MIJIN BUZUWA complete Hausa Novels.txt

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   112 / 144

333K to 336K   out of 431K words

batare da nace mai komai ba yace kina ganin wanan rayuwan da kika dauko shine zai fisheki a gurina komay ?
Ni dai ban mashi magana ba ya buga tsuki ya fita a hasale na bishi da harara tare da fadin karfin hali wai barawo da sallama ke nan.
Yanzun kuma wai laifina mutumin nan zai gani yanzu ban masan kan girkin gidan ba yanzu tunda na daina bin komai.
Falo na fito na samu laraba tana ganina tace injin dai ba wani abu tace kinyi ba kuma naga mai gidan ya fita a hasale mama rabu dashi rainin wayo yake son yi min wai ni ban mai sannu da zuwa ba.
Lokacin da zaiyi tafiyan shi ya sallamay ni balle yanzu in tare shi da dawowa tace ai da kin tare sa din ba komai bane Aljannan ki kikaiwa hakan.
Mama har zancen wani Aljanna ake a gidan nan da babu tsari dole in masa haka mama ai idan na gaida shi gobe ma fiya da haka zangani garesa .
Yaba nufin zan zaman bisa ne yana min wullakanci ina bishi shi yana bin umurnin wata saboda ya gyara mata raine yaki sallama na ai yasan dani a gidan.
Watau yanzu hankalin shi ya fara dawowa gare shi idon shi ya bude zai zo ya lalashi banza ko ban cikin matan da zasu dinga bin namiji yana cusguna masu cikin nan ne kawai ya kawo min cikas a gidan nan.
Ki dai yi hakkuri tunda ya sauko yanzu ba gashi har ya biyo ki dakin ki ba inda yana tsoron ta ne ai ba zaizo nan din ba ko yanzu.
Allah ne ya karba muna adduan mu ya kawo saukin lamarin nan kurkusa har ya gane hakan nace bai gane komai ba wallahi mama ki barni dasu kawai a gidan nan.
Dana haihu sai an nemay ni don ba zan zauna ina cin wanan kashin ba da kurciyana su bata min lokaci na a banza.
Sai dai iyayyena da nasa suyi hakkuri tunda basu ke zama min ba nice nasan abinda ake min don haka ni zan wa kaina mafita a gidan nan.
Abincin dare muka gama na dauka bayan nayi sallah na kaiwa Suraj tare na samay su zaune a falon sama din dagani dukkan su rayukan su a bace yake.
Muryan nafisa naji tana fadin akan may zaki kawo mai abinci a gurin ki yake ne ko may kayya ke zaman shi gurin ki ya dama a rayuwan ki ni yaya Suraj na kawowa abinci.
Ke waya kiraki gurin nan ko an fada maki sa,annin ki ne zaune girin nan suraj ya fadi a hasale yana kallon ta.
Tace amma dai kasan a gidan mijina kake ko ina da daman shiga ko ina naga dama a gidan nan ba wanda zai min shamaki.
Ai na dauka gidan ubanki ne nan din ba ita ba harni saida na waro ido waje ya nuna mata kofa yace fice nan tun ranki bai baci ba ko yanzu in tatakaki a gaban mijin naki yana kallo.
Don shi ya daure maki gindin iya shegen da kikeyi gidan nan saboda samun wuri yayi maki yawa har kishiya kike son juyawa ko ?
Kallon AA tayi don yai magana yace Nafisa ki fita kin san halin suraj tunda kikaji ya fadi zai iya aikata maki abinda yace yanzu.
Ta juya yace dawo da sauri ta tsaya yace waye da girki ranan da ya tafi a cikin ku kallona nayi na dukar da kaina kasa ya sake maimaita maganan shi.
Nace itace don nima ban san yayi tafiya ba ya dago yana kallon dan uwan nasa tare da fadin why brother why kabari haka na faruwa a gidan ka.
Kan wanan mara mutuncin zaka watsar da matan ka na kirki ka kama banza can wanan da kake gani cin kasuwa ne ya kawota wurin ku munsan irin case din su da dama.
And kuma gobe goben nan ina son duk taron buzayen nan subar gidan nan tun suna sheda kansu ko in turo a kwashe min su kaf wallahi.
Ke kuma kin zauna wanan banza tana juya ku kamar ta samu waina daga yau ni suraj nace ki mike da tai maki tsiya kikirani ina garin nan yanzu .
