fadin ina hankalin ta zaisa ta gane hakan yanzu tana can wurin bakin yawon ta mara dalili daga haka ya haura sama.
Sai da ya dan jima da shiga na mike na samay shi a dakin yana kwance rigingine na karaso na zauna a gaban shi ajiyan zuciya naji ya sauke.
Dan kwantawa nayi saman jikin shi tare da kokarin kawar mashi da tunanen shi wanda nasan akan Nafisa din yake yin shi nace.
Bazaka koma wurin aikin ke nan ba ya sake sauke ajiyan zuciya yana dora hannun shi a saman ciki na yace banjin komawa na gama na yau sai dai gobe.
Zan zauna inga dawowan wanan mara mutuncin ne nace haba zakuyi halin kuma ke nan ka kyale ta tunda kun saba da hakan.
Yawon nan na fisa yakai min ko ina ko aikin gwaunati take iyakar ta ke nan kai ko aiki take ai ba zata kai haka ba dai.
Ta saba ne tun farko babu hanawa a gurin ta amma da tun farko akwai dokan hakan a gidan ka bazata yi ba ai yanzu ko abin wuyan tankwarawa zai yi a furin ka.
Zan ko baki mama idan ba zata iya zama gida ba sai dai mu rabu wallahi dagawa nayi daga jikin shi don jin kalamin shi da yayi nace.
Haba yaya kada kai fatan rabuwa da uwar yayan ka don abin ba zai damay ka ba sai gaba idan yara sun tasa babu uwar su a cikin gidan ka nan fitinan haka ke taso wa.
Ka saba hakkuri da abinka kayi hakkuri da abin ka sai dai ka zama na miji akan hakan ka nuna mata kai ke auren mu bamu ke auren ka ba ka nuna kaine maigida a gidan ka shine nake gani solution din haka.
Samad amma kasan yau ba ranan girkin wanan bace da kuka shige daki da ita haka da sauri na dago saman jikin shi sai dai shi hannun shi na saman ciki na din har lokacin.
Kallon ta nayi daga gani ko daki bata shiga ba dawowan ta ke nan taga motar shi tasan yana gidan ta hawo sama.
Malama a koyi yin sallama idan za a shiga wuri gada kizo ki samu ba daidai ba tace gidan ku su koya min sallama din .
Zama na gyara tace tashi ki fice daga dakin nan nace koke ki fice min daga dakin nan na kalli agogo kiga lokaci idan kin iya karfe nawa yanzu ko kuma kwancen girkin da kika saba zaki min yanzu kuma.
Tace an ki a kalla din wai kokarin kike ki jaye mai hankali zuwa gare ki wai yarinya kin makara samad nawa ne don haka kije ki nemo mijin ki.
Ke bakiji kunyar fadann maganan nan ba wai yaya Abdulsamad namu duka ne da naki ne ke kadai da baki wanan haukan da kikeyi ba don Allah ki ficewa mutane daga daki na fadi a dake.
Muryan shi a dake ya daka muna tsaya yace ke kifice min nan tun ban bata maki rai ba gidan ubanwa kika fito yanzu kin bar yarinya a wullakace ita kadai a gida.
Wai Nafisa anya kina da burbushin imani a zuciyar ki kuwa tace sasai ka saman naka ina kake son in fita da wanan yar haka a nuna ni a gari.
Yace lalai yanzu na kara tabbatar da koke wacece na yarda baki da imani tunda har kina iya yayya da hukuncin Allah akan abinda yaso gare mu.
Inajin sun kaure na mike tsam da zumar in bar masu dakin suci kansu sai naji tace duk munafukin da ya fada ma na tafi na barta sai ya rungumay ta ai dama may yarage ba ai mata ba .
An riga da an shiga an fita tun tana ciki an hakakala ta sai ki karasa abinda ya rage gatanan na bar maki ita babu inda zan fita da ita a dinga nuna ni.
Kin san dai inda kika shiga aka hurhura maki yarki kaikayine ya koma kan mashekiyar sa ai kowa ya dai bo da zafi bakin sa.
Ki bari ki ga kema abin da zaki haifa ga cikin jikin kin ki da yardan Allah sai kin haifi wanda tafi wanan munu nace Allah ya bani sai in rugumi abina da hannu biyu watarana sai ya bani mai kyau.
