MIJIN BUZUWA complete Hausa Novels.txt

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   132 / 144

393K to 396K   out of 431K words

ni har yaran da Alkasim duk mun gaji.
Sunyi murna sosai da ganin mu inda aka shiga dawai niya damu da yaran sai nuna min yan uwa akeyi duk wanda yazo gaida mu.
AA ya shigo gidan ya kalli inda nake fakin baiga motana ba a wurin ga gajiyan daya debo ga yunwa na damun sa part din shi ya shige ya fara watsa ruwa ya fito.
Sai bayan magariba ya shigo part dina sin gaisa yana tambayan Altine ina nake ne tace ai tun fitan da nayi da safe ban dawo ba.
Da mamaki ya maimaita abinda tace yace bata dawo ba fa ina tashiga haka da yaran kuma ai shine Altine ta bashi amsa.
Yayi yace ya juya ya fita daga dakin ya kara jin bacin rai fiye dana safe din wayana ya kara gwadawa bai shiga ya haura part din shi.
Abin duniya ya taru yai mai yawa a rai yasha alwashin sai ya bata min rai ranan idan na dawo don bai yarda da fita irin haka .
Kara shigowa yayi part din tara saura ya tambaya suma hankalin su a tashe yake don laraba tace ban taba fita irin haka ba tunda suka ce mai ban dawo ba.
Gaban shi ne ya bada dam yana fadin ina na shiga a cikin ran shi a fili ko cewa yayi OK idan ta shigo kice ta samay ni a wurina.
Abinci Altine ta taya mai don ranan nice da girki duk da ban nan sun girka abinci sun saka mai nashi.
Yace a hada ya tafi dashi shiru shiru ban shigo ba ya kara trying din layina a kashe wayan yake har lokacin haka yasa ya kira momy yana tambayan ta nazo kaduna ne ?
Momy tace dashi bata gane ni ba sai dai idan ina gidan su ya Amina ne amma bata tsammanin hakan don da ya Amina ta kira ta fada mata nazo.
Ta sake tambayan wani abu ya faru ne babangida da zata wuto baka san inda taje ba tun yaushe ta fita gidan ma ?
Kasa amsa mata tambayan nata yayi don yadda yake ji a ransa yace zan kira momy kada ki fada ma hajiyan mu don Allah ko Abba zan maki bayani daga baya.
Tace to shike nan gashi baida lamban maryam kuma yana son ya kirata ba hali Yusuf ne ya fado mai a rai yasan da wuya idan baida layin maryam din don yaga suna dasawa da ita.
Ya kirashi ya tambaya yace yana dashi inji dai lafiya nan dai yake fada mai abinda ke faruwa yace shine baka nemay ta tun dazu ba man.
Yanzu fa fast ten muke yace shiyasa hankali na ya tashi ai nan dai suka dan taba magana yace bari ya kira maryam din bayan ya turo mai layin ta.
Maryam tayi mamakin jin ban gida tace kuma wallahi ban fada mata komai ba balle ta san inda na tafi din itama dai hankalin ta ya tashi sosai.
Tace idan ansan inda nake don Allah a kirata yana dauka wasa ne sai ga abu ya zama gaskiya don har safe ban gidan ranan hankali tashe ya kwana.
Sai tunane yake ina nashiga don da minna naje da daddy mu ya kirashi ya sheda mai mun sauka lafiya ai.
Tun da safe ya kira daddy bayan sun gaisa sai ya rasa abinda zai fada mai daddy na ya tambayi yan jikokin shi yace daddy su na kira inji ko sun zo gidane ?
Bata gidan ne daddy ya tambaya da sauri yace daga dan magana kadan akan karatun ta tun jiya ta fice gidan da safe bata dawo ba har yanzu.
Hankali daddy ya tashi sosai sai dai ya kwantar ma AA da nasa hankalin yace ka barta duk inda taje nasan gida ne saboda nasan halin khadija.
Ba zata inda zamu ce asha ba da ziwanta zan kirata in gani yace daddy wayan ta a kashe yake tun jiya bai shiga.
Shiyasa na kira ina tsoro idan ba wani mugun abin bane ya samay ta a can don yanzu duniya ya lalace da fitina.