Dama nasan zuwa ka nan ba alheri bane an turo kane ka koreni ko ta halin kaka a gidan nan ba inda zan tafi yan uwa na kuma ba zasu tafi ko ina ba tunda ina gidan nan.
Ai bakai nake aure ba dan uwanka nake aure yace zaki gane baki da wayo ranan ma kyale ki nayi don mijin naki baya kusa yanzu ya dawo a gaban shi zan lalatsaki son raina.
Ganin yana magana AA baiko dago kai ya kalle mu ba sai wayar shi yake latsawa a binsa kamar hankalin shi bai gurin draman da akeyi.
Har na bar gurin ina cike da mamakin wai shi AA wani irin mutum ne haka wanda bai iya yin katabus a gidan sa kanin ka yazo yana shimfida doka a gidan ka kana zaune kana sauraro batare da ka furta wani magana ba.
Har na kasa boyewa na fada ma laraba abinda ke faruwa tayi dariya tace bazaki shiga tsakan su ba tun suna yara ance haka suka taso su uku da Yusuf da yanzu ya zama dan gida shima garesu.
Idan ma da ta matsa a kanta zaimai da haushin rashin mutuncin idan tayiwa dan uwan nasa sai kunji mamakin shi.
Allah ne ya karba adduan mu ya jefo aikin shi nan kuma har ya zabi zama daku mutumin da baida sauki ko kadan kowa yasan shi da rashin mutunci ai.
Washe gari ina daki kwance naji kururuwa yana tashi muka fito ciki da sauri ashe nafisa ne shiko yana tsaye murtuk da fuska yasa bakin glass cikin kakin su na sojoji.
Sai umurni yake bayarwa nafisa na Fadin sai dai ta bisu yace tafi nono fari amma yau babu buzun da zai kwana a gidan nan.
Kaf mazan su da matan su aka kwashe a gidan karo na biyu ina fatan daga wanan tafiya kada Allah ya dawo muna dasu gidan kuma.
Ranan laraba taita aiki a falon yasa duk a kwashe kujerun falon aka saka wani su tv da komai na nu,ora aka canza na gidan nafisa tunda ta fita banji duriyan ta ba haka shima mai gidan ashe wuri suka nema masu can wani unguwa da zasu zauna.
Sai dare bayan goma ya shigo lokacin ni har na kwanta mun rufe part din mu yazo yana kwankwasawa don waya a kashe take tunda zan kwanta.
Laraba dake falo ne ta taso ta bude mashi part din ya shigo yana fadin tana ina tace tana daki a nan ya samay ni kwance saidai na falka daga barcin dana fara.
Har kun kwanta yace eh kawai na iya bashi amsa don haushin shi da takaici da nake ji a raina yasa ban ganin dan sauran girman shi da nake gani dama.
Ashe abinda ni ban sani ba shine waya suraj sukayi da hajiya yana tambayan AA zai zo abuja yana son sauka gidan shi shine kafin ya samu wuri.
Hajiya tayi murmushi tace anya zaka iya zama a gidan dan uwanka yanzu yace saboda may hajiya tace gidan ya koma kamar tashan buzaye kowa yaje bai marmarin komawa kuma.
Nan dai ta kora mai duk halin da dan uwan ki ciki yace kada ta damu zai ma abin magani in sha Allahu shine mafarin wanan turjin da yazo yi a gidan ya watsa kowa don bai barta da kowa ba yace idan tana son mai aiki a nema mata yar kasan nan.
Ranan kan sun sha zagi su da dangin su kaf a gurin su da abikan ta inda suka tasa AA a gaba saida ya basu wani gida nashi suka tare a cikin sa wai kafin su gama shiri su koma gida.
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Yanzu gidan AA tankar babu kowa a cikin sa ne don shirun da gidan ya koma wani lokaci muna fitowa falo anan zamu zauna muyi hira da mama sai yaran Nafisa da in ta fita ta barsu a gidan.
Da farko dasu take fita zuwa unguwa daga baya kuma ban ya akayi ba take barin su gidan ta fita haka zasu wuni da yunwa sai idan ni na basu abinci.
Babu wani dogon shiri tsakanina da maigidan tun wanan Clash din ya faru Yusuf ma yanzu ya dauke kafan sa a gidan.