Zaki gani dani kike wasa a gidan nan nace inga Alherin Allah a tare dani don bakiyi kamar Allah ba ai yace wai nafisa kina da hankali kuwa ?
Yar uwar zaman ki kikewa wanan fatan haka tace yar uwar zamana na ina yar uwar zaman ka ai da tai min sherin ai banga ka dauki wani mataki ba ga hakan.
Yace mai tayi maki da zan dauki mata ki a kanta ko itace mai bayarwa ba Allah ba har kina ikirarin sheri da bakin ki a gaba na kuma.
Wallahi duk abinda ya saman min jinina nan gaba ba zan barki akan hakan ba don ki sani tunda kiyi ikirarin haka da bakiin ki.
Oh ashe da yafi dane tun dan baizo duniya ba kana ikirarin daure ni ai ban san da yafi da dadi ba sai yanzu daka nuna nace ni ba abinda zaki iya min da yardan ubangiji na don ga Allah na dogara baga wani ba.
Ina fadar haka na fice na barsu a dakin nafito rai bace zuwa daki na laraba na gani na haka duk ta damu dan zama nayi da ita gurin na mikewa zuwa yin sallah ina idar da sallah ns kira mamana ina fada mata abinda tace min din.
Mama tace ds yardan ubangiji lafiya zaki haihu mai albarka wanda zamu aika ita batayii kamar Allah ba duk cika baki ne irin na wanda bai san Allah ba.
Kada kisa zancen ta arai ya damay ki lafiya lau zaki haihu cikin hukuncin ubangiji nace to mama tace kira kakan ki fada mai yadda kukayi kiji may zaice.
Muna gama waya ba kirashi don gaskiya na tsorata da zancen nafisa don nasan shuuma ce tunda har ta furta zata iya din.
Mun gaisa yana min wasan jika da kaka nace Bado akwai matsala fa yace na sani ai tunda naga kin kirani murmushi nayi nace ai da banda layin kane ban kiran ka.
Yace to yaya akwai sauki dakika koma din nan ko abin yana nan har yazu nace Bado akwai sauki sosai wallahi tsakani da miji ba wanan yawan fitinan yanzu sai dai ita abokiyar zaman nawa ne.
Nan dai na kora mashi halin da ake ciki naji yayi dariya tare da fadin hadizatu kin yarda Allah nace kwarai Bado yace to kisa yarda kika yarda da Allah kika kuma imani dashi ba abinda zata aiko maki ya kara galaba a kanki insha Allahu.
Ki kwantar da hankalin ki kidai ci gaba da yawaita addua da yawan sadaka da kyautatawa mabukata na kasa dake in sha Allah duk abinda ta dauko a kanta zai koma idan ta mata zata ga ba daidai ba a rayuwan ta.
Mukai sallama dashi na kashe wayana sai danayi isha,i na fito falo na samu laraba zaune ita kadai a cikin damuwa nace mama anan zaune ne ?
Tace to uwar dakina banda zaman bamu da wani aikin yi sai kallo ba kamar can da yan aiyukan wata rana har suka fi karfina bane.
Zama nayi nace an karbo kayan guga wuri mai wankin nan tace an karbo sai dai yazo min da wani zance wai an yagi zanin ki ta kasa jiya ba haka ya wanke shi ba.
Nace ikon Allah wata sabuwa ke nan kuma zani na may zasuyi dashi kuma tace sheri mana yar nan ai haka masu bakar bidan asiri suke da yawan surkulen su.
Yanzu wani katon mushirinkin bokan ne nasan ya bukaci a kawo mai yankin zanin ki nace wallahi mama haka aka taba min kafin ki zo garin nan ban fada ma kowa ba sai maryam dana nuna kayan.
Sai tace injin dai baki saka kayan ba nace wallahi na saka tace ashe idan har Allah ya nuna ma sheri ka gani ga idon ka ai sai kayi taka tsamtsam kinga kwanaki kafin muje garin nan naku.
Nace tace Yanyala na samu tana kakabe carpet din kofan nan tana tara kasan a zata zuba a cikin wani leda sai gani munyi rikici sosai da ita ban fada maki bane don gudun fitina bakiga na dauke carpet din a wurin ba.
Nace ikon Allah wai duk akan in bar gidan suke wanan abin haka tace ko ki nakasa ba ba sherin da yan bakar bida basu iyawa yar uwanzaman su ba ai Allah dai ya tsare ya kare nace Amin.
