MIJIN BUZUWA complete Hausa Novels.txt

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   80 / 144

237K to 240K   out of 431K words

A zato yayi barci ne yadda na ganshi a gajiye don haka na dan tako a hankali zuwa gadon can na kwanta na takure a wuri daya.
Can naji shi yana shafa addua a jikin shi tare da sauke ajiyan zuciya ni dai ina wuri daya a takure sai rokon Allah nake a zuciya na kada yace zai taba ni alokacin.
Saukan hannun shi naji a jikina dan zabura nayi a firgice tare da lumshe idona ina jin yadda hannun shi yake yawo a saman jikina.
Sai faman runtse idanuwa na nakeyi kokarin rabani da dan rigar barcin dake jikina yakeyi a hankali na iya furta don Allah ka barni please.
Why naji yace dani kamar mai yin rada nace banjin dadin jikinane kawai shiru yayi na dan wani lokaci sai naji ya matse ni a jikin shi yana sauke numfashi a hankali.
Bai mun komai ba haka muka kwanta da sassafe na tashi bayan nayi sallah kitchen na fada don sama muna abin karyawa.
Nan na barshi zaune yana addua na shige kitchen din don gudun makaran shiga school da nake tsamanin zuwa yau din.
Sai da na gama in son shiga wanka sai gashi ya shigo dakin har yayi wanka a lokacin yayi shirin fita sai lokacin na gaida shi da kwana.
Ya amsa min yana kallon fuskana tare da tambayana yaya jikin naki nace naji sauki cikin wani murya.
Ni zan fita yace yanzun suka kirani daga asibiti wai ana nema na a can dago kai nayi na kalleshi tare da fadin abinci fa nagama hadawa.
Yace banda time din karyawa yanzu sai dana kalleshi nace idan ka tafi wa zai sauke ni school ?
Yace wani school ke da ba dadin jikin ki kike ji ba zaki fita ki zauna ki huta a gida har ki kara walwalewa.
Don girman Allah ka bari in shiga yau kada nayi hadaran point dina jiya banje ba yau kuma kace haka.
Yace eh yana tafiya yana fadin haka naga yafi ga lafiyan ki don ki samu sauki sosai ina kallon shi ya fita naji kamar in saka hannu a kai in kurma ihu a wurin.
Tunane kalakala nayi shi a cikin dan lokaci kan kankani wankan da ban iya shiga nayi ba ke nan ban kuma iya kallon abincin dake gabana ba.
Na dan dauki lokaci a wurin zaune ban iya ko motsawa daga inda nake zaune ba naji wayana daga daki yana ringing kamar in share wayan.
Sai kuma nayi tunanen kila maryam ce ke nema na a layina don haka na tashi zuwa daukan wayan kafin in isa kiran ya katse.
Na duba naga shine a layin kokarin aje wayan nake wani kira ya shigo min nashi na dauka yana fadin kina ina haka waya ke ringing baki dauka ba ?
Ina falo na bashi amsa yace ki shirya min breakfast yanzo zan aiko a daukar min ke kuma ki shirya ya sauke ki a school din idan zaki iya zuwa.
Kamar in ce mai ba zan tafi ba sai naga kaina zanwa sheri nace dashi to kawai ba tare dana furta wani abu ba shima naji ya kashe wayan diban lokaci nayi naga ina da sauran lokaci.
Mikewa nayi na fada bandaki ina tunane a raina ashe haka mata suke fama da ikon maza a kan su mace ita shike nan bata da wani right din kanta sai inda akayi da ita.
A gurguje na shirya tare da shirya mai komai sai ga driver ya iso shiya kirani yana fada min driver na waje yana jirana .
Ban tsaya bata lokaci ba na fito a cikin shirna a waje na samu driver yana jirana fitowa tayi ya karbi kayan hannu na ta sa a motar ya bude min na shiga muka fara hanya.
Tunda ya gaida ni bai kara magana ba sai da na gama tunane nace dashi yana asibiti ne ko office yanzu.
Yace yanzu na sauke shi office ya baro asibiti a raina nace watau akan zuwa asibiti duba matar shine yasa ya fita ba tare da ya jirani ba komay.
Ko kuma wanin sallon ne suka fito dashi a gidan yanzu ya daina saukeni don an hanashi fita dani da wanan tunanen har muka isa school.