Gida nake son zuwa nakai sati ina binshi da zancen yana ja min rai akan zuwa na gida wai sai na haihu zan tafi na dage akan maganan bai dai ban amsa ba kan tafiya.
Sai yau da ya dawo ya same mu a babban falon gidan muna hira Samira ne ke bamu labari ina rike da yar gurin Nafisa a jikina abinci nake bata.
Ya shigo kamar yadda ya saba idan ya dawo gurin aiki a kasalance muna gaida shi ya samu guri ya zauna Ihisan ya tambaya maman su tace ta fita tunda safe.
Kai ya girgiza yana fadin ina son ranan Friday din nan zan yi tafiya sai ki shirya kuje gida ki dubasu kwana uku ai is ok ya fada yana kallon fuskana.
Kwana uku wanan dadewan da nayi banje gida ba haka one week dai dan dama ke nan yace idan zaki wuce kwana ukun ki fasa ki bari sai idan kin haihu.
Tun ranan na fara shiri na shiga kasuwa da maryam muka sai tsaraban da zamu kai gida tare da mama laraba zan tafi don barin ta gidan ba zai yuyu gare ni ba.
Nafisa bata san da zancen tafiya na ba sai ranan da zamu wuce naje sallaman ta har dakin ta na samay ta nace mu zamu tafi ai muna gafara.
Tace na aikeki ne da zaki sallamay ni dariya nayi nace akwai rai akwai mutuwa don haka ba don ki na zo ba nazo sauke nauyin hakkin makwabtakane gare ki.
Daga haka na fito abina na samu mama a kofa tana jirana a waje muna fita na samu AA a gurin motar .
Motar shigan shi ce ya bamu zamu tafi dashi nan dai ya kara jaddawa driver da yaja mu a sannu kada yai gudu damu.
A raina nace kaji kitihin maza kamar wata wace ya damu da ita a gidan abin mamaki harda hilux na biye damu a bayan mu dauke da kayan tsaraban da ya saya muna .
Ban san da wanan sayayyan ba sai yanzu da motar mu zai tashi yace tsaraban ki na dayan motar.
Ban samu godiya ba muka daga daga wurin ina mamakin shi wa zai ganni da tarin arzikin nan yace wai ba zaman lafiya a gidan shi.
Shike nan ya gama daure ni ta wanan fannin kai maza sun sa takon sheri nace dole in ja bakina in tsuke kan wani matsala nawa ke nan don babu wanda zai yarda da wanan.
Duk da fadan da yai ma driver bai hana shi sharara gudu ba dan kankanin lokaci sai gamu garin minna wani dadi naji a raina daya sakani lumshe idanuwa.
Ina mai jin dadi a raina gidan mu ba bakon wuri bane ga driver nayi mamaki ba tare da kwatance ba ya kaimu har kofan gidan.
Sai dai nayi mamakin ganin sauyin da gaban gidan ya samu sosai an rushe ginan dana sani anyi na zamani a yanzu.
Da mamaki na fito daga ciki motar sai kallon tsarin da akaiwa gidan nake yi gaisuwa nake samu daga wurin samarin dake zama opposite din gidan mu suna zaman kashe wando.
Wa yan nan samarin da suka taso ne suka yi kokarin shiga muna da kayan mu cikin gida sai ga yaran gidan mu a guje sun fito taron mu.
Nan dai muka rungumay juna dasu muna murnan gani junan mu na yaushe rabo ciki muka shiga laraba tana biye damu a baya.
Maman mu tana tsaye ta kasa boye farin cikin ta gare mu sai fara,a take a fuskan ta da dan gudu na karaso na rungumay ta cikin farin ciki.
Ke da hankalin ki kuwa kike wanan gudun da tsohon cikin ki nace mama don Allah bari mana ina cikin yake ina kallon kaina na sake rungumay ta ina jin wani irin abu har cikin raina.
Mun shiga ciki inda samarin ke ta faman jibga kayan a tsakar gidan mu kallon dakin mama nayi nace mama nifa na kasa fahinta wanan sauyin da na gani a gidan nan yanzu.
Tace bari ki huta mana ai zakiji komai dake gudana ko a bakin baban ku idan ya shigo nima haka naga wanan aikin.
Allah sarki dan uwa mai dadi sai ga kanina Nasir da gudu ya sawo min banbara da ta waska wai abin tarban shi ya kawo min.
Nan na baje falon mama na ci bambarana sosai na kora ruwa sama iskan fanka na buguna sai barci ya dauke ni a gurin.
