Da sallama na isa gurin su suka amsa min gaida su nayi da shan ruwa tare da kara tambayan su ya mutanen asibiti sukace da sauki.
Yusuf ne yace kanwata kina yin azumin nan akai akai ga lalurar ciki kuma ki dan sahirta ma ki dinga dan hutawa ko kwana bibiyu ne mana.
Murmushi nayi ina kaiwa zaune nace banda matsalan komai yayana bari kawai in bi sahun jamma,a in sauke nauyin shi a kaina.
Yace na fada mata bata jin magane na yanzu kinga inda rashin jin maganan Nafisa ya kai ta taja wa yarinya wahala don rashin tausayi.
Amma ai kaji ita basu yarda rashin kulane kamar yadda likita ya fada ba ya jawo haka ita ba dauka take wai wani ne ya sa mata hannu kamar wai sheri akai mata na sihiri.
AA yace kyale ma haukaciya naji duk haukan da take fadi ai, yau aka fara haihuwan diya da wanan matsalan haka.
An fada mata ta yi bedrest don ciki ya samu ya tsayu yarda ake so amma matar nan ta tayar da hankali wai ita gida zata dawo ta dawo gidan kuma bata zauna ba kullun tana cikin yawo in ma wani abune ai ita tajawa kanta shi wurin bakin yawace yawacen ta na banza.
Tunda ya fara magana nayi kasake tare da tagumi ina sauraren shi tare da son in gano wani matsala ne ga yarinyar har yanzu banji sun fada ba.
Kin ci wani abune da aka sha ruwa naga baki debi abincin kin ci ba tundazun yace min yana kallo na sai lokacin nayi ajiyan zuciya nace wallahi tausayin yarinyar dai nake yi a raina.
Yar jaririya tana wahala irin haka abin akwai ban tausayi sosai wallahi Yusuf yace indan an bi yadda likitan yace ai ana iya mata aikin kan da cibiyar nata insha Allahu.
Wani irin tsoro naji har cikin raina ya mamaye ni sai nake ganin nima wata kila haka zan haifo abinda ke cikina da matsala din kamar yadda nafisa ta haifi nata.
Sun kula da yadda na shiga damuwa a lokacin Yusuf ne ke fadin kada fa wanan abin ya tayar maki da hankalin ki yanzu ki jawa kanki wani matsala kuma.
AA yace tambayan ki nayi kinci abinci yanzu ko kuwa idan baki cin abinci fa zan dakatar dake ga azumin nan tunda Allah da kanshi ya sawaka ma mai irin laluran ki yin azumi.
Yanzun zan je in ci na basu amsa ina kokarin mikewa tsaye jawo plate yayi ya fara zuba min farar shimkafa da kayan hadi ya turo min gaba na yace zauna nan kici in gani.
Dole na fara ci kira ne ta shigo a waya shi ya dauka banji may ake fadi ba sai dai na fahinci Nafisa ce akan layin tunda ya kasa kunne sauraren ta yake baiyi magana ba.
Sai data gama yace nafisa so kike nima in fadi da ciwo ne komai ina yanzun nabar gurin naku da zaki ce nazo gida na zauna na manta daku.
Kashe wayan tayi naga yabi wayan da kallo sai Yusuf ne yayi dan murmushi yace ita matsalan ta ke nan idan abu yazo bata binsa a hankali.
Wayan yake kallo baiyi magana ba sai dai yanayin fuskan shi daya nuna bacin rai karara a lokacin ya gama kallon wayan ya dago ya kalli Yusuf din yana fadin.
Idan ka gama muje muyi sallah daga can sai mu wuce tace wai likitan yazo yana nema na yanzu.
Yana fadin haka ya mike tsaye dama ba cin abincin nake yi ba tunda nayi cibi uku naji ya fita raina bazan iya ci ba yace ki tabbatar da kin cinye wanan abincin kai kawai na gyada mashi.
Sun fita na tatara kayan gurin da sukai amfani dashi na kwaso zuwa kasa ina shiga dasu laraba dake zaune ta taso zata karba nace mama barshi ki zauna ki huta ke ma hakana.
Juyawa nayi na fita zuwa kwaso sauran kayan da na bari sai ga samira yar wurin nafisa babbban tace anty akwai abinci a gurin ki ki bamu yau basu girka muna komai ba suna asibiti kuma an rufe store din.