Na sauka tare da yima driver godiya na shige ciki na samu har an fara lectures malamin bai hanani shiga ba don ya ganni saye da hijab.
Saboda yana respecting din mata aure sosai yace lalura ke tsayar dasu a wani lokacin haka yasa yake dan rangwanta ma matan aure.
Ban fito ba har sai da mukaje break daidai lokacin sallah azahar wanda a lokacin ne muke dan samun lokacin cin abinci da sauran su.
Yau ma kamar kullun a masallaci muka hade da maryam ina alwala naji tana fadin matar manya yau kin samu fitowa ashe.
Saida na gama na mike nake cewa da ita nikan ai naga iko maryam yanzu na fara ganin matsalan da aure keda shi wallahi.
Bayan mun fito daga sallah muka zauna a inda mukan dan huta idan mun ffito daga sallah kafin mu koma lectures din.
Sai lokacin na fito da abincin da na dan zuba don in karya idan nazo yau kuma abinci zaki ci nace.
Ban karaya ba maryam yau AA yayi bala,in bata min rai sosai wallahi nan dai nake fada mata yadda mukayi dashi.
Dariya naji tana min tare da fadin ai ma ya raga maki cewa fa kikayi bakijin dadin jikin ki.
Kin hana ma bawan Allah hakin shi kice ba zai dauki mataki a kan ki ba ya gane rowa kike mashj ai kyale ki dai yayi wallahi.
Wayana na naji yana verviration na dauko naga sunan shi nace kamar wani wandaa ya damu dani don Allah kirana na may yake yanzu kuma, ?
Ina dauka naji yana fadin yawa kina jina wai su mommy ne suka zo ban san da zuwan su ba yanzun suke sanar dani tasowan su.
Kallon maryam nayi yaci gaba da fadin idan kina free sai ki koma gida yanzu su samay ki a gida idan sun iso.
To kawai na amsa mai dashi na kashe wayan kallon maryam din nayi nake fada mata tace ai dole kije ku gyara gidan ki dan yi masu wani abu ko ?
Tare muka tafi don driver shi ya dawo ya dauke mu zuwa gidan tunda muka isa gidan bamu zauna ba falon gidan ne kawai ban taba ba don ko na gyara buzaye zasu bata shine.

NAFISA
Duk da tana kwance asibiti ba abinda ya rage a cikin halin ta madam na shigowa dakin bayan sun gaisa ne tace madam.
Duk da nasan wanan dan bakan a tamke yake ban cire shi ba a yadda yake tun ranan don gudun su faki idon ya amfa mata yasana barshi a hake.
Yanzun ma jiya da dare nake jin likitocin nan suna magana wai zan kara kwana ki anan na nuna masu bazan iya ba gwamma na koma gida na fake yan iskan nan da idona.
Kai nafisa akwai ki da shirmay wallahi ba zaki batun lafiyan ki ba yanzu ta wani shirmay kike can wai kishiya.
Kishiyar da kika san babu abinda zai taba faru a tsakanin gaban ki ko bayan ki duk dayane a gare su tun da kin dane shegu.
Tayi dariya tare da fadin kai nafisa kin san kan sheri wallahi yanzu kirikiri kin hana komai ya wakana a tsakanin wayan nan mutanen.
Tace ina zan barsu yar iskan koni ta samu haka zata hake ni kin sani tunda ba kishiyar dake son ganin dingo karuwa ga yar uwar zaman ta ai.
Ta kasheni ko in kashe ta shine aure zamanin nan ai don kowace hake take da yar uwarta kowa na sukar dan uwa.
Wallahi indai nice haka zata kare a gidan nan bata gane komai yar iska harta tafi don wanan da ace ta samu ranke ranke ce ni da yanzu taimin yadda naiwa fati.
Da ita da ban za duk daya a gurin miji wallahi madam naki jini a lokacin in bude ido inga wanan bakar fatin gidan samad da yaran ta.
Ina murnan sun tafi ashe zaune bata kare min ba yaje ya kwaso min jikan mayu ya kawo min gida ina hadiyan takaici.
Idan naga yarinyar nan kamar in shake yar iska nake ji a rayuwa na ga shegen feleke wai ita yar boko a dole.
Madam ne tai dariya tare da fadin watau ma waine ko baki tabbatar ba ke nan ke madam tace yanzun kina ganin babu abinda ke faruwa a tsakanin su har yanzu.
