Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MIJIN Buzuwa Complete Complete Hausa Novel by Nil

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   95 / 144

282K to 285K   out of 431K words

a gareni bansan may zakiyi da karatun nan ba haka da har kike son wahal min da baby na haka akan wanan karatu.
Dan harara nakai mai nace da abina kuka ganni don haka ku barni in karasa don Allah na hada da kalman roko gare shi saboda kada ya hanani.
Yace shike nan amma sai idan kin kara jin sauki zuwa anjima zan kaiki don ina gida yau zanyi jinya baby na tare da ke yana kokarin cusa hannun shi a sanan cikina .
Nace wai wa ya fada ma cikin gareni don Allah na fada a shagwabe ina kawar da kaina gefe daya dan murmushi ya sauke yayin da hannun nashi ya sauka saman cikin nawa yace.
Yanzu Khadija kin kyauta min ke nan da kika ki sanar dani zancen ciki nan har saida ya girma haka naji gun wasu ?
Yana kokarin juyo fuskan shi gare ni nace to ni may kake son in fada ma akan haka tunda bashi ne na farkon ciki a gidan ka ba.
Amma a wurin ki shine farko ai ko don may ba zaki sanar dani wanan abin alherin da ya samay ni ba muyi farin cikin shi a tare.
Nace nima bansan da cikin ba sai zuwan mu kadunan nan ne hajiyan ka ta fara fada min a gurin ta na fara ji.
Yace serious har hajiya ta sani ni ban sani ba ashe zancen da take min ke nan ban fahince ta ba ranan da take fadin kina bukatan taimako a yanzu shiyasa ta bamu laraba muzo da ita.
Nace ashe kuma alherin da ka aikawa su daddy ke nan ranan sun bugo min suna sanar dani an gode Allah ya karawa arziki albarka yace amin yana ja min hanci na.
Tare da fadin ba sai kin min godiya ba deedar don nima yanzu iyayyenane su yanzun dai ki kwantar da hankalin ki ku rage yawan fitinan nan ki renan min cikina cikin koshin lafiya don Allah.
Nace cikin dan marairaice murya na ai kasan ni ban shiga alamarin kowa a gidan nan sai dai idan an tabani ne ban kyalewa.
Yace yanzu ina rokon ki da ki kyale don ni deedar ina matukar son haihuwa a gidana sosai yasa kikaga ina kafakafa da ciki jikin Nafisa ma.
Banyi magana ba shima shiru ya dan yi a inda yake zaune muryan Nafisa ne a falona tana fadin wanan wani sabon cin amana ne ya dauko komay a gidan.
Mikewa yayi zuwa falon inda ya samay ta tana sababi yace lafiya may ke faruwa ne wai ?
Tace nifa gaskiya ba zan yarda da wanan halin ba ka shigo dakin wanan ka dauki lokaci haka a ciki kansan kuma nice da girki wani rainin hankali kake son ka jawo min a wurinta ko may ?
Har kuna wani shigewa kuna shiru a haka wani lalashin ta zakayi a daki tunda bata da moriya a gurin ka sai ci takai a masai.
Mamaki ya kama shi sosai yace wai nafisa wanan wani irin kishi ne haka harda bata da lafiya din ban da halin in zo in duba halin da ta kwana ke nan ?
A wurin ki ne kila bata da mori a wurina kar kiyi mamaki inkinji irin moriyan da take min tabe baki tayi tace banda abincin da take girka ma kana ci kana santi wani moriya take ma bayan shi.
Zaki gani da idon ki idan lokacin haka yayi yanzun dai ki fice mata a shiya tunda ke baki da tausayin gaida mara lafiya idan yar uwarki bata da lafiya.
Yace ni dana jawo mata rashin lafiya aikin ga nazo in duba abina ko don haka ki fice muje kada ki damay su da surutun ki.
Gaba ta sashi suka fice kamar yaro suna fitane maryam ta shigo dakin ta kawo min tea na tashi na dan sha kadan mikewa nayi ina zufa na shiga wanka don gudun kada mu makara.
Hakana na daure na shirya muka tafi school cikin yanayin rashin jin dadin jikina ko a mota sai korafi yake min nashi fa kada inje wani abu ya samu cikin shi.
Nidai ban iya magana ba sai kaina dana dora saman glass din motar ina sauraren shi da kyat na gama ranan sauki na daya banda wani exam kuma sai wani monday.