Akwai abinci nace mata tare da tambayan ta da ku nawane kije can mama tana ciki ta zuba maku na wuce zuwa sama sauran katan da zaiyi amfani dashi idan ya dawo na sa a dakin na sauko kasan .
Na samu ta karbo abincin suna zaune su hudu a falo suna ci ban tanka su ba na wuce abina zuwa part dina mama zaune da yaran suna kallo Affan ya tasa fruit's a gaba yana sha.
Sai dana tsinki aya daya na zauna ina barewa naji laraba tana fadin kudai yaran yanzu baku da tadan abinci idan dane ai ba zakici wanan ayaban ba don cewa ake yana saka turken yaro yayi tauri cibi yaki faduwa da wuri.
Da sauri na mikawa daddy ayaban dana bare din ya karba duk da ban fahinci maganan nata sosai ba sai dai banci din ba.
Tace waini wani irin lalura aka haifi yar dashi ne na sauke ajiyan zuciya ina fadin mama ban tambaya ba don gudun magana.
Saidai ina ganin matsalan a kaine da cibin da kike magana yanzu a yadda na fahinci maganan su sunayi shida Yusuf yanzu.
Allah ya sauwaka tace tare da fadin Allah yasa wanan abin ya zama mata ishara ta daina halin banza nace amin .
Gobe idan Allah ya kaimu ai zamu shiga mu gaida su duk da dai nasan zuwan nawa wurin ba zata so shi ba amma ai dole in lekasu ko dan mijin ta kada yaga rashin kyautawa na ko mama ?
Tace kwarai kuwa yar nan ai ba don ta zakiyi ba don Allah zakiyi da mijin naku amma in don itace ai ba kya je ko ina ba wallahi.
Waya na dauko ina kiran maryam nake fada mata da safe idan tana da lokaci ta shigo muje asibiti mu gaidasu.
Khadija ke baki da zuciyane komay matar da za, a ja gayarwa taiwa mutane tijara zaki ce mu koma gaishe ta kuma.
Nace maryam ba don ta zanje gurin nan ba kin sani saboda Allah da mijin mu zan tafi don kinga rashin zuwa na bai dace ba gaskiya tace sai kin dawo ta kashe wayan ta barni da kallon wayan a hannu na.
Bai dawo ba ni kuma nayi kwanciyana a part dina saida asuba na shiga na tayar dashi don sahur saboda nasan ba zai kwana dai a can ba.
Fada yai man na rashin zuwana dakin nace baka nan dawa kake son in zo inzauna anan ka dai so dora min laifi ne.
Na fito na barshi a dakin bayan na gama hada mai abinda zaiyi sahur din dashi yana bandaki na fice part din.
Nayi masa hakane don yasan abinda yayi din bai kyauta min ba don ya gyara saboda har sha biyu da rabi ya wuce muka kwanta da mama laraba bai dawo gidan ba har lokacin.
Idan kuma na kyalesu ga sanin halin Nafisa da nayi don burin ta shine taga ta kuntatamin ta ko wani hali a gidan.
Washe gari da safe sai da muka gama gyara part din mukai waka muka kwanta har lokacin yaran na barci basu tashi ba yasa muma muka kara kwantawa bayan tanadar masu abinda zasuci idan sun tashi din.
Sun sake jiki sosai dama karamin ne ya so yai fitina daga baya kuma ya daina ya sake jiki sosai dani ga kuma mama laraba da tun farko sun bude ido da ita akwai sabo a tsakanin su sosai.
Ina cikin barci muryan maryam ne ya falkar dani daga barci tana fadin iyyeh kin hanani barci akan wanan bakar kishiyan taki ke gaki kina abinki hankali kwance.
Idona bude da sukai min nauyi ina fadin ai na dauka baki zuwa din tunda kin fadi haka takai zaune a bakin gadon tana fadin.
Ai ba don ta zan je ba don AA din ki ne kawai wallahi saboda mutuncin dake akwai a tsakanin mu da banje wurin yar iska ba yanzun dai ai taga ishara akan ta bakin halin ta ya jawa yar cikin ta matsala dama irin su a haka suke ganin abinsu.
Allah dai ta sawaka nace da ita ina kokarin mikewa zaune nace ai jiya mama ta lurar dani wani zance maryam nan dai nake fada mata yadda mukayi da laraban.
Tace ai dama kema kin san abinda zai biyo baya ke nan ga zancen din dauka suke kowa haka yake kamar su ai ke dai yanzu ki kula da addua Allah ya sauke ki lafiya.