Mama dauko zanin da aka yanka din mu gani nace wa laraba ta mike taje daukowa sai ga AA ya shigo dakin yana fada min wai Abba ya daga bukin zainab sai gaba.
Da sauri nace mai subbahanallahi yace eh dalilin da ya bayar yana da kyau kin san ta kusa kara karatun yace idan ta karasa sai ayi ya wuto da ita nan gaba daya.
Nace Allah yasa haka yafi zama alheri ai ni abin zai mun dadi gashi an fara fadin dama ba zan tafi yanzu yai min daidai ke nan.
Ni dai ban san abinda yasa yayana Yusuf ya daina zuwa gidan nan ba yanzu na tambaye shi kallo na yayi zaiyi magana.
Laraba ce ta shigo dauke da kayan a hannun ta ina gani na manta yana gurin nace wanan sabon kayane fa mama sai ya juya yana kallo.
May ya faru yace nace nakai wanki ne yanzu mai wanki ya aiko min wai yazo guga ya samu an yankar min zani na da mamaki yace yankar zani kuma may za a yi dashi idan an yan ka din.
Laraba bata san sanda ta bashi amsa ba da fadin asiri mana Alhaji yace ta miko mai zanin tana mika mai tare da nuna mai gurin da aka yanka din.
Fita yayi da zanin a hannun shi laraba ta fice part din yana fita tana zaune falo yace Nafisa waya yankawa Deedar zanin ta gidan nan.
Tace wanan ai tambayan banza ne zaka zo ka sani a gaba kana tambayana wa ya yankawa matar ka zanin ta kafin yai magana Ihisan tace Ami ne Abbi tare da Yanyala muka je da Ami ta tsare yanyala ta yanka da suka aiki mai wanki.
Dawo da kallon shi yayi gurin Nafisa din yace kin gani yarki ta fadi gaskiya zaki lalata min ya da bakar bidan asirin ko har da ita kike zuwa.
Ihisan kamar mai wasa tace Abbi an kai wa wanan mutumin da baida riga har ya shafa min wani abu a jikina jikake dim dim uwar takai ma yarinyar duka sai da ta kife kasa daga saman kujeran.
Yana karasowa shima ya dauke ta da mari kauuu sai data duka ya tallabo yarinyar yana rarashin ta yaja hannun ta suka nufi part din shi.
A gaban laraba akai komai tana labarta min abinda ya faru nace Allah ke nan dayake ban da amanan ta ya fitar min da hakki na Allah ya gani ina matukar son kayan nan.
Ban ji duriya shi ba haka yasa na fahinci yana cikin bacin rai sai da safe ya shigo part dina yana fadin shi zai fita nawa zanin yake ya biyani nace ka barshi tunda ina da wasu dama cikin wanda ka saya min na lefe ne na dinka shi.
Kudi ya fito dashi koda ban kalla ba nasan kudin yana da yawa yace gashi in za a samu irin sa a nan sai ki saya a kara dinka maki kalarsa.
Nace daka barshi ai don ba yau suka fara min haka ba a gidan nan karo na biyu ke nan wallahi yace ga Ihisan ta fadi yadda sukayi wani gardama zatai min kuma.
Har fa da yata suka tafi gurin shirkan su aka shafa mata wani abu bayan bokan yai mata tsirara wai da ita da Samira duk jiya ihisan din ke fada min.
Allah ya kyauta shine kallama ga sherin ta ko yanzu din shina kara maimaitawa a bakina ya fice nace monday zamu koma school fa.
Ya juyo yana fadin monday din nan mai zuwa nace insha Allah sai yai dan shiru yaja tsuki tare da fadin Allah ya kaimu nace Amin komawan kakewa tsuki kuma ?
Yace No naso kafin ki koma motocin mu sunzo ne don akwai naki a ciki ban son wanan toiries din gare ki kwanaki naba da sako sai ba a samo wanda nake so ba.
Nace ai ba komai tunda ana kaini ba wani matsala bane duk lokacin da suka shigo sai a bani yace shike nan .
Sai ki min list din abinda ake bukata mu gani kafin monday din in baki daga haka yasa kai ya fita a dawo lafiya nayi masa daga gurin da nake zaune din.
Kudin da ya aje min na dauka na kirga sai da nayi mamaki tare da fadi a raina wanan kudin har da toshin baki dai kada naja zancen da nisa watau.
