ta janshi da ba a tace sai munzo Abuja suna idan matar ka ta haihu yace kada kiyi mamakin ma kije can ki zauna har ta haihu din.
Ahmed din yace dako abu yayi kyawo wallahi tunda ba aure takeyi ba yace ai shine taki aure ba sai ki koma zama da mu ba muka wuce suna daga muna hannu .
Ajiyan zuciya na sauke ya juyo yana fadin ya akayi ne nace ummm, umm gani nayi ashe dai kuna da yan uwa ne haka da yawa garin nan yace wanan da kike gani uwar su daya da Abban mu da ita da Iyan bawa ok baki santa bako lokacin haihuwan Ihisan ne ta zauna damu acan Abuja.
Nace ok wanan tsohuwar da suka zauna da mommy yace ita ok inji kin ji don su binta lokacin nace naje mana matarka tai muna hauka kai ya girgiza yace yanzun ma tana can ai na barta tana haukan ne .
Wai ita girki zata karba yau nace ai da kabarta ta karba din tunda ita taga zata iya yace in kaita ina idan ta karba din ko ta cika min daki da fitina.
Nace da ina kake kaita da kuke daki daya kefa baki da kunya nace I'm sorry big brother tuba nake yace hauka ta dai takeyi.
Allah da ka barta tayi ai tunda zata iya din ko ba wani matsala bane shiru yayi min bai bani amsa ba nima shirun nayi mai sai can nace yawwa don Allah ko kasan wani AS Hamza jalingo wai.
Sai da ya waigo ni yace cikin dakewa ina kika san shi ke nace mijin yayan Adam ne mijin anty Amina da ta rasu tabar mai yara biyar.
Yace nasan shi may ya faru shiru na danyi kafin in ce wai alfarma suke so a wurin ka don Allah badon mu ba sai dan yan maratun diyan nan ka saka masu hannu a takardan da yake so ka saka mai hannu.
Yace aikin da suka baki ke nan kuma nace a, a wallahi basu bani wani aiki ba magana daine ta taso har naji amma ni basu sani ma magana ba.
Shi AS jalingo din ne baida abin duban marayu ko shirmay ki din ne yasa kika fadi haka nace kai kullun ai banda wayo ne a giri ka yace abinda nake so dake daga yau kada wani hurda aikina ya kara hada ki da kowa kinji na fada maki.
Don ban daukan wanan shashanci abi ta matana ace ana neman wani abu a gurina haka don yaudara ko may ?
Don Allah kayi hakkuri bansan maganan zai bata maka rai haka ba da banyi mashi ba amma ban karawa da yardan Allah kayi hakkuri ka yafe min idan na bata ma raine.
Ni abinda yasa kaji nama maga hakane kawai zanyi in rama itin halarcin da yaya Adam din yai min a rayuwana wanda dashi nake tunkaho yanzu do badon shi da yai min tsaye a karatuna ba da iyakata secondry school don daddy baida halin kaini gaba.
Amma ya Adam shiyayi tsaye har sai da nayi aure ya daina sa hannu a zancen karatuna shine kawai yasa kaji nayi ma maganan nan.
Huci naji ya furzo dana gama maganan bai sake tanka min ba har aka wagale get din gidan muka shiga muna tsayawa ya bude motar nafita yace dauki ledan na daya ki shiga dashi wurin ki na juya baya na dauka kamar yadda yace nace Allah bamu alheri ban tsaya ba na wuce.
Ina shiga falon yaran nata wasa suka sheko suka rike ni suna mi oyoyo nace miss you guys ina ihisan na tambaya tana gurin uwar ta na karasa dasu a rike a hannu na na gaida Anty Fati da tayi kamar bata ganni ba.
Mama laraba ta fito daga inda take tana sannu da zuwa an dawo nace na dawo mama ya gida tace muna lafiya wajen antyn taki suna gaida ku nace tare da fadin barin dan watsa ruwa mama tace kudai baku da tada ko wani lokaci wanka kuke bamu gujewa wahala da cikin ki da tsohon daren nan zaki wanka.
Idan ban watsa ruwa bane banjin dadi mama nace mata ina dariya na wuce dauke da leda a hannu na har na fara hawa sama nace mama in akwai ruwa a flasks akawo min don ban iya saukowa kuma.
