ba ko wace mace dama da zata raina shi a matsayin shi na maigida ba garesu.
Kaiko duk wanan abin kayi watsi dasu ka kama akidar turawa da wanda ba naka ba don kawai so da ya rufe ma ido.
Yatsun hannu na ya ja da karfi ina fadin wanan maganan sai da na dan sake kara dan zafin da naji a lokacin.
Yace kika kara fadin haka sai na maki fiye da hakan yace akwai wata wace nake so da har son ta zai rufe min idona bayan ke.
Ko kin mata kece maganin Nafisa a gidan nan kin fada tun kan ki shigo gidan nan kuma na sheda hakan a gare tunda gashi yau kin koreta.
Dan dagowa nayi na kalleshi nace nine ma na koreta ke nan ba kai ba yace akan wa ta bar gidan nan to akan kine ke Deedar dama tace yar matsafa kike kinga kuwa tsafin ki yafi nata ke nan yanzu.
Murmushi nayi don jin abinda ya fada din nace wata sabuwa ke nan yace ai sinan ki yakai har inda baki tsamani ba.
Ni din nace yace yes yana dagawa daga dukawan da yayi a kaina yace yanzu dai jeki shirya don naga kin fara sallah kinga dama kin mata bukulu kin karbi girkin ki tun farko.
Nace ni ban fara sallah ba don ko yanzu wallahi banda tsarki a tare dani yace har da fadin wallahi nace ba karya nakeyi ba ai gaskiya na fada ma.
Mikewa nayi ina fadin ni zan tafi kada yaran su tashi a nemay ni kasa sai dai idan maganan da nayi dazun ya bata ma rai kayi hakkuri don Allah ka gafarce ni.
Haba dai zuciyar ki kika fada min fa kuma gaskiya kika fada idan kin bar abin a dunkule ai ba zan farga haka da saurin in gyara muna kuskuren mu ba.
Baki taba yimin musu ba iyakar ki bakar magana wanda na saba da wanan tun waje baki tsalake umurnina akan wanan maganan ba zan taba ganin laifin ki ba.
Nace Allah ya sauka don Allah a kula da ibada wanda zai zama garkuwa a gare mu da yayan mu nan gaba yace in sha Allah.
Ina kokarin hada kayan wurin yace barin in biki in duba Al,amin da yani nace mun hutar dakai ka bari har da safe idan Allah ya kaimu kaganshi.
Yace rowan dan nawa zaki min nace ban maka rowa ba sai ka dawo a tare muka sauka zuwa kasan don ya duba yaron sai dai mun samu sunyi barci da laraba a daki na ko yasa yai muna saida safe ya koma.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/8/21, 8:34 AM - Xxxxx: Tun dana dawo part dina na kasa barci saboda maganan daya fada min na Nafisa dake mai gizo a ido ke nan Nafisa bata bar bibiyan shi ba ko a can.
Tunanen samun mafita ga wanan alamarin nakeyi a raina har nakai wani lokaci dare ya raba sosai san nan na tsaya ga shawaran dana yanke a raina.
Ya zama dole in tsaya tsayin daka in koma ga mahallicin mu Allah in dukufa dakai kuka na gare shi in dukufa da fada mai damuwan mu gaba daya don samun mafita a gare shi.
Da farko dai na yanke shawaran zan kula da maigidan in mayar da hankali akan aure na sai kuma in kaifafa katfin ibada na dare da rana in yawaita karatin kur,ani da sadaka da taimakon wanda nafi mabukaci.
Da ire iren wanan shawaran ne nakai karshe har barci yazo ya dauke ni ban sani ba a gurin.
Kamar yadda nasa a raina haka na mike gabanin asuba da yake ba sallah nake ba na zauna na dinga tasbihi har zuwa bayan sallah asuba.
Wanka nayi ban kwanta ba, sai dana gama shirina na fito zuwa hada breakfast koda Laraba ta fito ta samu har na kusa hasawa dan wanke wanke da goge wuri ta tayani.
Part din shi na nufa nakai abin karyawa na jera mai kofan dakin shi yana rufe har lokacin don haka na sauko kada in tayar dashi tunda ba aiki zai fita ba ranan.
Na dawo na samu laraba ta gama shirya yaran nan na zauna falo gurin ta muna hira sai gashi ya sauko yana saye da dogon jalabiya baka a jikin shi mai taushi.
