan tace wanda kuma anan ita fati ta fishi gaskiya don dana kirata ina mata fada cewa tayi bai fada mata zuwan su ba.
Kinga ta fishi gaskiya laifin ta daya da bata tashi cikin daren ta sama masu abinda zasu ci ba ta bari aka je waje sayowa.
Hajiyan mu kin san halinta fa da shegen mako yanzun haka bata saya ba ma sai dai a turo mata da kudi ta haye sama ta zauna tabar yara da yunwa inji Faiziya.
Fa,iza tace ita kan tana da matsala wallahi bata ci bata bari na tare da ita yaci kuma ba a gani a jikin ta shine matsalanta.
Hajiya mama tace Allah dai ya kyauta haka abubuwa sukan zowa mutum wani lokaci ta baibai binta tai caraf tace saura musan matsalan khadija kuma.
Hajiya tace diyata bata da matsala insha Allahu sai dai wanda ba,a rasaba yanzun dai kuyi abinda ya kawo ku muji yaya za, a yi.
Hajiya yaya kika tsara abin ne inji Faiza tana tambayan mahaifiyar tasu wani abu zan tsara kuma yanzu gaku ga khadija sai dai inda gyara in gyara maku idan kun da bukatan hakan.
Sunyi ta tsara abinda zasuyi ni dai ina sauraren su tunda ban san kai ba sai in sun tambaye ni ince yayi daida.
Karshe nayi masu sallama akan zan leka gidan ya Amina na barsu a dakin zainab da binta suka taka min muka tafi.
Ya Amina ta riga da tasan da zuwa na garin a gidan suka barni bayan mun dan zauna dasu suna fita ya Amina ta kalle ni tace khadija ciki ne dake ?
Kai ya Amina haka ma mama fa tace min yanzu ina ciki don Allah anan banda abin ku tace cikin murmushi gashi ko har ya fito ana gani.
Ganin may kuma ina shafa tunbina da hannu tace wai ke da gaske baki da komai ko may don Allah ki fada min gaskiya duk alamomin ki sun nuna ciki a jikin ki wallahi.
Gabana ya fadi ina kara kallon kaina nace haka fa kowa ke fada min ya Amina tun a abuja tace rabon ki da mesturation wata nawa yanzu ?
Nace nima har na manta wallahi kin san tun ina gida yakan min haka wani lokaci ai shiyasa ni ban damu ba.
Tace kajiki da wani shirmay yanzun a gida kike ko a gidan mijin ki da zaki fadi haka tsaya inzo tace tana mikewa tsaye ta shiga dakin ta.
Sai gata ta fito da wani takarda fari mai dan tsawo a hannun ta ta kokarin yaga ledan tace na sawo shine da nake ganin kamar cikine dani.
Sai kuma kafin in amfani dashi sai ga jini yazo min na aje ashe da rabon ke za aiwa gwaji dashi tashi kiyi fitsri mugani ki dan debo cikin wani abu mu gani.
Nace fitsarin nawa kuma ya Amina tace eh mana tunda ke har yanzu yarinya ce baki san komai ba don wauta irin naki .
Kina kwana da namiji ki tsaya gardaman abu gashi kirikiri ana ganin shigar ciki a jikin ki kina gardama kuma.
Shiga nayi ban dakin nayi na kawo mata kamar yadda ta bukata ta saka tsinken ciki sai gashi ya nuna alaman wata uku ke na yanzu.
Nashiga uku na furta tare da kara tambayan ya Amina din nace ya Amina wai ciki ya nuna ina dauke dashi don Allah ?
Tace bagashi kin gani ba da idin ki kina tambaya kuma tana fadi tana dariya kai na girgiza mata ina fadin wallahi ya Amina da matsala.
Ni ina zankai wani ciki can yanzu ina tsaka da wanan karatun na ga rikicin wanan gidan nashi ba mai karewa bane kullun.
Kai amma khadija ke har yanzun dai yarinyace wallahi shiyasa nake matukar tausaya maki a gidan nan wallahi iyakar ki baki amma idan kinyi wani abu sai mutum yaji kamar ya mangareki don haushi.
Yanzun saboda karatu zakiki gina rayuwan ki ko saboda matsalan gidan mijin ki sai ke ki, ki haihuwa yadda kowa ya haihu dashi a gidan.
Idan kina barin wanan wautar ki bari tun wuri kada ki kuskura ki bari mijin ku yaji wanan shashancin naki don duk yadda yake son ki zaku samu matsala dashi.
Ya Amina ni bama zan yarda ya sani ba sai dai idan wani ya fada mashi ko ya gani da idon shi ni kunya ma ai ba zai barni na yi maganan dashi ba gaskiya.
Shawara tayi ta bani barci nayi sosai har yayi ta kirana a waya ban sani ba sai dana tashi yin sallah ne nags kiran shi a wayana har uku.
Na kira shi fada ya fara dani wai ina na shiga haka waya na ruri ban dauka ba tun dazu nace barci nake kuma wayan na cikin jakata ba, a ji.
Yace ok yanzu kina ina nace gidan ya Amina na nake yace ok ganiman zuwa daukan ki ki dawo gida hakana tunda baki jin dadin jikin ki.