Tace barin in duba lokacin naji yaran na mashi sannu da zuwa na shige abina ban tsaya ba ina shiga na tube na shiga bandaki daidai fitowa na sai ga mama laraba dauke da ruwan zafi a cup tana fadin banga flasks din ba ina ganin mai abune ta dauke abinta nace tofa kuma wata sabuwa ashe ?
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Kallon yarinyar Abba yayi tare da dan jujuya ta ya dago yana fadin Allahu akbar ya mika wa hajiya umma yar yace yanzu da wanan yar haka babangida ya turaki waje a cikin daren nan ?
Bai tausayawa yar shi ba saboda saboda halin da zata iya shiga yana magana yana duban wayan shi bayan ya gama kafa glass din ido shi.
Umma tace ai fushin uwar ne ya shafi yar amma ai ba zaiki yar shi ba tunda ya iya kaita har waje cikin wata mai alfarma da kowa ke son ya natsu yayi ibada a cikin sa.
Murmushi tsohon yayi yana danna kira a wayan shi ya kafa a kunnen shi tare da alaman saurarawa.
Muna zaune falo bayan na gabatar mai da abinci yana shan ferfesun kajin danayi a matsayin abincin dare ihisan da daddy ne a gefen shi suna wasa.
Sai ni da anty Fati da Affan da muke hira daga can wurin kujerun da muke zaune mukaji yace hello Abba.
Duk muka dago muka kalle shi cikin kashe murya anty Fati tace yar iskan kila itace yanzu haka takai karanshi gurin Abba ai dai ta fara ganin sheri ga kaya ta.
Sauren wayan yake yi ba tare da yayi magana ba mukaji yace naji Abba nagode ya kashe wayan ya dan kallo mu yana mikewa yabar gurin tare da nufar hanyar fita waje.
Wallahi ban taba tausayin wanan matar a rayuwa na khadija don ban iya manta abubuwan da tai min a rayuwa na har in koma ga mahalici na kuwa.
Hakuri za a Anty ai ita bata bar kowa ba nidai ban mata sheri ba indan kuma ta nufe ni dashi ya koma saman kanta insha Allahu.
Tace kiri kiri mata ta hanani zama a dakina ta fito fili ta fada min kuma wai kadan na gani daga sherin ta shine yanzu zan tausaya mata ai mata ma yafi haka wallahi.
Allah ya kama su daga shi har ita abinda na gani akan wanan matar nawa sane kiri kiri zasu garin nan tare tace bazan yi girki ba har su gama kwanakin su su koma suna tare.
Ai wurin nan kan shagoce a wurin kwana da miji ko ni can shine yawan matsalan mu don ba shiga harkanta nake ba tun farko don haka ne abubuwa suka zo min da sauki.
Don bamu taba zama haka yadda muke dake din nan ba tunda na shiga gidan nan har rana ita yau kuwa don yar rainin wayo ce tana ganin ita tafi kowa ko shi kan shi gani take tafi shi bata san namiji ki sabo ne ba idan halin shi ya tashi dan abu kadan sai ya kaskanta ka akan shi.
Tace Allah ne fa ya kama su khadija ina fada maki koshi ba kanwar lasa bane wurin wullakanci bata kai karshe ba sai gashi a gaban mu don duk bamu farga da shigowan shi ba lokacin.
May kike fada ya tsure fati da ido ta kasa magana ya kara maimaita maganan shi tare da kallo inda nake nace bafa maganar ka ake ba da Affan take kutawa yayi ya wuce sama.
Nan yafi auki ai don nan zai iya zare idanu can ko ko mussu bai iya yi nace anty wa ya fada maki wallahi yana yi yar iskan matace dai ya hadu da ita.
Sallaman su mommy ne da Anty amarya yasa muka mayar da hankalin mu gurin taron su muna gaida su da shigo tare da masu barka da sallah.
Mommy suka kai kallo a gare mu yaran duk suna a kujeran da nake zaune two seater sai samira dake barci gajiya a dayan kujeran dake gefe na ta rankofo jikin ta wuri na.
Mommy tace don Allah duba saboda Allah may yafi wanan Nafisa kina can kina fada akan wanan yarinyar duba yaran ki a tare da ita.
Anty Amarya tace yaro ai dama fuska yake bi idan bata basu fuska ba ai ba zasu bita haka ba dukkan su.