Daga inda take zaune tana fuskantar madam din tace ban tsan mani ba duk rawan kan dakikaga yana mata a yanzu wani tsigane na lalashi kada ta tona mashi asiri ace bakai namiji ba.
Dariya suka dauka tare da tafawa kamar ba a asibiti suke suna jinya ba sai faman hanya kulla sheri suke na yarda zasu kasara rayuna da na Fati gidan ya koma nata.
Wanan ai kin gano takon shegeya mai ido a tsaye don idan kika bari har ta fara dandana maki miji ta samu ciki ja dake zatayi sosai a gidan nan don a bude idon ta yake.
Gaban Nafisa ne ya fadi jin abinda madam diin ta fadi a gamay dani na zancen haihuwa da sauri tace madam ranan ko da anyi aika aika ba kadan ba a gidan nan.
Don wallahi na tsani samad ace yana da wasu diya shiyasa ko wa yan nan yaran ban yarda ya saka su a ranshi ba.
Da karfi da yaji sai da naga gaba daya hankalin shi ya fita a gare su bai ko ambanta sunan su ako ina yake yanzu.
Ai mutumiyar baki da wasa wallahi kin huta ganin takaici ba mai maki sallon haihuwan da na namiji har biyu tace shiyasa nake son wanan cikin don in haifi namiji nima.
Badon haka ba ai da tuni na bar da shege na huta da wanan wahalan da nakeyi haka nifa ba haihuwan nake so ba haihuwan namiji kawai nake kwadayi dashi.
Shigowan wasu matar abokan aikin shi ne ya katse masu hiran nasu idan ko nan bata bar halinta ba sai wani jiji dakai tana basarwa take masu.
Basu dade ba sukai masu sallama tare da Allah ya sauwaka suka fice matsn sheri ko wanan bakin Nafisa da madsn basu barsu ba sai gulman su suka dasa kuma a wurin.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Abinci lafiyayye na shirya ma su mommy da ban san su nawa ne tafe ba sa,a na shine ina da komai da muke bukata a gida.
Zakace abincin restaurant ne yadda muka kawa ta komai tuwon faran shimka shine nafiso a rayuwana don haka ban rabuwa da abin sarrafa shi a duk inda nake.
Yauma bayan na tuka tuwon na daure a cikin farar leda ba wasu manyan kwasa nayi ba daidai yadda mutum zai iya cinye kwasar nayi.
Miyar a laihu da manja sai egusi dana daure miyan wanda nama ciki na yankashi da girma yadda zai cika miyar a plate idan anzuba.
Bayan mun gama na shiga wanka nafito na gyara jikina a cikin dogon ringa dinkin kasar Dubai yaji duwatsu har kasa atamfar super ce akaiwa pattern din kwalliya da stone masu kala.
Maryam ma wani dogon riga ta saka a jikin ta muka zauna zaman jiransu ashe sun iso suna asibiti .
Bai samu zuwa ba a lokacin don haka ya tura wani dan ma,aikatan su yayi masu iso inda Nafisa take kwance.
Bai samu sheda mata zuwan su ba don ranan yana busy da baki a office shiyasa ya manta nima zai shiga ne kiran da Abba yai mai cewa sun taso sai yayi tunanen irin taron da zasu samu a gidan idan ban nan shine ya kirani.
Tana zaune saman gado ta baje tana cin kaza gassa da aka kawo mata su madam ma kazar suke yaga daga inda suke sai hira ake kwasa da dararaku irin na shakiyan ci daga bakunan su.
Sallama sukaji a kofan dakin suka waiga don ganin masu shigowa ds sallaman idon tane ya sauka akan anty Amarya dake gaba mommy tana bi mata sai anty Fauziya da Anty Faiza da ya Amina a bayan su.
Take yanayin fuskan ta ya sauya daga dariya zuwa daurewa don batai maraba da zuwan su ba a lokacin don bata ga dalilin zuwan su ba.
Ta dauki zuwan su da munafunci ya kawo su don su zo suga halin da take ciki su koma su baza a dangi ga halin da take ciki.
Don haka ta shiya masu cin mutunci a wurin don sai sun raina kan su da zuwan da sukayi din anty amarya dake gaba dama nafisa ta dade da fahintar son shige mata da take son yi.
Anty amarya cikin kulawa da nuna damuwa a gare ta take fadin Nafisa sannu ashe kuma haka abin ya zo da akasi kuma.