Barci nayi sosai a gurin sai da mama ta tayar dani in sallah na tuna da driver da muka zo dashi nace mama ankaiwa driver ruwa kuwa ?
Tace yanzun kika tuna dashi ankai mai har abinci sun ci suna can da Alhassan ya kai su su samu inda zasu sauka.
Laraba fa na tambaya tace tana can dakin tana sallah na mike nima don zuwa sallah amma cikin nan naki ya girma da yawa anya ba batan wata kikayi ba kuwa baku kidaya da kyau ba.
Ai ina zuwa awo mama su suka fada min cikin yayi girma kamar ba cikin fari ba ne na gani kai mama bar wanan magana kina sa ina jin kunya sosai wallahi.
Tace ikon Allah shi zancen cikin ne abin kunya kamar bamai uba ba ciki ciki da gatan shi zaki wani kama noke noke haka.
Bayan nayi sallah ne daddy mu ya shigo gidan da murna na taso na tare shi shima yaji dadin gani na da yayi yace that is my girl khadija ke ce haka kika zama wata big mama.
O lord daddy har dakai cikin min sheri yace common zo nan in kara ganin ki nayi dariya naje gab dashi na zauna sai kallona yake yana jin dadin ganina.
Mun dauki lokaci dashi muna hira anan yake fada min irin alherin da AA yake masu a raina nace munafuki yar ku nacan yana gana mata tasko yazo nan yana wani kyautata maku.
Yanzu ni zan fara kawo korafin zanan da muke a gidan nan a gaban su dole in ja baki na in shiru ko kuma in kebe da mama da take ita mace ce ta taimaka min da shawara..
Sai washe gari aka fara raba tsara na nesa ni na shirya zuwa gidajen su kai masu don ba lokacin da zan ja dole na shirya ban hutaba na fita.
Gidan ya suwaiba ne karshen zuwa acan muke har karfe takwas muka dawo gida ranan na samu kebewa da mamana itace ta fara kawo min maganan tana fadin.
Naji dadin ganin ki a haka khadija kullun ina kwana da zancen ki a raina dashi kuma nake tashi nasha mafalki da farko mara dadi a kan ki.
Sai da naje gida maikunkele na karasa har beji naga baba nacan ya ban addua da zandinga yi akan ku yace idan kin zo a sanar mashi tun jiya da kuka iso na tayar da Alkassim ya tafi ya sanar mashi da zuwan ku.
Shine yaba da sako a kawo maki kinga sakon nan ta mike tana daukowa tace rubutu ne da hayaki yace kiyi shi tun nan gida dama ina Allah kizo ba sai kin kaiga haihuwa kamar yadda yace ba.
Nace mama nasan kin damu da rashin zuwa na ai sai dai ai kin san ba laifina bane tsoron daddy nake ji kan umurnin daya bani da za a kaini.
Dadin ku haka yake ai ni ban san halin shi ba idan na matsa da magana sai yace ina son kashe maku aure ne komay ?
Mama zuwan nan da nayi akan haihuwa na ne na matsa in zo don irin abinda za a aiwatar idan na haihu din na ce nazo da kudi da zan bar maku ai lalurar haihuwan dashi in Allah ya sauke ni lafiya.
Maganin da ta dauko ta fara min bayanin su tare da fadin yanzu idan kin gama sai in debo maki garwashi ki hayakin yace idan kin kwanta zaki mafalki da wani abu duk abinda ya tsaya maki a rai to kiyi taka tsatsan da abin nan.
Ruwan rubutu ta miko min tace wanan idan kin gama wanka kiyi hayakin sai ki shanye gaba daya ki shafa sauran a jikin ki sai ki dora da hayakin.
Ga ruwa can ki watsa kafin dare yayi sosai ta fadi tana mikewa na tashi na wanka kamar yadda mama tace ina fitowa na samu tana zaune tana jirana da garwashi a gaban ta.
Rubutun ta miko min nasha na shafe jikina da saura na shiga yin hayakin sai da yabi jikina da kyau na cire rufin danayi mun dan taba hira nan cikin daren naba kudin nace ta boye su zan ba daddy nasa da wani don kada ya fahinci wani abu.
Albarka tai ta saka min tare da kara min nasiha kan hakkuri da juriya a gidan miji har barci

112 / 144

Chapters