Yanzu ba Fati da khadija muka samu a tare ba suna hiran su gwanin ban sha,awa amma ke kice da kowa ba za a zauna lafiya ba.
Muryan AA mukaji daga baya yana fadin mommy kun shigo tace eh babangida don Allah kai hakkuri don Alhaji da ya saka baki a cikin maganan nan kada wani abu kuma ya kara samun wanan yar.
Kallon Nafisa da take tsaye tun lokacin nayi mommy tana sance yarinyar a bayan ta tana kokarin mikawa Anty Fati da ta gane haka sai tayi saurin mikewa tare da fadin tana zuwa tayi hanyar kitchen duk muka bita da kallo don kowa ya dago ta.
Ni mommy ta mikowa yarinyar tana fadin karbar ta khadija nasa hannu bayan na jaye ihisan a jikina na karbi yarinyar tana ta barcin ta ba wasu kayan kirki a jikin ta duk da sanyin kaduna da akeyi din.
Zama sukayi tare da fadin Nafisa ki zauna mana ayi magana tana wani harare harare ta zauna tare da yanyala.
Mommy tace Alhaji ne yace idan munzo dama mu tara ku sai gashi Allah yasa mun samay ku a nan din baki dayan ku.
Tau Nafisa duk da Alhaji baiji ta bakin mijin ku ba yanzu dai wanan abin ya ishe ki ishara baka shigowa wuri kace kai kan ka kasani kai kadai.
Ihisan da ta kara hawa jikina anty amarya tace wai ku bakuga uwar taku cikin wani hali bane ku barta ta huta mana hakana.
Shiya karbe da fadin laifin tane ai anty ko yaushe yaran nan suna saman jikin ta hatta idan abinci zata ci sai dasu take ci nayi fada bai sa sun daina ba.
Tace kin zama uwar yara khadija mommy tace in dai khadija ce haka take ai tun gida da yara ita yaro baya isanta ai.
Fada mai kama da nasiha sukai muna a gurin tare da jawa kowa kunne a cikin mu sukai muna sallama suka tafi suna fita yanyala ta mika hannu ta karbi yar daga hannu na suka shige dakin su.
Don shi ya raka su mommy har bakin motar da sukazo dashi an daiji kunya idan an santa angama cika baki gashi tun ba,a je ko ina ba anfara gani.
Anty Fati ce ke wanan maganan bayan wucewar nafisa din ciki ta ce ni ai ba zan taba yarda da kishiya ba har dai irin nafisa mara imani.
A raina nace hardani ke nan dama ban ce sai kin yarda dani ba ai banda ma kowa sheri idan kun min kuma insha Allahu ya koma kan mace.
Bamu dade ba na tayar da Samira na kora ihisan zuwa dakin su nima na shige nawa na barta da yaran ta a gurin.
Washe gari na tashi da son zuwa gidan Ya Amina don can nake son wuni idan na shiga na gaida su hajiya da sallah daga can sai in wuce wurin ta.
Sai dai hakan bai samu ba don bakin dake shigo muna su Anty fauziya ne tare dasu binta suka shigo muna gaida dan uwan su da sallah basu samay shi gida ba.
Har lokacin ba duriyan Nafisa ko wani nata hatta ihisan banga ta fito ba yau abin karyawa ma yanyala ce ta fito ta karbi ruwan shayi ta koma.
A dakina muke zaune tare dasu bayan sun fito wurin Anty Fati nan suka zauna muna hira sosai da su wanda hiran na zancen auren zainab ne.
Sai gashi ya turo kofa suka shiga gaida shi ina dan tsaya a jikin mirrro sai dai duwawo na dake saman mirrow na zauna akai.
Gaidashi da dawowa nayi ya mayar da kallon shi gare ni yana fadin bazaki zauna da kyau ba wanan tsayin da kikayi fa haka ?
Gyara tsayawa nayi da kyau yace dani yau dakin nan nawa yana bukatan gyara don tunda nazo haka yake da kyakyami nake zama a cikin sa.
Nace zaka bar key ne a gyara maka yace eh ina ma gida ban fita sai anjima idan Yusuf ya shigo.
Ya fice Anty Fa,iza tace kai daga Yusuf dai sai yayan mu Allah ya hada amintaka a wurin nan nan suka shiga tuna labarin su na baya suna dariya.