Sallaman shi muka karba tare da gaida shi ya karasa inda nake zaune ya karbi yaron a hannu na yana tambayan yaya jikin nasa ?
Nace jiya yayi barci sosai baiyi wani fitina ba yau kuma koda ya tashi babu alaman zazzabin a tare dashi kuma.
Dan wasa yayi mai kafin ya ajeshi ya dauki mami a hannun Laraba yana fadin Laraba wanan yarinyar kamar tana fin babana girma fa.
Tace ai ya dan fada ne saboda dan zazzabin nan dayayi kwana biyu amma ba wani finshi tayi ba gasunan kamar su kadai ake kiwo a gidan nonon uwar tasu yana da kyau sosai sai kace madara ake basu.
Daga inda nake nace mama kamar kin san nakusa fara basu madara tundai tsotson daren nan da suke yana damuna sosai wallahi.
Juyowa yayi inda nake zaune yana fadin idan kin hana su abincin su saidawa zaki yi komay ba wani madara da za a basu tunda suna jin dadin wanda Allah ya wadatar dasu din.
Nace don bakai ake wa wanan tsotson bane yace ki dai daure ki barsu su sha abinsu don Allah ban faye son wanan madaran ba da akeba yara yanzu.
Altine ce daga bayan shi data fito take fadin ina kwana tsohon su yace a, a manyan mata sai yanzu aka tashi ke nan.
Tace na dan koma na kwanta yau matar ka ce ta girka muna abin karyawa da kanta ta fara kyarkyaran mijin ta ke nan .
Nace kai haba Anty daga na taimaka maku kuma kudan huta bagashi shiga kitchen dina yasa kin dan samu runtsawan safe ba yau.
Sadiya basu tashi bane ya tambaya nace da safe dai ta falka an bata abinci ta koma barci Ihisan ko sai zuwa goma don ba school tana hutawa.
Ya juya dauke da yarinyar a hannun shi ya fita daga part din sai dan wani lokaci kiran shi ya shigo min na daga yace breakfast zaki bani nace ok gani nan zuwa.
A zaune suke a dinning din suke zaune yana ma yarinyar wasa na karaso ya tsura min ido har na iso gare su ina fadin yau kuma abincin sai nazo za a ci.
Yace ba haka kika saba min ba da sanyayyar murmushi na sauke a fuska na don jin may yace din yace koba gaskiya na fada ba.
Murmushi na sake yi na bude warmer din na fara zuba mai abincin ido ya kura min yayin da hannun shi ke ma yarinyar wasa nazarin nayake sosai yadda ban nuna abu a cikin wasan dadi sai abin yai mugun damuna.
Daren jiya shima ya dade yana tunanen magana na yayi nazari yagano rashin kyatawan shi sosai don yasan ida Nafisa ce yaiwa hakan da wani ya jisu a gidan tuni.
Sai yaji ba dadi a ranshi irin yadda yake min abubuwa ina hadewa ba tare da nuna damuwa ba sai dai indan yaba baka in bar maganan.
Dagowa nayi da niyar in tambaye shi idan abincin ya isa hakana sai naga ni yake kallo cikin wani irin yanayi na damuwa murmushi muka sauke wa juna nace wani abin nayi kuma ko kake min wanan kallo ?
Yace har yanzu hakkuri nake son kara baki Deedar kiyi hakkuri da abubuwan da suka faru tsakanin mu in Allah ya yarda hakan ba zai kara faruwa ba.
Kallon shi nayi ido cikin ido na nufe inda yake na mika hannu zan karbi yarinyar nace wanan ya wuce ai tun jiya ni ban rikon magana dama kasani tunda mun fahinci juna.
Sai dai wani bukata daya danake dashi akan Anty Fati don Allah idan da hali may zai hana itama ta dawo nan da zama yanzu mu zauna tare tunda can din ba ko yaushe kake samun zuwa ba akai akai.
Kina son kawo wanin zance ke nan a tsakanin mu yanzu kuma nace ba haka bane yaya kawai dai naga kamar shima wani nauyi ne a kan ka.
Sai dai naga kamar dawowan nasu nan zai sai kuma nayi shiru don irin kallon da yake min din yasa na kasa karasa abinda zan fadi din.