Nace ina yi maryam ke nima auren dai matsala ne wallahi yanzu shi yasa nake tausayin yan mata idan suna rawan kai wai su zasuyi aure kiga yarinya yanzu ba kunya tana fitsara.
Tace rashin sanin ciwon kaine mana tunda hankali bai kai ba sai idan an shiga ido ya raina fata kuma don mazan yanzu ko wata ba a rufewa za a fara saida hali idan kuma ka samu kishiya tace dawa Allah ya hada ta bada ke ba irin naku din nan.
Wurin wardrobe dina na nufo na fito da wasu material da zan saka a jikina tsab na shirya a cikin su ni kaina nasan kayan sun matukar karban jikina.
Tace gara da kika saka kayan nan don nasan yanzu gurin nan kamar kasuwa da a bokanta yan duniya irin ta.
Waya na dauko na kirashi ina fada mai zan fita yace ki jira driver yazo yanzu ya kashe a yadda ya amsa min wayan yasa na fahinci a gaban Nafisa yake a lokacin.
Don idan suna tare muna waya dashi yanzu ina ganewa ga yanayin da yake amsa min wayan daban ne da idan bata a kusa dashi.
Bamu dade da jira ba driver ya iso yace mu fito tare da laraba da yaran muka nufi asibitin gida tsit kamar ba kowa a cikin sa.
Maganan mu ya zama gaskiya don muna zuwa driver ne yai muna jagora dakin da suke tun daga nisa muke hagon su sun sako idanuwan su akan mu.
Canjin yanayina gaba daya ya basu mamaki don zakace ko baturiyar asalice tayi shigan hausa yadda komai nawa ya bude a lokaci guda ga traning din anty Salbiya da anty Hauwa na aiki.
Nayi masu kwarjini sosai a idon su yaran da mama larabane a gaba suna bin driver sai ni da maryam a baya da muka jero tare muna magana.
Gab da zamu shiga dakin ne wata buzuwa da ban santa ba take muna magana tana fadin ba,a fa barin kowa ya shiga daga nan ake mika masu gaisuwan su.
Ni kan mamaki nake na yadda naga yan yaren su a gurin da yawa haka ashe suna da hadin kai ne haka sosai nan dai gasu madan dasu sabuwa a gurin su ma.
Tsayin mu yayi daidai da fitowan Yusuf ciki yana ganin mu ya washe baki tare da fadin a kune tafe ashe ku shigo mana ko suna ciki AA din ma yana nan yanzu muka shigo.
Nace wa yan nan sunce ai ba a shiga inda suke ko yace akan wani dalili ba gaida ita kukazo yi bane mujen ku dan Allah ya fada yana fara tafiya muka bishi a baya.
Ya tura kofan dakin da sallama muna biye dashi na hango AA ya zaune da hannun nafisa dake kwance a saman gado duk ta sauya saboda damuwa.
Ga yar a kwance a gefen ta an rufeta da shorwel fari kallo daya nayi wa yar da sauri na kawar da idona shiko duk yai wani daburcewa da ganin mu.
Gaida ita muka fara yi tare da mata barka da arziki tayi kamar bata jimu ba shine yadan matsi hannun ta yace bakijin su Deedar na gaida ke ne ?
Ta dago kai ta kalle mu wani iri ta watsar tace kai ka san su don ni ban gaiyace su ba tunda nasan gulma ya kawo ai don suzo suga abinda ake fadin na haifa din.
Murmushi nayi ina gyara tsayina tare da dafa gadon nace mu bashi ya kawo mu ba don inda sabo mun saba da wanan zuwa mukayi muyi maki barka kuma mu gaida babyn mu.
Hannun ta ya sake ya nufi yar zai dauko ya bamu tace kabar min ya a inda take duk da take hakan tana ganin banson abina inson ta a hakan.
Nace dama ka barta ai tana barcin ta, ke banda abinki ina kika taba ganin jujin yara kowa ya haifi da ai yana son abinshi ya haifa.
Dauko yar yayi ya mikawa laraba ita tace yanzun ma zuwa kikayi nan ki karasa ta komay tunda baki so yar ta fito duniya tana numfashi duk da sherin da kikai mata tun a ciki.
Ba laifin ki bane hakan da Allah kike son yin jayaya mu bashi ya kawo mu ba daidai laraba na mike mun yar kamar kada in karbe ta nadai sa hannu na karbi yar tare da fadin ubangiji Allah ya baki lafiya kinji.