Nace ai gaskiya zainab tayi dacen miji wallahi don idan ta iya zama dashi zata ji dadi wallahi Fa,iza tace ai kema kinyi dace don yayan shima yana da hali mai kyau.
Baki na mere masu nace kai anty kina dai son zance ne kawai wanan gidan gidan danger ko yaushe a cikin fitina ake.
Wallahi anty wani lokaci sai inji kamar in bude ido na in ganni gidan mu don fitinan yayi yawa wallahi tace ai dazun hajiya ke bamu labarin abinda ya faru jiya nace eh tana nan ta dawo zaku shiga ne.
Ina anty faiuziya ta fadi da sauri nace wurin ta anty ina dariya tace ban tashi jin bakar magana ba yau da farin ciki na fito gidana.
Dakin Nafisa kuwa har lokacin tana kwace a dunkule wuri daya sai kiyasta yadda zata dau fansa akan mu baki daya take a zuciyar ta.
Wai yau itace har iyayyen mijin da ta tsana sukai mata alfarman dawowa da ita gidan samad don albarkacin wanan yar data haifa a haka cikin wani yanayi.
Zuciyar ta ke mata soya tun safe gashi ta hana kowa fita sai da yaran suka damay tane ta tura yanyala gurina ta karbo masu abin karyawa.
Taba yaran sun sha amma har yanzu a takure suke a dakin tagane nufin su so suke ta barsu suje gun waccan yar isakan mayaudariyar yarinyar dija yar gidan malamai.
Waya sani ma ko duk ta asirce har da yaran nata ne bako daya irin wanan kulawa da shakuwa dake son shiga masu don ma tana tsaye a guri daya dasu da abinta tasan zaifi haka.
Madam ta kira a waya tana sheda mata duk yadda akayi tace dama ai malam ya fada muna zai karbe ki idan kin je tace kayya da kinga irin wullakantan danayi a gurin su madam sai kin tausaya min.
Wanan yarinyar na yarda ba a banza ta shigo gidan nan ba ga iya kissa kamar tsohuwar karuwa tasan kan sheri har ta gaji.
Yanzu so nake da komai ya daidai in shege kasar mu kafin yar iska ta haihu in yi waje da ita ta haihu can a gidan su ta dandana bacin ran data sani ciki ita ma taji idan da dadi.
Madam tace injin kin tuna da kai mata wanan yarinyar wurin ta shegiya muga karyan jan yara a jiki idan zata yarda ta mamay ta a haka yadda take.
Don nasan shegiya da wayon tsiya ba karbar yar zatayi ba zata samo wani abinda tace tana mata ta guje ma ganin ta kusa da ita.
Ai ko ta guje tura mata zanyi shegiya sai ta haifi irin ta itama ko wace ta fita idan tace sheri ta iya mu zuba dani da ita a gidan nan baki da dama wallahi nafisa madam tace.
Kofan ya turo tayi saurin kashe waya tana kallon shi yace dawa zaku zuba a gidan nan kina da aiki don ko yanzun kika kara gigin min iskanci ba kyale ki zanyi ba don nagaji da halinki nafisa.
Tace nasan ai ba yin kanka bane duk abinda zaka fada yanzu kana da daman fadi duk abinda kaga dama a kaina yanzu.
Yace ki bi sannu wallahi kin san zaman da kike a gidan nan don haka ki natsu kamar yadda kowa ta natsu don ba fin wata kikayi a gidan nan ba duk abu daya ya kawo ku gidana.
Idan akwai abinda ta tsani ji shine yace duk daya suke da sauran matan shi har da wanan da ta shigo kamar jiya a rayuwan shi dama fati abin banza da bata da wani kira na mata da ake so.
Juyawa yayi wurin su samira yacewa ihisan may takewa kuka samira ne ta bashi amsa da fadin wurin anty take son zuwa Ami ta hanata fita.
Common taso kije don may zaki tsare yarinya haka a daki ki hanata walwala tace don ya tace ita din yace yanzu kin daina fadin tayi zuciya ta haifi nata ne ?
Ya rike hannun Ihisan suka fita a cikin yare ta fadawa samira ta dauki baby takai min ita tare da feeder din ta ta mike dama itama fita take son yi ta sukuci yarinyar suka fito daga dakin.
Muna zaune dasu anty Faiza muna hira ya shigo