Shi da kanshi yazo ya dauke ni muka koma gida ban iya komai kwana biyu naji jiki sosai na samu na murmure namike tun lokacin kuma ban kara jin komai ba tare dani.
Na murmure nayi wani irin fresh dani kyau na ya kara fitowa farina yayi wani fau kamar wata halfcas dani.
Damun kebe dashi zai shiga yaba irin kyau din dana yi a lokacin yana zuzutani irin na maza masu mata biyu zuwa hudu yadda suke wa mace idan suna su kadai.
Sai na lura ko a gabankowa muke dashi zai bini da manyatacen kallon shi yana mamaki irin canzawan da nayi wanda dagani sai maryam muka san sirin abin.
Ga wani ni,imtacen kamshi da nakeyi koda kuwa na bar guri ne zai dade yana bada kamshin jikina hakan na yawan haifar mai da kasala .
Wanan kamshin ko may yake dana ratso zai dago yakalle ni duk abinda yake zai iya dakatar dashi a lokacin .
Gulma haka su yanyala suka kai mata haka yasa ta zauna ta kula da abinda ke wakana a tsakanin mu ta sa ido ta gane ma idon ta fitina.
Ranan sunyi tashin hankali dashi sosai a gidan ranan suyi tujara a cikin dare ni dai ina part dina gashi ana batun fara azumi a washe garin muna ciki muna shirin abinda zamuyi sahur dashi.
Sai da suka gama ne ya shigo dakin namu ina zaune a kasa dogon rigan body hock a jikina rigar ya kama jikina daram ya fitar da suran jikina a waje dan cikina ya baiyana a fili kaina ba dan kwali baida kitso na daure shi a baya.
Daddy yayi barci yayi filo da cinya na sai da ya kalli inda yaron yake kwance yace dani wanan ai sun maki nauyi a jiki ko ?
Nace barshi so nake barcin shi yai nisa yanzun ya gama min fitina kallon yaron dake barci yayi yana makale da goran bobo da yake sha yai barci.
Dukawa yayi ya dauki yaron zuwa saman kujera ya shimfide shi tare da fadin zanga yadda yaran nan zasuyi idan sun koma wurin uwar su duk kin bi kin shagwaba su yanzu da riritawan ki barci ma sai yaro yayi a jikin ki.
Dan murmushi nayi nake fadin haba dai kamar daddy kuma za, a ce wai an bata duka shekarun sa nawa a duniya.
Yanzu dai may kike kuma a zaune haka nace haba yaya kasan fa azumi za a dauka gobe kuma ma kaida ke can kuma sha,anin ku da matarka falo.
Ya harare ni tare da fadin niba shirmay na tambaye ki ba idan kin gama kizo ina jira ki a ciki yana shigewa bed room dina nace na dauka ai an hanaka shiga nan idan ba nice dakai ba.
Aiko bai karasa shiga ba sai ga Nafisa a dakin ni dai ranan naga masifa saidai duk fitinan ta idon ta yana akaina yadda nake zaune da kammanina take kallo.
Da kyat taga safiya tun da safe gidan madam ta yiwa tsinke madam dake barcin safe na masu azumi take kwalawa kira.
Dole ta fito a gigice daga dakin ta zani na sabule mata tana fadin lafiya Nafisa anyi mutuwa ne komay naganki haka.
Madam ai da mutuwa akayi min nasan maishi ya tafi ke nan ko madam ta kara tambayan ta ko aikin mune yaci tace don Allah madam bar wanan shirmay naki yanzu ki saurare ni.
Mu zauna tace mata tana nuna mata kujera tun kan sukai zaune take fadin madam jiya banyi barci ba wallahi ina Allah Allah gari ta waye in zo nan.
Ki tayani duba madam yariyar nan wai bata da aljannu kuwa don ni abinta yana ban tsoro wallahi kinga yadda yarinya take nema ta zuzutani nida gidana kuwa.
Madam ina yi kamar banyi nan dai ta koro mata komai madam tace bari tai wanka taje gidan don ita bata fahinci wanan zuzutawan da nafisa ke nufi ba.
Ina daki sai ga Samiha wai inzo ga madam tazo gaida mu mu gaisa nace yau madam ta saba zuwa da za ace in fito mu gaisa tafice taje ta fada mata.