Naji sauki fa nan kuma ai gidane gare ni ya kashe wayan dole na fara shirin komawa gidan ba a dauki lokaci ba sai gashi har ciki ya shigo ranan suka gaisa yai mata alheri muka tafi.
Ina shiga motar ya kalle ni baya ya zauna yake fadin kinga yar uwar ki kin manta da mutane ko nace kai da ke ganin naka kullun fa.
Gidan ya kaini bai bari na shiga gidan su ba in masu sallama gidan shi muka nufa a falo na samu su Anty na dan zauna nagaida su na haura sama dakina .
Kayan jikina na rage na dauko wani dongon riga baki nasaka irin mai matse jiki din nan watau hook gaban mirrow naje na kalli kaina ina mamaki kai ni daya a dakin.
Kallon cikina nayi naga yana nan a lefe nace abin da mamaki wallahi ya za, ace wai cikine dani ina shafan cikin nawa.
Wani abu naji cikin ciki na da jikina gaba daya ya amsa min abin na motsi bol bol daidai inda na dora hannu na akai.
Tsoro naji nayi saurin cire hannu na saman cikin ina mamaki da abinda naji yayi din na kara dora hannuna ya dan kara yin hakan again.
Nafisa buzuwa ce ta fado min a rai ashe duk gorin da take min Allah ya riga da yayi nasa ikon akai na ko ita ke nata kalar shirmay.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Yau da wuri na tashi na fada kitchen sai da na gyara komai na dora girki lafiyayyen abin karyawa na dora da dan abinda na gani a kicltchen din ina aiki zuciyata fam da tunanen yadda na samu kitchen din nasu.
Na rasa ta inda laifin yake shin daga bangaren AA ne ko na anty Fati sai dai zuciyana tafi bashi laifi don shi nake zargi da rashin basu kulawan da ya dace dasu.
Tausayin uwar da yayan tane ya kamani a raina na duba yadda acan yake aje muna komai amma nan ba makamancin irin sa kafin wani abin yakai rabi ya kara labto muna irin sa don amfani.
Sai nazo na samu anan ba haka abin yake masu ba a store kan gaskiya ba laifi don akwai komai na kayan masarufi sai dai a kitchen ne irin su nama mai wadattace da saura kayan amfanin gida ga mace duk sai a hankali.
Muryan Laraba ne ya katse min tunane tana fadin hajiya ashe har kin fito ina jiran fitowar uwar dakina ne ta fada min abinda zan yi shiyasa ban fito ba.
Nace basu fito ba nima karanbanin nayi na shigo aikin don kada a makara hajiya hakan ba karan bani bane tace min don hakan na da kyau Allah yasa a dore da hakan .
Murmushi nayi nace mama laraba don wanan aikin ai ba komai bane don mun riga da mun horu da aiki tun a gida.
Nace yanzu ko za, a samu masu kayan miya don naman kai nake son a sayo muna ta amshe da may zai hana hajiya yanzun sai in je nan bakin kasuwa zan samay su sun fito.
Daki na koma na dauko kudi na bata tare da lissafa mata abinda zata sayo muna kudin ta kalla tare da fadin hajiya kudin sun yi yawa ai.
Nace ki je dashi ki sawo na yadda ya dace don gobe ma da jibi sauran canji kyayi amfani dashi tace kai madallah barin yi sauri in dawo.
Ta juya zata fita nace kuma kada muyi rashin hankali da ki dan saurara matar gidan ta fito muji ra,ayin ta.
Kai hajiya dai ai tasan da irin hakan dole ne idan miji yana gari dole a gyara mai balle irin mijin ku mai yawan jama,a nan barin yi sauri in tafi.
Nace to shike nan sai kin dawo naci gaba da aikin gabana cus, cus nayi na da ganye don shi nake ganin zai dan ciwo da safe ga kowa sai ferfesun sauran kayan cikin ragon da na gani a fridge din.
Daga baya na dora ruwa tea wanda na saka kayan kamshi a cikin sa sallaman mama laraba ne da har ta dawo daga aiken da nai mata din.
Nace mama abin ba wuya har kin dawo tace aikin abin hawa ne ai kuma a nan kasuwan cikin unguwa na tsaya don in sauri.
Nace na gode mama ga abin karyawa nan na hada sai ki dibi mai isar ki ki zuba wa kanki kafin in kwashe ma saura tace ai ayi haka dadai kin zuba min yadda aka saba zai fi.
Tana miko min canjin da ta dawo dashi nace kai mama banace ki bar canjin ba yanzu dai nuna min kulan da kuke zubawa direbobin abinci idan sun zo dana maigidan.
Ta nuna min wani karamin kula nace kai haba mama su uku ne fa wanan ko mutum daya ba zai isa ba ai na jawo wani babban kula na zuba masu a ciki karamin shi na zuba masi ferfesun kayan cikin.
Nace mama sai akai masu ko tace to yar albarka ta dauka ta fita na gyara kulan da na zuba masu AA da Yusuf tare da na Anty Fati da yaran ta sai kuma laraba a karshe na cika mata kulan data nuna min na direbobi da farko.