Ki bar wanan zancen don baki gama sanin ko waye Fati har yanzu nace koma may ye dai iyalinka ne itama diyan ka ake cutawa don sune har yanzu ba shakuwa a tsakanin ku.
To yanzu may kike son inyi ita fa ta zabi zaman kaduna bani na mayar da ita dole ba can so ki bar wanan zancen don Allah nace Allah ya kyauta.
Ya juya ya fara cin abincin shi hankali kwance ba tare da ya kara magana ba na mike da yarinyar a hannu na na nufi inda yake na kai mai kiss nace hucewan ka lafiya yayan mu.
Murmushi ya sauke yana fadin kin kuru wanan ya fanshe ki gare ni don dana bata maki rai kan wanan maganan nace a dai yi hakuri damu dan Allah.
Na fice ina fadin barin sauka kafin Altine ta fara min sherin data iya don bai mata wuya yanzu gashi ta fara fadi ko.
Yace kina tsoron ta ke nan indai Altine ce sai kin gaji kin fara bata amsa ai a gidan nan na fice ina dariya na barshi zai shige daki shima.
Na samu maryam tazo duba jikin Al,amin a falon gidan na samay su nan muka zauna muna hira dasu sai gashi ya fito cikin wani shadda Gezenah mai kyau ruwan sky color kalan yayi matukar karban jikin shi sosai.
Gaida shi maryam tayi ya amsa tare da fadin yana gyaran hulan shi yace zan fita zamu dan je wani guri da abokina nace na dauka ai gurin budurwa zaka wanan shigar haka ?
Altine ta cabe da cewa da baki fadi ba ai ke dai kice shigar tayi maki kyau sosai ko nace kamar kin sani anty don bai faye saka kayan gargajiya haka ba sai irin wanan lokacin na sallah .
Murmushi yayi ya fice mukai mashi sai ya dawo sai da ya fita maryam tace ai laufin ki ne da baki tsayawa ya shirya a gaban ki idan kin zabo mai yasa mai zai hana ya saka tunda kina sonsu.
Nace kina ganin idan na shiga dakin nakai dan wani lokaci ban fito ba yanzu Nafisa zata kutsa ciki taga may muke yi kedai maryam Allah ya kyauta kawai.
Don ko yanzu ban debe rai da zata dawo gidan nan ba nan dai nake fada mata abinda yace a gamay da ita din tace dama na sani khadija wanan matar ba kyale shi zatayi ba.
Ya zama dole yanzu gare ki kafinta dawo in ma dawowa zatayi gidan nan din kin kafa gwaunatin ki a zuciyar mijin ku ya zama kin mamaye ko ina a gidan nan ta yadda zata rasa gane kan gidan da komai.
Maryam ina kokarta hakan sai dai kin san shi da bahagon hali shima maryam amma zan kokarta in gani don aikine ja a gabana na yin hakan.
Don gaba daya sun sukurkuta mashi lissafin rayuwan shi maryam yana bukatan sai saiti sai dai na fahinci yana da saukin kai a wurin fahinta idan an sashi a hanya.
Sai yamma ya shigo gidan tunda ya fita daidai lokacin naci kwaliya ina zaune a falon gidan ya shigo idon shi a kaina na kada manyan idanuwa na ina mashi sannu da dawowa ya amsa.
Sadiya dake gefe na ya nufa yana mata wasa tare da dan daukan ta ya dan yi mata wasa ya aje ta tare da tambayan ina su mami na ?
Nace suna ciki ana masu wanka yace kinyi kyau sosai da wanan shigar nace na gode tunda ka yaba min dama don kai nayi shi ai.
Yace idan zan samu haka kullun zan yi godiya a kullun duk da dama kina yi amma shigan kananan kaya kamar sun fi karban ki ai.
Sai bayan sallah isha,i na shirya cikin wani arabian gown daga cikin kayan lefena rigar baka ce sai aikin da akai mata a gaba har kasa ya dane jikina dakyau har zaka iya ganin suran jikina dakyau.
Na shiga wurin shi yana zaune yana aiki a dakin shi ya dago yana amsa min sallama na nace barka da yamma ya gajiya ina zaunawa a gefen shi.
Yace ya kuke nace lafiyan mu kalau yaya dan murmushi yayi yace ba zaki daina kirana da yayan nan ba ko sallon ki yaudare ni da wanan kalman yayan naki.