Zuwan anty hauwa yau kenan na farko gidan mu tazo dubani da jiki ita da anty Salbiya sun kawo min tsaranban tafiyan da sukayi.
Mun dan jima a dakin muka fito na raka su kafin in dawo su na falo a zaune dukan su ina shigowa idanuwan su a kaina ya sauka.
Na wuce ciki rike da hannun daddy dake biye dani kamar bindi shiga madam tayi sauri mayar da hankakinta ga Nafisa tana fadin shike nan kuma yanzu Nafisa kun zama daya da wanan yariyar a gidan nan.
Tace don ta sauya shine zama mu daya da ita ko may tace kina nufin baki ga abinda na gani ba komay kuna gida daya da ita.
Tace nifa har yanzu ban fahince ki ba madam ki fito fili ki magana yadda zan fahince ki tace bakiga abinda idona ya gano ba ke nan .
Ban gani ba tace mata cikin rike habanta tace nafisa ai ciki ke ga amaryan ki tsoho ko don har ya tasa sosai gashi a na gani a filin Allah.
Madam ci may tace wallahi ciki don ko ba gizo idona ke min ba ciki na gani a jikin ta yanzun tunda nafisa ta dafe kirjin ta maranta ya yanka bai daina ciwo ba sai gaba abu ke mata wasa wasa duk suna kanta.
Har aka kai ga kiran mijin ta yazo suka kwasa zuwa asibiti can suka rike ta don sunce cikin bai isa haihuwa ba a lokacin.
Bata san inda take ba don drip di ruwan munje gaida da ita da laraba har lokacin tana barci bamu zauna ba muka dawo gidan don an kusa shan ruwa.
Sai da tai kwana bata san inda take ba ta falka washe gari sai dai har yanzu da damuwa a ranta sosai farkon maganan ta shine AA na shigowa tace dashi baya ya gasheta.
Samad ciki ne ga matan ka komai sai a lokacin ya gane asalin ciwon ta yace cikin wayan cewa ciki kuma wata matar tawa wai kike nufi.?
Ajiyan zuciya yaga ta sauke ta mayar da idanuwan ta ta lumshe bata kara budewa ba saj da ya fita daga dakin Yanyala dake zaune gefen ta ta tambaya a cijin yare ko ta ga ciki a jikina itama.
Yanyala tace ita dai taga na sauya mata ainun ba kamar yadda nake ba a baya ko cikar dakine nayi hakana itama bata sani ba gaskiya.
Fada ta hau yanyalsn dashi wai dama haka suke basu mayar mata da hankali kan abu har sai abu ya lalace hakkuri ta shiga bata a wurin sai da ta gaji tayi shiru.
Samihace ke fada mata wai ai mun zo dubata tana barci fa kuma hausu da fada don may suka bari na shigo inda suke tai masu fada sosai a wurin .
Har da fadin su basu ganin laraba iya inda na tsayar da ita take tsayawa bata gusawa a gurin dana ajeta idon ta na saman aikina.
Kwana biyu tayi asibitin ta matsa zata dawo gida aka sallamay ta ta dawo zuwa madam tayi tace anya babu hannu ga wanan matsalan naki.
Tace na dade da sanin haka madam ina kuma kokarina ga hakan wanan shegiyar badon nafi karfinta ba ai da yanzu ta halakani gidan nan don da karfi ta shigo min gidan nan.
Ko mafalkin ta zanyi ba mai dadi bane gareni shiyasa kike ganina tsaya kyam a kanta kamar layan wuya .
Madam tace kinyi bincike akan cikin ne a jikin ta ko kibane tayi ido ta lumshe tare da fadin na binke shi yace bai san da zancen cikin ba.
Zai fada maki gaskiya ne kike tunane ko may namiji ai makiri ne kila ma dashi aka hada baki a rufe maki kada ki sani ki dauki mataki tun farko.
Yanzu isan ya kosa ai ba wani abinda zamu iys sai dai idan ta haife mu illanta diyar ko dan cikin wani murya tace don Allah madam kibar wanan magana don ma ba cikin bane ni dana daure su daga shi har ita ina wani zancen ciki kuma zai fito gare ta yanzu.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Azumi da kwana goma Nafisa ta haihu lokacin muna gida mun fara hutu hayaniya dana ji cikin ji muryoyin su, kamar waka a falon, yasa ni laikawa waje.