Kazar dake gaban ta ta kawar gefe tana fadin akasi kuma anty wanan ai matsalan ciki ne duk mace mai haihuwa na tare da wanan laurar.
Mommy ne ta yi kamar basu fahinci abinda take nufi ba tace Nafisa ya jikin Allah yasa haka ya zamo alheri ubangiji ya baki lafiya ki koma cikin iyalan ki.
Wanan magana na mommy yai mata tsauri don addua mai kyau mommy tayi mata sai ta amsa da amin mommy faiza da fauziya da kamar zuwan dole sukayi dama sukace sannu Allah ya baki lafiya.
Tace ai lafiya ya samu don gashi kun ganin a cikin sa yanzun ma muna jiran likita ya dawo ne ya bamu sallama mu koma gida.
Fauziya tace ashe ma yadda ake fadi kina jin jikin bai kai yadda yayan mu ya ruda mu ba eh baikai ba tunda ba a jikin ku ciwon yake ba.
Shi kuma da ya damu din ban aike shi shela na a duniya ga halin da nake ciki ba a,a may ya kawo wanan magana kuma haka daga zuwan mu gaida ke inji Fauziya.
Nafisa tace wanan haka yake ai maganar gaskiya na fada daga dan ciwo zai kama tallatani a duniya kamar wani matsala babba.
Allah dai ya baki lafiya inji ya Amina dake kallon ta gaban ta ne ya fadi don kamar da tagani nawa ga ya Amina din sai ta kafe ta da ido.
Mommy ne ta kula da hakan tace ga yar uwar amaryan ki nan makwaciyar mu ne tazo ta gaida ke da taga zamu zo .
Au itama ashe gulma ya kawo ta tazo ta ga ko zan mutu ko ai ban farga ba tun farko har da dangin mayu kuka zo min su karasa ni tana fadi tana jan zani dake jikin ta tana rufe cikin ta da jikin ta.
Haba Nafisa wanan wani magana ne kuma kina nufin gulma ya kawo mu ko may idan ma kin mata ki sani abinda ke cikin ki yana da alaka damu don haka dole muzo muga lafiyan ki.
A, mommy ki dai gyara zancen ki abinda ke cikina da Samad yake da alaka don ko wace ke fili a yanzu ba damuwa kukayi da ita ba a cikin ku.
Kin nuna mata mu yan uwan ubanta ne aka kita don da kin gwada mata mu ai da kinga gatan dakin a gare ta mufa ba don ke muka zo wurin nan ba don mijin ki ne da Abba da yace mu zo mu duba ki.
Kuka dai zo ganin halin da nake ciki amma wace ba a damu da ita da abinda ta haifa a cikin ku ba har aure akai ma Samad aga yadda zan nakasa a gurin shi ko in koma baya don tsabar kiyayyan da ake nuna min.
Anty amarya zatai magana mommy ta tare da fadin bamu san kina kule damu ba ai nafisa da bamu zo ba sai idan kin huce kin fahinci mu ba makiyar ki bane sannan mu zo dubaki.
Don bamu dauke kina rike damu ba a ranki haka sannan ki sani shi aure da samad yayi ra,ayin kanshi ne yayi haka ba ra,ayin mu ba.
Don ba mu zamu zauna mashi da ita ba aure ya nema kuma muja bashi goyon bayan hakan sai dai kiyi hakkuri da kaddara don aure kan anyi shi ba rabuwa sai fatan alheri ta juya tana fadin mu tafin ku Allah ya sauwaka.
Suka juya Faiza ta juyo tana fadin ke kan ki canza halin ki don kina tare da wahala kan ki kika wullakan ta bamu ba don dai Ya AA zai iya rabuwa dake mukuma yana tare da mu har abada.
Nan suka fice suka barta tana jefan su da bakaken magana masu zafi suna fita faiza tace kunga abinda nake fadi tun a gida akaki yarda da magana na yanzu ai gashi kun gani.
Suna mota hanyar zuwa gidan sai masifa suke ya Amina dai shiru tayi mamaki ya cika mata zuciya halin nafisa ya bata tsoro yadda taciwa su mommy mutunci.
Ina gani wani irin zama na keyi a gidan dasu ga yan uwan ta tab a gidan niko ni kadai babu ko abokin

80 / 144

Chapters