Na mikawa maryam sai sababi take muna muka mika mashi yar muka ce Allah ya raya muka juya yace wanan wai wani irin haukane akan yaran ma fada zakuyi ko may yarinya nata kanta cikin wanan halin.
Tace idan haihuwa yana da dadi tayi mana mu gani na juyo ina fadin zaki gani idan muna raye kwana nawa ya rage inji maye .
Haihuwa kan tunda ina tare da mijina ai yin sa zanyi da yardan Allah yadda kowa yayi shi kuma ki dai gani anayi nace yaushe kuma Allah ya fiki don dan zaki ya girma ko na nuna mata cikina na fita.
Samad wai may yarinyar nan ke nufi ne da maganan ta yace abinda kika tambaye ta ne ta baki amsa da nuna maki mana tunda ke baki san yakamata ba.
Kina cikin wanan halin haka har kinga wurin fada bazaki ji da abinda Allah ya jarabi mutum dashi ba wai kana nufin itama ciki gare ta komay yace baga shi kinga ta nuna maki ba.
Kururuwan ta ne yasa yan wajen saurin shiga dakin hankali tashe suka samay su taci kwalan mijin tana fadin wasau maganga nu da bata san tana fafi ba a lokacin.
Ya banbare hannunwanta daga jikin shi yana fadin wawiya mara hankali bazakiji da abinda ke gaban mutane sai kin jajibo wani fitinan kuma.
Ita din ba matana bace da ba zata haihu dani ba komay da kishi zai rufe maki ido kina wanan hauka haka yanzu ai kinji ma kanki wani tashin hankalin tunda haka kike so.
Samad Allah ya isa tsakanina dakai da yan uwanka yadda kukai min sai Allah yai maku shi kuma munafukin banza kawai azzalumi.
Madam ne tayi mai magana akan yaiwa Allah ya fice daga dakin ya kyale ta yan uwanta buzaye kuma na magana a cikin yare suna fadin may ye haka take yi ne wai.
Ciki ina bama zai yuyu ba wallahi tasan dai inda ta kwaso cikin ta take son kakaba maka kaiko daba kasan ciwon kan ka ka yarda dashi.
Ya juyo a fusace yana fadin gada ki soma sheganta min cikin jikin matana don nike da abina ni nasan kuma zafin abina.
Munyi dake ne idan na aure ta ban haihuwa da ita ko may ke da nake haihuwa dake fa madam ta samu ya fice dakin da kyat a lokacin mu har yusuf ya saka mun bar asibitin ko.
Yafito a hasale yana fadin shine dalilin da kaji nace muzo wurin nan yanzu don sanin halin Nafisa da nayi don kada suzo ta nemi salwanta min wani cikin kuma ta gama yiwa nata ta,adi.
Don Allah ka daina biye mata kuna haka mana AA a bainin jama,a tunda kasan halin abinka yace ina amfanin kullun a boye mata cikin jikin Deedar Yusuf ai gara ta sani idan ma mutuwa zatayi taje tayi wanan matar halinta ya isheni yanzu.
Hakkuri zakayi ka san halin mata akan kishi yanzu wanan abin kunyan da take damay yai kama AA yace ita ta sani yana tsuki.
Yanzun Nafisa kin tabbatar tun kwanaki nake fada maki ciki ne da yarinyar nan kika ce Samad yace ba ciki bane shi baisan tana da ciki ba a ina ta samo ciki.
Ai yanzun dai kinji ga bakunan su ko madam tace duk da cikin ne mun tabbatar din ai mu kwantar da hankalin mu muga cikin to mujira hauhuwan shi mukagani mana.
Damu take wasa ba har tana iya nuna wai ita mai ciki bane shi a dole ga mijin mai cikin fari a haihu din mu gani in shari ne ai kowa ya iya ko.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Tafiya muke a motar babu mai magana a cikin mu kowa da abinda zuciyar shi ke saka mai a lokacin duk mu a cikin motar sai maryam ne ta kawar da shirun da motar yayi a lokacin.
Khadi tunda kuke fada da buzuwan nan a gabana baki taba burge niba irin yau mace haka bata san Allah ba ita.
Ko wanan yar dake gabanta haka saye da naura bai ishe ta ishara taji tsoron Allah ba a zuciyan ta abinta ne fa Allah ya fara