Ashe itace ke labour zasu asibiti suke addua hakana banyi gigin zuwa inda suke ba na dai yi mata adduan Allah ya raba su lafiya.
Diya ce mace aka fitar mata sai dai kuma yar tazo da lalura don haka hankalin kowa ya tashi saukin abin uban yar na da hali tun tashi farko sai da ya zube kudi masu yawa aka fara mata amfani dashi.
Mu dai samu labarin ta haihu don da farko theater aka tashi mata sai Allah ya kawo saukin abin ta haife da kanta a cikin sauki.
Maryam ne tazo min da labarin halin da ake ciki na matukar tausayawa baby da iyayyen ta acikin dan lokacin kankani na shiga damuwa a raina.
Ban ko tsaya mamaki ina maryam ta samu wanan labarin ba sai halin da yarinyar ke ciki nake tausayawa.
Haihuwan safe ta yi don haka ranan tun fitan su da safen ban kara ganin AA ba yana asibitin gurin su sai bayan sallan la,asar ya shigo part din namu.
Lokacin mun rarage girkin da zamuyi don shan ruwa ya shigo falon da sallama a bakin shi na dago kai ina amsa mai sallaman tare da mashi sannu da zuwa.
Sai da ya kai zaune ya amsa min tare da tambayan ya muke nace da Alhamdullahi laraba ta fito kitchen ta gama gyara min zobon da zan hada muna na shan ruwa tace Babangida barka da arziki ashe an sauka lafiya.
Yace barkan mu dai laraba ya gida ya aiki kuma yanzun ma na dawo ne ko zan samu ai min kunun tsamiya in buda baki dashi.
Kallon mamaki nayi mai da abinda naji yace din sai naga duk ya fada min a lokaci daya daganin shi kasan yana cikin tashin hankali.
Laraba ta kalle ni nace akwai sauran garin ai bari tashi in dama mai ki huta don tasan nafi son in girka mai abinda zaici da hannu na ban son wani yai masa.
Nace bari idan na tashi zan dama mai yace ok nace mai barka fa ashe an sauka Allah ya raya muna yasa dadin musulmine yace amin sai dai yarinyar bata da koshin lafiya haka tazo da lalura.
Subbahanallah nace da sauri tare da tausayawa ga maganan nan na jero mata adduan samun lafiya ga Allah yace amin tare da fadin.
Likita yace kila sai an fita da ita waje a acan kila a samu nasaran mata surgerier don matsalan da abin ke da.
Nace Allah yasa a dace yace amin yana dagawa daga inda yake zaune din a kasalance ya nufi hanyar fita part din cikin damuwa.
Ya dade da fita ina a inda ya barni zaune cikin jimamay maganan da ya fada min din laraba data zo ta zauna baya fitan shi tace irin wanan abin ishara ne ga mutum wani lokaci.
Sai dai yanzu uwar daki na karshe akan ki maganan zai dawo don kin san ance mai kishiya bata mutuwar Allah dama.
Nace ni may ye nawa a ciki kuma mama tace kin manta da halin matar gidan nan ne da rashi yarda da Allah bata san kadara ba fa irin su.
Nace hakane fa mama maganan ki dutse wallahi Allah ya gani banje ko ina ba akan ta balle yar da bata ko zo duniya bna
Tace ai zama da irin matan nan sai su bace su batar da na tare dasu don shirka da yai masu yawa yanzun haka wurin shige shigen ta da tsohon ciki taje ta hadu da gamon ta can Allah ya sauwaka nace na mike zuwa kitchen do dama masa kunun da yace.
Sai da na dora na jira ya tafasa na dama na na zuba mai a jug gundun kada ya huce duk da lokaci ya karaso sosai na shan ruwa.
Daga kitchen na fito zuwa part din shi na gyara mai ko ina tunda yau ni kadaice a gidan dole aikin komai nasa ya dawo kaina.
Duk da dama ita ba wai tana gyara mai part din bane iyakan ta ta kwanta ta tashi shike nan nata girki ma ba kullun yake samu ba sai idan tana da bukatan yaci wani abu ne zata sa a girka mai ta barbade shi da abinda zata sa mai shi kuma ya lamshe cikin rashin sanin kai.
Zaune suke shi da Yusuf wanda tunda aka fara azumi a tare suke shan ruwa yanzun ma daga asibiti suka yo nan tare don buda baki.

95 / 144

Chapters