Sun rabar da Daddy zai zaga cikin yan uqa yaji ko ina can daddu ya kashe wayan ya fada tunane bayan sun gama magana da daddy ya ce khadija ba matar da ta taba min haka a gidan sai ke.
Yaushe wanan bakin shawaran yazo maki har kika aikata hakan ki fita min da yara haka ban san inda kika tafi ba.
Hankalin shi idan yai dubu a tashe yake ranan ya har zuwa karfe hudu baiji wani labari ba kuma wayan baya shiga.
Lokaci daya ya zabge dashi don yana cikin tashin hankali kwana mu uku na raba tsaranba da na saya masu tsohon gidan yake tambayana yaushe ne komawan mu sai nayi shi.
Haka yasa ya gane ba lafiya muka zo ba gidan nan cikin hikima yake tambayana ban boye mai komai ba na fada masu abinda ke faruwa .
Sukace in zauna in kyale su zasu kirashi daga baya su fada mai kamar illa ina kuna wayana kiran maryam yana shigo min.
Na dauka naji tana fadin khadija ne kina ina don Allah haka kika tayar da hankalin mutane nace ina garin mu Minna tace nace minna garin mu ne.
Asalin mu dai nazo don nasan in naje minna ba zasu share min hawaye na ba niko kin san ba zan bar karatuna ba don shi.
Khadija ai da sai ki tsaya ku fahinci juna nace kina ganin zai saurare ni yadda ya hau din nan bari ke dai in mashi hakan.
Muna gama waya ta dana ma AA kira suna tare da Yusuf ya dauki wayan tare da sallama tace yanzu mukai magana da khadija.
Cikin sauri yace tana inane haka tace wai garin su ta tafi a jahar kebbi garin yake yace what yaya akayi har taje can din Yusuf yana tambayan shi an ganta dai ko ya kada mashi kai kawai.
Sun gama magana da maryam ya dubi Yusuf yaja tsoki tare da fadin wai kaji wanan yarinyar kebbi fa ta tafi don hauka irin nata da yaran nan.
Yusuf yace tunda dai an san inda suke ai yanzu hankali ya kwanta dai ko da ba a san inda suke bane kaga shine tashin hankalin mu ka tafi Niger ma don mace balle nan da kebbi cikin kasan nan.
May ye marabin kebbin da Niger Yusuf ai kusan nisan su dayane dan bambamcin kadan ne ya fada yana jan tsoki.
Yusuf yace dama su khadija yan kebbi ne ashe yace ta taba fada min hakan amma basu san gida ba garin su wai fulani ne su tace min tun kan muyi aure ta fada min hakan.
Daddy ya kira ya fada mai komai sai da Daddy yakai zaune a inda yake tsaye tsakar gidan mu yace kebbi fa kace yace haka ta fada ma kawar ta .
Suna gama waya da daddy na kiran hajiyan su na shigo mai don momy ta gaji da boye mata kada tayi laifi momy bata bar dakin ba hajiya ta daga waya ta kirata.
Fada ta fara mai tana fadin duk inda yar mutane ta shiga ka nemo masu yar su tunda kai baka san mutunci ba yanzun haka akan wanan bakar matar taka yarinyar nan ta bar gidan ka.
Yace hajiya an gasu wai suna kebbi can ta tafi garin su wurin yan uwan mahaifin ta na can fada sosai hajiya tayi mai ta nuna mashi bacin ranta na yarda ya bari har haka ya faru tsakanin mu.
Bata bari yai mata bayanin komai ba tace gobe goben nan kaje ka dawo da yarinyar nan ko in saba maka hankalin shine ya kara tashi da fadan hajiyan tasu sosai.
Agida ko cewa yayi wasu Altine gida naje in gan su ai badon sun yarda ba suka bar maganan a hanka duk yadda suka so su samu layina a ranan ba wanda ya kamani.
Don muna gama waya da maryam na kara kashe wayan dama itama don ta daukan min excuse ne a school na kirata.
Da ko ita ba zata samay ni ba don naso in barsu sai sun sha wahalan sosai ba wanda yasan inda na tafi har yan gidan mu din.
Tunda mukai waya da maryam din ta fada min yadda ya tayar da hankalin shi kan rashin sanin inda muka shiga nace ai duk tsiyan shi sai ya sake ni don ba zan koma gidan shi ba tunda ba sona yakeyi ba.