Nace to yaya zance cikin dan marairaicewa yace wanda ya dace dani mana nace baban twince ko yace kamar wani tsoho can nace a dan shagwabe to nikan yaya zance ma don Allah bayan wanan.
Ke kika sani duk maganan da yake kanshi yana a duke bai dago ba sai murmushin da yake a baiyane a fuskan shi jin yadda nai magana ya dago kai yana kallo na.
Sai naji yai murmushi yace oya ki fadi ina sauraren ki nace sai nayi shawara zan fada ma juyowa yayi ya harare ni da sauri na kawar da kaina ina dariyan kasa kasa.
Mikewa nayi da zumar barin shi ya karasa aikin shi sai naji ya jawo ni da hannun shi guda yana fadin yarinya ni zakiwa wayo.
Juyowa yayi da kyau gare ni yabar abinda yakr yace ki tausaya min hakana khadija ina cikin matsuwa don Allah idan kin san kin fara sallah ki fada min please?
Ya kara matso da fuskan shi ya tokare gadon dani a tsakiyan shi har hancin mu yana gogan na juna magana kamar mai rada ya kara fadin in matse dake wallahi.
Nace wallahi yaya bana sallah dadi yakai ma bakina yace waye yayan naki sai kuma yaci gaba da fadin kamar in kara dokan Allah in badon tsoron shi ba da nake ji.
Nace tunda ya fara daukewa mai zaisa ka kara dokan ubangijin nasan nan da kamar sati biyu ko uku zai dauke gaba daya ne.
Ya goga fuskan shi saman nawa yace baki da tausayi wlh kin ma rainani har tsawon sati biyu kice jiya kika haihu ma.
Dariya nayi ya sake matso dani a jikin shi yace Allah bakiga yadda kika koma bane jegon nan yai maki kyau kamar in hadiye ki nake ji.
Nace kai ka taba ganin inda aka hade mutum da ransa yace da wuya in ba a fara kaina ba yanzu nace da ka amayar dani ba shiri idan matan ka suka gane hakan.
Juyawa yayi ya mike zaune ya koma inda yake yaci gaba da aikin shi na mike zaune naji yace yaushe ne zaku samu hutu.
Nace kasan bamu wani dade da komawa ba ai ina ga sai nan da wata da wata biyu mai zuwa yace ok na dauka ai ba zaifi wata daya mai zuwa ba don ina son mu fita da kune waje.
Nace da yaran nan kanana haka gara dai a bari idan sun kara wayau ko yace yara zasu hanamu jin dadi ne a can sai dai idan baki son zuwa ne kawai.
Zanso fita mana tunda ban taba fita wajen kasan nan ba ai nakai wani lokaci a gurin shi muna hira kafin na mike na bar dakin .
Rayuwa jin dadi da so da kauna muke nuna ma juna a gidan yana nuna muna matukar kulawa ni kuma ina kokari wurin kyautata mashi.
Har na yi wanka na fara sallah ranan da na fara zuwa gare shi yayi murna sosai da hakan ranan ya tabbatar da kewan da yake fadi na gaske ne har cikin ranshi.
Sai dai banje da yara dakin ba nan na barsu da gwagon su Altine da laraba suka kwana a wirin su sai ma mami ne ta danyi kuka ana bata ruwa ta koma barci.
Muna kwance bayan mun gama azzakar yake fada min zuwa next week zaiyi tafiya kasan waje zai dan dauki lokaci a can bai dawo ba sai dai kuma idan bai samu yadda yake so ba.
Nace idan alheri ne Allah ya tabbatar da tafiyan yace amin yace ina son kiyi min list din abinda zaku bukata a gidan nan.
Nace gaskiya ban tsanmani akwai abinda bamu dashi ba dai a yanzu amma ya bari zan duba in ga abinda za a kara muna.
Yace kina ban mamaki deedar ke wai baki san kice bari ki karba irin na wasu matan nace may ye riba na a cikin yin haka tunda nasan wata rana za,a tambaye ni kan hakan.
Ban taba tsamanin hakan daga gare ki ba idan mutum ya ganki ganin farko sai ya dauka idon ki a bude yake kan komai.
Dan murmushi nayi nace saboda may za ai min kallon hakan yace da anganki anga wayyan yar boko sai dai idan anzo magana mutum zai sha baka sai ya gane halin ki zai fahinci wanan a jinin ki yake.
Na dauki lokaci a dakin