Ina adana kudin maryam na shigowa gidan sai da ta kalle ni ta tuntsire da dariya tace wanan ciki ya kara maidake wata babba mace haka.
Nace da ba babban nake ba may nake tace ai na manta tana kaiwa zaune tace yau banga buzuwar gidan ku falo ba don haka take zama kullun kamar mai gadi.
Yau Allah ya tona mata asirine ai nan dai na kwashe maganan na fada mata tace muguwa Allah yaki aniyar yar iska da Allah kadai yasan sherin da zasuyi dashi.
Nace wallahi shiya ban saka yaran nan a cikin zancen mu da ace ina masu mugun hali a rayuwan su bazasuga ana cuta min suyi magana ba tace wallahi da ba,a jin komai haka don koyo zasuyi suma yau da gobe bai bar komai ba ai.
Nace bata da kunya ai don wanan ba shine farko tsura ta ba kin manta zacen layun da aka gani cikin filo daya kirata cewa tayi sheri ake son mata dai.
Maryam tace shi wanan din ma sheri ne yar nata ta fada ai tayiwa kanta don idan tasan kunya taji shi muna cikin zancen laraba ta shigo tana fadin ga gugumanmun nan su shigo da sauri muke tambayan ta tace tace magajiya ko madam ake ce mata.
Dariya muka kwashe dashi nace kai mama kin iya sawa mutum suna wallahi maryam tace ai magajiyar ce kin sani ko har kauce hanya anayi wanan irin abu nasu haka.
Nice na kawar da zacen da jefo da maganan komawan mu makaranta tace wallahi na dauka kafin mu koma kin haihu nace haba dai yanzu fa nake a takwas.
Tace ni dai rokona kada ki haihu muna exam don wanan karon ba wani dadewa zamuyi ba sosai nace to gani nan dai ni san abin zaizo min ne a rikice wallahi.
Kana naka Allah na nasa ne ban taba daukan haka a gare ni ba wallahi maryam tace ai haka abin yake muna cikin hira mukaji ihun Ihisah kamar ancire mata rai.
Zan daga maryam taja tsuki tana fadin ina kuma zaki don baki da zuciya ta kashe ta mana ba ita ta haifi abinta ba ki kyalesu su kashe ta in sun isa sai can muka tsinkayi muryan namiji yana fada nace yadawo ne gidan.
Mama laraba tace kamar muryan Soja nake ji maryam tace shine ma don munyi waya yace min yana hanya zai shigo kallon ta nayi da mamaki nace maryam yaushe kuka dinke dashi kuma ban sani ba.
Tace kece zaune ai tun yaushe muke tare tun wannan ranan daya rage min hanya fa ai da badon Allah ya gyara ya kawo sojan ku da kila mun samu matsala dake don saura kiris kijini ana min guda.
Kallon ta nayi da mamaki nace wa ke din tace wallahi saboda ke nayi ta daga ma zancen kafa don ban san yadda zasu dauke ki ba idan zancen ya fasu anji.
Wa da zaki aure na tambaya cikin tsure ta da ido tace yayan ki mana Yusuf sai da naji gabana ya fadi nace ina zuwa daki na shiga na kewaya na fito.
Tana kwance saman digon kujeran falon nace maryam wai wani Yusuf dai kike nufi tace kina son kara kewayawan ke nan Yusuf dai da kika sani mana.
Na dafe kirji tare da fadin haba biri yayi kama da mutum ashe shiyasa zainab ke min hannun ka mai sanda tace ai bata san ko wacece ba don ko AA bai bari ya sani ba.
Maryam da kin daure ni wallahi dakin sakani tsaka mai wuya a tsakanin ku da barin gidan nan zanyi tace don may saboda kawai na auri mijin sister inlaw din ki zaki bar gida.
Nace ai idan nayi rantsuwa dubu bazan fita ba sai suce dani aka kulla zancen tace dasun dauki alhakin ki wallahi yanzun haka muna rikici dashi ne ai.
Wai wallahi nayi kadan na fada mai ai ko rikici suraj ya fishi shima kwakwan da yake kenan yasan ko waye aka saka muna rana a kd din.
Nace wallahi baki da kirki maryam harda saka rana ban sani ba tace yes don bamu son ki sani ki bata muna zance ba nace to Allah ya sani ai.
Tace yanzun