Tace keke wanan haukan mukan ai mun tabbatar da son ki a ranshi a fili don yadda ya tayar da hankalin shi ga batan ki.
Nace yaran shi dai yakewa amma ba niba zata damay na kashe wayan na barta tare da danna ma wayan off gaba daya.
Nasan zasu ta nema na don fada ma maryam din duk da nace kada ta fadawa kowa inda nake aikin banza ne sai ta fada yasa na kashe wayan nawa gaba daya.
Washe gari ban san irin sakkon da sukayi ba karfe hudu da wani abu suna cikin kaoje tare da Yusuf da wani dan uwan daddy na suka zo har da daddy.
Muna hira a lungun sarakan kakan namu naji wani saurayi yazo yana fadin ga baki nan daga Abuja sun zo wuri na sai naji gaba ta fadi.
Don ban taba zaton zuwan su ba da wuri hakan nan dayar matar tace karya yake yi yace wallahi suka kalle ni sukace mijin ki ne yazo tafiya ya tashi.
Nace ban zuwa ko ina nazo gida ke nan suka sa min dariya sai da suka huta aka tare su da abin arziki sai da suka huta akaiwa su daddy korafi rashin zuwan su gida.
Sai aka dauko zancen mu kuma nan dai aka kirani nazo a cikin hijjab dina har kasa na zauna gaida su da zuwa.
Daddy na dauka zaiyi fushi dani amma sai naji yace kai khadi idon ki ke nan ke mai iyayye kin kwaso kafa kinzo gidan ku ko.
Dan murmushi nayi na noke kaina nan dai kakan namu ya fara magana yace to Alhaji Abdulsamad ga matar ka nan ta kawo muna korafi duk da kawaici irin namu na fulani korafin ta ya zama dole mu duba mata.
Kasan tana karatu ka aure ta komu nan yan kauye yanzu mun san mahinmacin boko ga diya mace don yaran mu nayi sosai balle ita yar birni.
Don haka muna son ji a nan may ye matsalanka ga karatun nata don mu san makomar ta akai ya gyara zama don tunda na shigo ya daga kai ya kalleni ya sunkuyar da kan shi kasa.
Sai yanzu ya dago yana fadin ba manufa in hanata karatun ta ba tunda dashi na samay ta ni matsalana da ita akan yaran da bata fita dasu ne.
Yara ko nan ai naga basu fita dasu zuwa daukan darasi a gida suke barin su don Allah kayi hakkuri yarinyar nan ta samu ta karasa karatun ta yace ba komai malam in Allah ya yarda an wuce maganan.
Yace shi zancen kishiya da zamantakewan gida ba zan ce maka komai ba mu hilani ba a san mu da raki kan kishiya ba ko kadan balle wata buzuwa can ta tayar mata da hankali.
Don haka ba zamu taba wanan zancen ba amma don Allah duk da haka a kula a tsare hakki abawa kowa hakkin sa a daidaita adalci a tsakani.
Sai zancen yaran da tace ka kwace hannun kishiya ka bata wanan bamu dan dalilin ka nayin hakan ba na bata hakkuri akan haka ta sa maku ido dole kana da manufa akan haka.
Nasiha sosai yai muna sun so su juya ranan don Yusuf ne ya tambaya yace ai ba tare kuka zo ba sai ku bari idan mun shiryata zuwa karshen sati zatazo da yan uwa aga inda kuke da zama don sada zumunci.
Mu wanan yarinyar tai muna komai a rayuwan mu don ta farfado muna da abinda muka kasa yi a tsakanin mu sada zumunci tunda tsofin mu suka kare.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/17/21, 6:30 AM - Xxxxx: Yusuf da sai faman murmushi yake saukewa a fuskan shi tunda tsohon ya fara magana AA dake kula dashi ya fahinci murmushin may Yusuf din ke yi.
Saida suka fito don yin magariba yake sake dan guntun tsoki alokacin Yusuf ya fadada murmushin shi mai sauti yace dama ai na fada maka khadija ta daban ce gashi ko kagani yanzu.
Kai a tunanen ka baka ga macen da zata barka don kanta ba ko wani abu sai idan kai ka saka kan ka binta .
To yanzu ka gani mata suna suka tara don khadija dai ta nuna maka ita ba dukiyan ka ne a gaban ta ba nata take nema da incin kanta.