Sai kayan tea din da na gani na ce idan tazo sai ta dauka mu a dauko wani ai amfani dashi cikin wanda za a rabawa mutane da muka zo dashi.
Ta dawo nace ga ruwan zafi nan akai masu sai kice su dauki gwangwani madara da millo a mota da suga na amfanin su ne tace to hajiya tana washe baki.
Ta dauka suka hade da Anty Fati take tambayan ta ina kuma zaki da wanan tace aike na akayi hajiya amaryan ku tana kitchen din.
Bin laraba tayi da harara ta nufi kitchen din ganin ledan cus cus a dustbin din kicin din cike ya hanata min sallama sai cewa tayi wanan ai barna ne duk wanan ledan cus,cus din may akayi dashi haka ne ?
Fuska dauke da murmushi na juyo gare ta ina fadin anty kin tashi ina kwana ta amsa min sai kuma ta kara maimaita maganan ta gare ni wanan cus cus haka da aka dafa fa?
Nace anty amfani nayi dashi wurin hada breakfast tace amma wanan duk ina za a kaishi haka kamar abin ya zama barna nace yi hakkuri anty gani nayi kamar zai isa .
Ta nufi kitchen din tana bude kulan abincin na fara mata bayanin komai ok kawai tace fuska a daure ta juya wurin ledan sakon da laraba ta sayo min tana fadin wanan kuma fa.
Nace wanda zan muna amfani dashi ne da rana tace shiya bada kudin ko ya sayo nayi kasa da murya nace nice na aiki laraba ta sayo su yanzu shi bai fito ba ai.
Tace Ok tana ja da baya sai gashi kitchen din da kansa yace na duba daki bakya ciki ashe kina nan ina kwana nace mai ya nufo ni ba tare da ya amsa min ba.
Ya dan kai hannun shi a saman wuya na yace jikin yayi sauki ko nace tun jiya ai na watsake sosai wanan aikin da kikayi haka ai yanuna alama.
Yanzu kuma may kike yi nace abincin rana zamu dora don kasan bamu da time yau sosai laraba ta shigo ganin da gwangwanayen kayan tea danace ta dauko a mota tana ganin su sai zata juya nace.
Yawwa mama sai ki aje a dinning barin fito da wanan kayan nace da ita anty fati tace da ki bari tazo ta kwashe ai yana fita ya juyo yace mata sai aikin bada commad baki iya motsa jikin ki ke ko kadan.
Nace ai ni kamata inyi tunda ina nan ita kuma ta huta ko ya wuce bai ce komai ba waje ya nufa nasan gun direbobin shi ya nufa su gaisa.
Mun gama jera komai muka dora girki abincin ranan da za a ci suna falon ya turo Affan ya kirani nazo.
Zaune suke sin fara karyawa na gaida Yusuf da kwana yace a, a kanwata wanan irin girkin haka tun da safe gaskiya naga wuyan mutumina yana dada kauri yanzu.
Murmushi nayi nace aikin su anty na ne da buzuwa idan kaga haka tana gefe zaune da yaranta suna cin abincin su hankali kwance tace wata fati aikin kune dai amare masu lokaci.
Murmushi nayi nace ni inani ina wanan aikin haka na samu abiku da a cikin yanayin sa AA ne yace ke zauna ki karya nace nasha tea a kitchen yanzu na gama karyawa.
Wani kallo yai min nayi saurin fadin Allah ko baka yarda bane anty fati tace may nagaya ma Yusuf yanzu ka gani shine ma mai sata ta karya ai.
Kamshi a duke baiyi magana ba sai nine nace ai anty ya rigaki ne don ke ya kamata ki min maganan karin.
Tace to angon ki ya rigani ai don shi yasan zafin ki fiye da kowa anan gane manufar maganan ta yasa nayi dariya tare da wasance maganar nace ni abincin daddy zanci ina nufar inda yaron yake zaune yana ta aika cibi a cikin shi.
Yana ganin na nufo shi ya jaye plate din shi yana fadin banyi banyi dariya aka kwaishe dashi Yusuf yace in banda abinka daddy ai ita ta girka ma zakai mata rowa kuma ko baka son ta karama wani ne.
Sai ya miko min plate din nace na koshi ci abincin ka baba na fada ina juyawa zan bar wurin yace kunyi magana time din da za a shigo da kayan Yusuf nasan sani don zamu zaria ne yau ?
Nace eh to naji kamar suna fadin Four na yamma ko yace ok lokacin mun dawo ke nan don naga yayan naki a zumude yake yau.
Nace kada kaga laifin yayana kai kariga da ka tara naka a gida ko Yusuf yace kyaleshi kanwata ni biyu ma zan yi kusan lokaci daya.
Nace kai haba dai yayana tun kawata bata gama cin amarcin ta ba zakai mata kishiya yace wanan an fada maki da gaske yake yi ne bafa jarumin gaske bane shi.
Yusuf Yace I mean it ku bari ku gani kuwa zan baku mamaki ai ita zainab ta sani don na fada mata komai tasan da maganan .