Zama yayi ya fara tatara hannun rigan dake jikin shi don jin dadin alwalan da zai gabatar a lokacin.
Yace kana tunanen don ta nazo nan din ko may yace ina son sanin wanda kayi uwar tafiyan nan don shi din yace kaima kasan saboda yara na ne don ban san halin da zasu shiga ba idan na barsu nan.
Yaran wa ya haife su ko ka dauki yaran ka tafi dasu man ka barta ai ita gida take gaji irin yabon da ta samu kan zuwan nata ai.
Kyale yusuf din yayi ya fara gabatar da alwalan shi yana tunanen maganan Yusuf din lalai khadija fassarata da wuya ita sam abin da ke gaban saurran bai gabanta kullun ita sai yakin neman wakanta mafita take.
Bayan sun dawo daga massalaci ne a gabatar masu da abinci ida idan sun ci zasu wuce birnin kebbi su kwana washe gari su kama hanya.
Wani yayana ne yazo da kanshi ya kirani wai in je mu gaisa kafin su tafi nace ai ba ni na kirasu ba ya barsu kawai.
Yace ke ko ayi hakan bakin mu ne fa har dake dole daya matsa min na fita zuwa wurin su don mu gaisa.
Na samay tsaye a bakin motar su nayi sallama ciki ciki ba tare da furta komai ba na ja na tsaya Yusuf ne yace maman biyu idon ki ke nan ?
Kin gudo muna da diyan mu ba tare da sanin mu ba nan ma da suka zo ai gidane na bashi amsa a takaice.
Hummm naji AA ya fada kawai tare da fadin gida ne amma ba gidan su ba nace dole dai kamar yadda za a ce gidan uban su nan ma ace gidan uwar su ce ai.
Yanzun dai kada ki saka fulanin garin nan su sauke muna sanda a kai duk inda bi gari ba kaji komai sai kodin kodin ba hausa mai dadi.
A haka aka gansu har aka nace masu Yusuf wanda ke gefe dariyan mumuke yake ma converstion din mu yace wai ni yaran ma ba za a bari mu gansu bane ko fushin mu ya shafe su suma ?
Suna wurin yan uwa na ni kuma ba zan iya cewa a kawo su ba yace gaskiya ne kin nuna muna ke bafullatan asalice wurin kawaici.
Yanzun dai gamu a kasa muna kara bada hakkuri bisa ga laifin da mukayi don Allah a yi hakkuri a dawo a cikin lokacin da aka saka din ko don karatun ki ke ma.
Ai ba damuwa da karatun nawa kukayi ba tunda ku kun kama naku yasa kuke son yi min sakaci da nawa.
Yusuf zaiyi magana ya tare shi da daga mai hannu yana fadin haka naki tunanen yake sai nake ganin kamar sauki na neman maki ashe ke a gurin ki ba haka abin yake ba.
Nace sauki may sauki da zama da jahilci akai ko sauki da gadara da abinda ba na ka ba kai kadai ban yarda da wanan saukin na dan lokaci ba nafi bukatan in sama ma kaina mafita da zufa na nima.
Yusuf muje dare na muna don ance akwai dan nisa tsakanin nan da garin kebbi din mu tafi kada dare yai muna anan.
Yaushe kuma ai dare ya riga yai muku nan don almuru ya wuce ko sai kuma na gobe duk da yasan magana na fada mai bai bani amsa ba sukai min sallama wanda Yusuf ne ya samu yin sallama din suka tafi.
Sunyi nisa ga tafiya yace yarinyar nan ta samu damana da yawa Yusuf ya dan nisa yace dama haka abin yake ai ba kullun ake hawa gado ba.
Ya maida kan shi ga seat din da yake zaune yana lumshe idanu sai tunane take a zuciyar shi lalai maganan Yusuf gaskiya ne.
Mata suna suka tara wai yau shine mace ta bar gidan shi don wani dalili nata can bai taba zaton akwai macen da zata iya tsallake shi da abinda yake dashi ba tace nata zabin ta zaba.
Kudi kyau ilimi wayewa da duk wani abinda mata ke so yana dashi don haka yake daukan ko dun dole mace ta bushi ya juya ta yadda yake so.
Sai gashi ita wanan abin ba haka yake gareta ba duk wanan abin daya lissafa ta ketare

132 / 144

Chapters